Jami’an tsaron Zulum sun buɗe wa Boko Haram wuta a Maiduguri
Published: 22nd, May 2025 GMT
Jami’an tsaro da ke raka ayarin motocin Gwamnan Borno, Farfesa Babagana Umara Zulum sun buɗe wuta kan ’yan Boko Haram a hanyarsu daga Gamboru Ngala zuwa Maiduguri bayan wani rangadi na kwanaki uku.
Kodayake ba a san dalilin ’yan ta’addan ba, amma jami’an tsaron ayarin motocin sun bi su inda suka yi ta musayar wuta na kusan rabin sa’a tsakanin ƙarfe 12:50 na rana zuwa ƙarfe 1:30 na rana.
Gwamnan ya zagaya ta wasu ƙananan hukumomin ne sakamakon hare-haren da ‘yan ta’addan suka kai musu, babu tabbas ko gwamnan na cikin ayarin motocin.
Wata majiya da ke cikin tawagar ta tabbatar wa da wakilinmu faruwar lamarin a wata tattaunawa ta wayar tarho.
Gwamnan ya je garin Wulgo ne tare da tawagarsa domin duba halin da tsaro ke ciki.
“A kan hanyarmu ta zuwa Maiduguri, bayan mun tashi daga Wulgo, lamarin ya faru,” in ji wata majiya.
Sautin harbe-harbe da aka yi ba zato ba tsammani ya haifar da firgici a cikin ayarin motocin, inda wasu ke ganin cewa harin kwanton ɓauna ne wadda ya sa ayarin motocin sun yi karo da ’yan ta’addar.
Wata majiya ta ce, ‘yan ta’addar sun harba makamin roka wanda bai fashe ba a lokacin da gwamnan ke jawabi.
‘Ɗaya daga cikin jami’an tsaro ya hango wani makamin roka da ’yan ta’addan suka harba a lokacin da gwamnan ke magana ga jama’a wanda ya sanar da tawagar da su bar wurin, akan hanyarsu ta fita ‘yan ta’addan sun yi artabu da jami’an tsaro,” in ji majiyar.
Jami’an tsaron da ke cikin ayarin motocin sun buɗe musu wuta tare da tarwatsa su bayan sun yi musayar wuta.
Wata majiya kuma ta ce ‘Alhamdu lillah, yanzu mun dawo Maiduguri.’
A cikin wannan batakashi majiyar da ke ayarin na cewa wasu daga cikin rundunar haɗin gwiwa ta farar hula da wasu mafarauta waɗanda har yanzu ba a tantance adadinsu ba sun samu raunuka.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Babagana Umara Zulum ayarin motocin yan ta addan
এছাড়াও পড়ুন:
An Karrama Farfesa Adamu Gwarzo Kan Gudummawarsa Ga Bunƙasa Ilimin Jami’a A Nijeriya
Ya ƙara da cewa ‘yan’uwa da abokan arziƙi da suka shirya wannan biki na karrama Farfesa Armaya’u Bichi tare da bashi lambar yabo tare da wasu muhimman mutane waɗanda suka taimaimake shi wajen gudanar da shugabanci sun kyauta sannan sun ajiye ƙwarya a gurbinta.
Shima da yake gabatar da jawabinsa, shugaban riƙo na jami’ar gwamnatin Tarayya dake Katsina (FUDMA), Farfesa Aminu Ado ya ce Bichi mutum ne mai jin tausayin al’umma musamman mutanen dake ƙarƙashinsa.
Farfesa Ado ya ce har ƙasa ta naɗe ba zai mance da irin gagarumin ci gaban da Farfesa Arma’yau ya kawo ma jami’ar FUDMA ba.
Haka kuma a yayin bikin an ƙaddamar da littafin waƙoƙin da wasu mawaƙa suka yi wa tsohon shugaban na FUDMA mai suna ‘MALAMI A BAKIN MAWAƘA,’ wanda wasu ma’aikatan jami’ar suka rubuta.
