Shuwagabannin Amurka da Afirka ta Kudu sun yi arangama kan zargin kisan kare dangi a Afirka ta Kudu

Fadar White House ta shaida wata zazzafar musayar wuta tsakanin shugaban Amurka Donald Trump da takwaransa na Afirka ta Kudu, Cyril Ramaphosa, wanda ya musanta zargin da ake masa na cewa Pretoria na cin zarafin ‘yan kasar fararen fata.

An yi ganawar ne mako guda bayan da Trump ya yi zargin cewa gwamnatin Afirka ta Kudu na yin kisan kiyashi ga ‘yan kasarta ‘yan asalin Turai.

A yayin tattaunawar da ta samu halartar jami’ai daga bangarorin biyu, shugaban na Amurka ya bukaci ma’aikatansa da su nuna masa faifan bidiyo da ke da alaka da zargin kisan kiyashin, sannan Ramaphosa ya kuma mika wasu takardu da alamu ke da alaka da wadannan zarge-zarge.

Ramaphosa dai ya nuna natsuwa a lokacin da yake mayar da martani kan zargin, yana mai cewa manufofin gwamnatinsa gaba daya sun yi hannun riga da abin da Trump ya fada.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Salon “Kasa Daya Manufa Daya” Ya Dace Da “Ayyuka Goma” Na Hadin Gwiwa Da Afirka

Ofishin watsa labarai na majalisar gudanarwar kasar Sin ya gudanar da taron manema labarai a yau Laraba, inda jami’in ma’aikatar kasuwancin kasar da ke da ruwa da tsaki ya bayyana cewa, aiwatar da matakan da suka dace bisa “Ayyuka guda goma” na hadin gwiwa da Afirka, ya haifar da sakamako mai kyau, wanda ya zuba babban kuzari ga hadin gwiwar Sin da Afirka.

Mataimakin ministan kasuwanci na kasar Sin Tang Wenhong ya bayyana cewa, an riga an tattauna tare da kasashen Afirka sau da dama, an kuma amince da tsarin “Kasa daya, manufa daya” wajen tsarawa da aiwatar da matakai.

Rashin Tsaro: Matasa Sun Yi Zanga-zangar Toshe Babbar Hanya Saboda Satar Mutane A Edo Za A Gudanar Da Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayya Tsakanin Sin Da Kasashen Afirka Karo Na 4 A Birnin Changsha Dake Lardin Hunan

A karkashin burin habaka kasuwanci, da hadin gwiwar tsarin masana’antu, an fara aiwatar da manufar soke harajin kwastam ga dukkan kayayyakin da ake shigowa da su daga kasashe masu karamin karfi, wadanda suka kulla huldar diplomasiyya da Sin, a ranar 1 ga Disamban shekarar 2024.

Karkashin ayyukan cudanya da juna, da samun ci gaba ba tare da gurbata muhalli ba, an kafa ayyukan hadin gwiwar samar da manyan ababen more rayuwa guda 18, wadanda suka shafi fannoni kamar layin dogo, da hanyoyi, da jiragen sama, da wutar lantarki, da kuma sadarwa. (Safiyah Ma)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Salon “Kasa Daya Manufa Daya” Ya Dace Da “Ayyuka Goma” Na Hadin Gwiwa Da Afirka
  • Zargin Satar Fasaha: Kotu ta sanya ranar yanke hukunci kan shari’ar BBC
  • An Tattauna Hanyar Zamanantar Da Kasa A Dandalin Tattaunawa Na Masanan Sin Da Afirka
  • Jagoran Juyin Juya Halin Musulunci Ya Bayyana Cewa Babu Wata Kyakkyawar Fata A Tattaunawar Iran Da Amurka
  • Wulayati Ya Ce Samun Kalamai Masu Karo Da Juna Tsakanin Trump Da Mukarrabansa Yana Zubar Da Kwarin Gwiwa
  • Sakataren Harkokin Wajen Amurka Ya Ce; Gwamnatin Siriya Zata Iya Rugujewa Cikin ‘Yan Makonni
  • Wasu Shugabannin Turai Sun Yi Barazanar Ladabtar Da Gwamnatin Haramtacciyar Kasar Isra’ila
  • Gwamnatin Kasar Masar Tana Shirye-Shiryen Sanya Kafar Wando Daya Da Gwamnatin ‘Yan Sahayoniyya
  • Kasar Sin Na Adawa Da Kai Wa Fararen Hula Da Kayayyakin More Rayuwa Hari A Sudan