Leadership News Hausa:
2025-05-01@01:10:38 GMT

Hanyoyi Biyar Na Kare Kajin Gidan Gona Daga Tsananin Zafi

Published: 12th, April 2025 GMT

Hanyoyi Biyar Na Kare Kajin Gidan Gona Daga Tsananin Zafi

Hanyoyi Biyar Da Mai Kiwon Kajin Gidan Gona Zai Kare Kajinsa Daga Tsananin Zafin Rana.

1- A Tabbatar An Sama Musu Wadacciyar Iska A Dakin Kwanansu:

Ana bukatar mai kiwon kajin ya tabbatar ya sama musu wadatacciyar iska a dakin kwanansu, ana kuma bukatar a yi wa shigifar dakinsu fenti yadda za ta rika rage zafin ranar da kuma samar da kayan koyon da za su sanyaya dakin kwanansu.

Haka kuma, ana bukatar a rika sanya musu na’urar da ke sanyaya daki, wadanda za su rika rage zafin ranar, akalla na’urar ta kasance mai ma’unin yanayi daga 5 zuwa 10°C.

2- Sanya Na’urar Sanya Daki:

Domin samun saukin yanayin zafin rana, ana bukatar mai kiwo ya sanya musu na’ura a dakin kwanansu, domin rika sanyaya dakin, yadda jikinsu zai rika yin sanyi.

Ana kuma bukatar masu kiwon, su rika sanya musu Fanka a dakin kwanansu, wanda hakan zai ba su damar samun wadatacciyar iska.

3- Shayar Da Su Wadataccen Ruwan Sha:

Tanadar musu da wadataccen ruwan sha, na taimaka musu wajen samun sinadaran da za su kara inganta rayuwarsu da kuma jurewa tsananin zafin rana.

Kazalika, ana bukatar masu kiwon su rika zuba musu garin sinadarin ‘glucose da amino acids’, domin kara musu karsashi da kuma kara karfafa garkuwar jikinsu.

4- Sama Musu Da Sauyin Ciyar Da Su Abinci:

Ana bukatar masu kiwonsu, su rika ciyar da su abinci mai dauke da sinadari kamar na ‘Bitamin E da selenium’, wadanda za su taimaka wa lafiyarsu.

Wadannan sinadarai, na matukar bayar da gudunmawa wajen ba su kariya daga jin tsananin zafin rana.

5- Sanya Ido Kan Yiwuwar Barkewar Wata Cuta:

Ana bukatar mai kiwon kajin ya tabbatar yana yawan sanya ido kan kajin, domin gano wasu alamomin da za su iya sanya su ji tsananin zafin rana ko kuma kamuwa da wasu kwayoyin cuta, musamman domin daukar matakan gaggawa na kare lafiyarsu.

Ana kuma bukatar mai kiwonsu ya tabbatar yana ciyar da su abinci mai gina jiki, wanda hakan zai taimaka musu daga saurin kamuwa da kwayoyin cututtuka.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: a dakin kwanansu bukatar mai Ana bukatar ana bukatar

এছাড়াও পড়ুন:

Cibiyar Yaƙi da Ta’addanci Ta Yaba Wa Gwamna Lawal Kan Matakan Yaƙi Da ‘Yan Bindiga A Zamfara

A nasa jawabin, Gwamna Dauda Lawal ya yaba da ziyarar da cibiyar ta kai Zamfara domin duba ƙoƙarin gwamnati na magance matsalar rashin tsaro a jihar.

 

“Ina yawan cewa, idan ku ka yi ƙoƙarin shawo kan Zamfara yadda ya kamata ta fuskar rashin tsaro, za ku magance kashi 80 na matsalolin tsaro a Arewa.

 

“Daga dukkan tsare-tsaren da na gani ya zuwa yanzu, mun mallaki abin da ake buƙata domin tunkarar waɗannan ƙalubale bisa tuntubar juna da haxin gwiwa tsakanin jihar Zamfara da ofishin mai ba shugaban ƙasa shawara kan harkokin tsaro, wannan abin a yaba ne.

 

“Na yi farin ciki da jin cewa Tarayyar Turai ta ware wasu kuɗaɗe, duk da cewa za mu samar da wani asusu, a Zamfara a shirye muke mu ba da tallafin, idan kun shirya gobe, mu ma mun shirya.

 

“Mun shirya, kuma ƙofar mu a buɗe take, duk wani abu da zai kawo sauyi mai kyau a Zamfara muna maraba da shi, muna buƙatar tsari na abin da ku ke yi domin mu ci gaba da bin diddigin lamarin, zan samu wata tawaga da za ta riƙa hulɗa da cibiyar yaƙi da ta’addanci.

 

Tun da farko, Shugabar Rigakafi da Yaƙi da Ta’addanci (PCVE), Ambasada Mairo Musa Abbas ta ce, tawagar ta zo jihar Zamfara ne a madadin mai baiwa shugaban ƙasa shawara kan harkokin tsaro Mallam Nuhu Ribadu da kuma kodinetan yaƙi da ta’addanci na ƙasa, Manjo Janar Adamu Garba Laka. “Muna nan a matsayin wani bangare na dabarun bayar da shawarwari na ƙasa baki ɗaya.”

 

“Muna son sake gode muku bisa irin karramawar da ka yi mana a Jihar Zamfara da kuma irin shugabancin da ka yi wa al’umma, muna sa ran haɗin kai don ganin cewa Zamfara ta zama kan gaba wajen yaƙi da ‘yan bindiga.”

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Xi Ya Jaddada Muhimmancin Tsara Nagartaccen Shirin Raya Tattalin Arziki Da Zamantakewar Al’umma Tsakanin 2026-2030
  • An ɗaure ’yar shekara 80 a kurkuku saboda dukan jikarta da silifas
  • NEMA Ta Karɓi ‘Yan Nijeriya 203 Da Suka Maƙale A Libya
  • Rashin tsaro: Gwamnan AbdulRahman Ya Gana Da Sarakuna Masu Daraja Ta Daya A Jihar Kwara 
  • Kungiyar Amnesty International Ta Kafa Hujja Kan Ta’asar’Yan Sahayoniyya A Gaza
  • Jaridar The Guardian Mafi Yawan ‘Yan Gudun Hijiran Sudan Ne A Gidan Yarin Kasar Girka
  • Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Jadadda Cewa: Duk Wani Harin Wuce Gona Da Iri Kan Iran Zai Fuskanci Mayar Da Martani
  • Jiragen Yakin Amurka Sun Kashe Mutane Da Dama A lardin Sa’ada Na Kasar Yemen
  • Cibiyar Yaƙi da Ta’addanci Ta Yaba Wa Gwamna Lawal Kan Matakan Yaƙi Da ‘Yan Bindiga A Zamfara
  • Dukan farar hula saboda sanya kayan sojoji kuskure ne — Janar Chibuisi