HausaTv:
2025-04-30@19:50:53 GMT

Saudiya Tace Shigo Da Agaji Cikin Gaza Bai Da Dangantaka Da Tsagaita Wuta

Published: 12th, April 2025 GMT

Ministan harkokin wajen kasar Saudiya ya bayyana cewa shigo da kayakin agaji zuwa cikin zirin Gaza bai da wata dangantka da tsagaita bude wuta.

Shafin yanar Gizo na labarai Arab News na kasar Saudiya ya nakalto Yerima Faisal bin Farhan yana fadar haka a jiya Jumma’a.. Ya kuma kara da cewa dole ne kasashen duniya su takurawa HKI ta bada dama a shigo da kayakin agaji zuwa cikin zirin gaza saboda ceton mutanen yankin daga yunwa mai tsanani da suke fama da shi.

Ministan yana magana ne bayan taron ministocin harkokin waje na kasashen larabawa da Musulmi a Antalya, inda suka tattauna batun yadda al-amura suke a zikin gaza da ya hanyoyin da za’a bi don tsagaita wuta da kuma shigo da kayakin agazaji cikin yankin da gaggawa.

Yerema faisal ya kamma da cewa kasashen larabawa da musulmi basa son duk wani shiri nakorar Falasdinawa daga Gaza, kuma suna goyon bayan shawarorin da kasashen Qatar da Masar suka gabatar dangane da tsagaita wuta a gazar.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

An Fara Baje Kolin Kayakin Da Ake Kerawa A Iran Tare Da Taron Iran Da Afirka Karo Na Uku

An fara kasuwar baje koli na kayakin kasuwancin da ake samarwa a cikin Iran ko IRAN EXPO 2025, karo na 3 a nan Tehran.

Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya bayyana cewa kasuwar baje koli na Iran EXPO 2025 zai jawa masu zuna jari daga kasashen Afirka.

Ministan harkokin wajen kasar Iran Abbas Aragchi ya fadawa kamfanin dillancin labaran IP kan cewa Kasuwar ta bana dai, za ta tara kamfanonin  masu samar da kayaki daga yankuna daban daban na kasar Iran da dama, kuma akwai fatan cewa wannan kasuwar ta zama mabudi ga kyautatuwan tattalin arzikin kasar.

EXPO dai ita ce kasuwar baje koli na kayakin kasar Iran mafi girma wanda ake gudanarwa a ko wace shekara, sannan daga nan take samun kasuwa a kasashen duniya. Kuma yan kasuwa daga kasahe fiya da 100 ne  suka shigo kasar don halattan kasuwar.

 Esma’il Bakaee, kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Iran ya ce ya na fatan a wannan  kasuwar, kasashen Afirka da Iran za su amfani juna a harkokin kasuwancin da ake bunkasa a tsakaninsu.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Araghchi : Za’ayi Tattaunawar Iran da Amurka ta gaba a Rome bayan taron E3
  • Yadda ’yan Tifa da baƙin direbobi ke haddasa haɗari a Abuja
  • Saudiya Ta Yi Allawadai Da Kissan Kiyashin Da HKI Take Yi A Gaza A Gaban Kutun ICJ
  •  Falasdinawa 40 Sun Yi Shahada A Cikin Sa’oi 24 A Gaza
  • An Fara Baje Kolin Kayakin Da Ake Kerawa A Iran Tare Da Taron Iran Da Afirka Karo Na Uku
  • Har Yanzun Ana Zaman Dar-Dar A Burkina Faso Bayan Kokarin Juyin Mulkin Da Bai SamiNasara Ba
  • Shugaban Putin Na Rasha Ya Bada Sanarwan Tsagaita Wuta Da Ukraine Na Sa’o’ii 72
  • Majalisar Dinkin Duniya Ta Jaddada Wajabcin Komawa Kan Shirin Tsagaita Bude Wuta A Gaza
  • Rasha ta ayyana tsagaita wuta ita kaɗai a yakinta da Ukraine
  • Takht Ravanji: Iran Ba Za Ta Taba Yin Tattaunawa Akan Dakatar Da Tace Sanadarin Uranium Ba