Babban mai ƙaddamar da littafin, kuma shugaban ƙungiyar Jami’oin Afrika masu zaman kansu, Farfesa Adamu Abubakar Gwarzo wanda ya samu wakilcin Dakta Ali Yusuf Kakaki ya sa ya sayi kwafi biyu a kan naira miliyan biyu (N2, 000, 000), sai kuma Sanata Alu Magatakardan Wamako ya sayi kwafi uku kan naira miliyan ɗaya.
Frafesa Armaya’u Bichi, ya nuna godiyarsa ga waɗanda suka shirya wannan taron domin taya shi murnar kammala aiki lafiya. Tare da jinjina da fatan alheri ga kafatanin waɗanda suka samu damar halartar wannan taro.
A yayin taron An karrama Farfesa Adamu Abubakar Gwarzo da shi kansa Farfesa Armaya’u Bichi da Farfesa Abubakar Rasheed da Malam Rufa’i Bichi da Malam Adamu Adamu, tsohon ministan ilimi a zamanin mulkin Buhari.
ranar Asabar 13 ga watan Satumban 2025 makusantan tsohon shugaban jami’ar Gwamnatin Tarayya dake Dutsinma ta jihar Katsina, Farfesa Armaya’u Hamisu Bichi sun gudanar da gagarumin taron murna da farin cikin kammala aiki lafiya tare da karrama shugaban rukunin jami’oin Maryam Abacha American University, Farfesa Adamu Abubakar Gwarzo da lamar yabo.
Gagarumin bikin wanda aka gudanar da shi a babban ɗakin taro na kwalejin ilimi na Tarayya (FCE) Bichi ya samu halartar ɗimbin masoya daga ko’ina a faɗin Nijeriya.
Farfesa Abubakar Adamu Rasheed tsohon shugaban Hukumar dake kula da jami’oin ƙasa (NUC), a yayin da yake jawabi ya bayyana Farfesa Armaya’u a matsayin mutumin kirki mai tausayi da ƙaunar jama’a.
Ya ƙara da cewa ‘yan’uwa da abokan arziƙi da suka shirya wannan biki na karrama Farfesa Armaya’u Bichi tare da bashi lambar yabo tare da wasu muhimman mutane waɗanda suka taimaimake shi wajen gudanar da shugabanci sun kyauta sannan sun ajiye ƙwarya a gurbinta.
Shima da yake gabatar da jawabinsa, shugaban riƙo na jami’ar gwamnatin Tarayya dake Katsina (FUDMA), Farfesa Aminu Ado ya ce Bichi mutum ne mai jin tausayin al’umma musamman mutanen dake ƙarƙashinsa.
Farfesa Ado ya ce har ƙasa ta naɗe ba zai mance da irin gagarumin ci gaban da Farfesa Arma’yau ya kawo ma jami’ar FUDMA ba.
Haka kuma a yayin bikin an ƙaddamar da littafin waƙoƙin da wasu mawaƙa suka yi wa tsohon shugaban na FUDMA mai suna ‘MALAMI A BAKIN MAWAƘA,’ wanda wasu ma’aikatan jami’ar suka rubuta.
Babban mai ƙaddamar da littafin, kuma shugaban ƙungiyar Jami’oin Afrika masu zaman kansu, Farfesa Adamu Abubakar Gwarzo wanda ya samu wakilcin Dakta Ali Yusuf Kakaki ya sa ya sayi kwafi biyu a kan naira miliyan biyu (N2, 000, 000), sai kuma Sanata Alu Magatakardan Wamako ya sayi kwafi uku kan naira miliyan ɗaya.
Frafesa Armaya’u Bichi, ya nuna godiyarsa ga waɗanda suka shirya wannan taron domin taya shi murnar kammala aiki lafiya. Tare da jinjina da fatan alheri ga kafatanin waɗanda suka samu damar halartar wannan taro.
A yayin taron An karrama Farfesa Adamu Abubakar Gwarzo da shi kansa Farfesa Armaya’u Bichi da Farfesa Abubakar Rasheed da Malam Rufa’i Bichi da Malam Adamu Adamu, tsohon ministan ilimi a zamanin mulkin Buhari.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp