Jami’an tsaron Zulum sun buɗe wa Boko Haram wuta a Maiduguri
Published: 22nd, May 2025 GMT
Jami’an tsaro da ke raka ayarin motocin Gwamnan Borno, Farfesa Babagana Umara Zulum sun buɗe wuta kan ’yan Boko Haram a hanyarsu daga Gamboru Ngala zuwa Maiduguri bayan wani rangadi na kwanaki uku.
Kodayake ba a san dalilin ’yan ta’addan ba, amma jami’an tsaron ayarin motocin sun bi su inda suka yi ta musayar wuta na kusan rabin sa’a tsakanin ƙarfe 12:50 na rana zuwa ƙarfe 1:30 na rana.
Gwamnan ya zagaya ta wasu ƙananan hukumomin ne sakamakon hare-haren da ‘yan ta’addan suka kai musu, babu tabbas ko gwamnan na cikin ayarin motocin.
Wata majiya da ke cikin tawagar ta tabbatar wa da wakilinmu faruwar lamarin a wata tattaunawa ta wayar tarho.
Gwamnan ya je garin Wulgo ne tare da tawagarsa domin duba halin da tsaro ke ciki.
“A kan hanyarmu ta zuwa Maiduguri, bayan mun tashi daga Wulgo, lamarin ya faru,” in ji wata majiya.
Sautin harbe-harbe da aka yi ba zato ba tsammani ya haifar da firgici a cikin ayarin motocin, inda wasu ke ganin cewa harin kwanton ɓauna ne wadda ya sa ayarin motocin sun yi karo da ’yan ta’addar.
Wata majiya ta ce, ‘yan ta’addar sun harba makamin roka wanda bai fashe ba a lokacin da gwamnan ke jawabi.
‘Ɗaya daga cikin jami’an tsaro ya hango wani makamin roka da ’yan ta’addan suka harba a lokacin da gwamnan ke magana ga jama’a wanda ya sanar da tawagar da su bar wurin, akan hanyarsu ta fita ‘yan ta’addan sun yi artabu da jami’an tsaro,” in ji majiyar.
Jami’an tsaron da ke cikin ayarin motocin sun buɗe musu wuta tare da tarwatsa su bayan sun yi musayar wuta.
Wata majiya kuma ta ce ‘Alhamdu lillah, yanzu mun dawo Maiduguri.’
A cikin wannan batakashi majiyar da ke ayarin na cewa wasu daga cikin rundunar haɗin gwiwa ta farar hula da wasu mafarauta waɗanda har yanzu ba a tantance adadinsu ba sun samu raunuka.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Babagana Umara Zulum ayarin motocin yan ta addan
এছাড়াও পড়ুন:
Shugaban Amurka Yace Yana Jiran Amsar Hamas Cikin Sa’o’i 24 Masu Zuwa Don Tsagaita Wuta Na Kwanaki 60
Shugaban kasar Amurka Donal Trump Ya Bayyana cewa nan da kwana guda ko sa’o’ii 24 masu zuwa ne zai sani, ko kungiyar Hamas ta amince da ‘shawararsa ta tsagaita wuta da HKI kuma ta karshe a gaza.
Shafin yanar gizo ta labarai ‘Arabnews ta kasar Saudia’ ta nakalto Trump yana fadar haka a yau jumma’a.
A wani bangare shugaban ya ce yayi magana da gwamnatin kasar Saudia dangane da fadada yarjeniyar Ibrahimia wacce ya samar da ita a shugabancinsa na baya wacce take bukatar kasashen larabawa su samar da huldar jakadanci da HKI, wanda kuma ya sami nasarar a kan wasu kasashen larabawa na yankin tekun Farisa.
Daga shekara ta 2023 ya zuwa yanzu yahudawan sun kashe falasdinawa kimani 56,000 sannan fiye da dubu 12000 suka ji rauni.
Majiyar Falasdinawan ya zuwa yansu, ta bayyana cewa fatansu shi ne tsagait wutar ta kaika ta zamam din-din din.