More Podcasts Najeriya a Yau Daga Laraba

Me sa jiga-jigan ’yan siyasar Najeriya ɓangaren adawa suka zaɓi inuwar Jam’iyyar ADC domin haɗa hannu da nufin kawar da Shugaban Kasa Bola Tinubu da jam’iyyarsa ta APC daga mulki?

Da daren Talata ne dai manyan ’yan adawar, waɗanda suka haɗa da tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa Atiku Abubakar, da tsohon Gwamnan Jihar Kaduna Malam Nasir Ahmed El-Rufai da kuma ɗan takarar Shugaban Kasa na Jam’iyyar LP a 2023, Peter Obi, suka yanke shawarar tsugunawa a ƙarƙashin inuwar ADC din.

Shin ko wannan jam’iyya tana da inuwa mai ni’imar da za ta iya riƙe wannan haɗaka?

Shin waɗannan ’yan siyasa za su iya ci gaba da shan hannu da juna har su kawar da gwamnati mai ci?

NAJERIYA A YAU: Yadda Za Ku Kula Da Lafiyar Jikinku DAGA LARABA: “Abba Al-Mustafa Ba Shi Da Hurumin Dakatar Da Fina-finanmu”

Shirin Najeriya a Yau na wannan lokaci zai yi nazari ne kan ƙarfin da wannan ƙawance yake da shi na ƙalubalantar gwamnati mai ci.

Domin sauke shirin, latsa nan

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Atiku Abubakar

এছাড়াও পড়ুন:

Shugaban Kasar Iran Ya Ce Kungiyar ECO Ta Yi Tir Da Hare-Haren HKI Kan Kasarsa

Shugaban kasar Iran Masoud Pezeshkiya ya bayyana cewa dukkan kasashe mambobia a kungiyar ECO ta raya tattalin arziki na kasashen yankin sun yi tir da HKI a taron kungiyar wanda aka gudanar a birnin Khankendi. Na kasar Azerbaijan. Kamfanin dillancin labaran Tasnim na kasar Iran ya nakalto shugaban yana fadar haka bayan tawowarsa daga taron a daren jumma’a a kuma shafinsa na X. Shugaban ya kuma kara da cewa Tehran a shirye take ta hada kai da wadannan kasashe makobta don taimakawwa juna a dukkan bangarorin rayuwa wadanda suka hada da kyautata tattalin arzikin yankin da al-adu da sauransu.

Shugaban ya bayyana cewa yana godiya ga dukkan kasashen kungiyar ECO da kuma sauran kasashen yankin da sauran kasashen duniya wadanda suka nuna goyon bayansu ga kasarsa bayan yakin kwanaki 12 da HKI da kuma Amurka.

Daga karshe yace  yana fatan kasar da sauran kasashen kungiyar ECO zasu kai ga gurunsu na bunkasar tattalin arziki ta shekara ta 2035.

A ranar jumma’a 13 ga watan Yuni ne jiragen yakin HKI suka kai hare-hare a kan Iran inda suka kashe manya-manyan jami’an sojojin kasar da masana fasahar Nukliya da kuma fararen hula wadanda basu san hawa ko sauka ba. Sannan Amurka ta kai hare-hare kan cibiyoyin makamashin nukliya na kasar da suke fordo Natanz da kuma Esfahan.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Dalilin da matan karkara a Kano suka fi son haihuwa a gida
  • Xi Ya Ajiye Furanni Ga Wadanda Suka Mutu Yayin Yakin Bijirewa Harin Japan
  • Miliyoyin Yan Najeriya Ne Suka Gudanar da Tattakin Ashoora Wasu Kuma A Makarantunsu…
  • NAJERIYA A YAU: Mene ne tasirin naɗin Mataimaka na Musamman a rayuwar jama’a?
  • Bincike ya nuna ’yan Najeriya ba su gamsu da gwamnatin Tinubu ba
  • Tinubu ya umarci sojoji su murƙushe ’yan ta’adda a faɗin Najeriya 
  • An kama ɗan Najeriya yana taimaka wa Rasha a yaƙinta da Ukraine
  • Shugaban Kasar Iran Ya Ce Kungiyar ECO Ta Yi Tir Da Hare-Haren HKI Kan Kasarsa
  • Dalilin Kwararru Na Bukatar Kafa Cibiyoyin Bincike Kan Nau’ikan Dabbobi A Nijeriya
  • Ana Tuhumar Tsohon Ɗan Wasan Arsenal Thomas Partey Da Laifin Fyaɗe A Ƙasar Ingila