Hanyoyi Biyar Na Kare Kajin Gidan Gona Daga Tsananin Zafi
Published: 12th, April 2025 GMT
Hanyoyi Biyar Da Mai Kiwon Kajin Gidan Gona Zai Kare Kajinsa Daga Tsananin Zafin Rana.
1- A Tabbatar An Sama Musu Wadacciyar Iska A Dakin Kwanansu:
Ana bukatar mai kiwon kajin ya tabbatar ya sama musu wadatacciyar iska a dakin kwanansu, ana kuma bukatar a yi wa shigifar dakinsu fenti yadda za ta rika rage zafin ranar da kuma samar da kayan koyon da za su sanyaya dakin kwanansu.
Haka kuma, ana bukatar a rika sanya musu na’urar da ke sanyaya daki, wadanda za su rika rage zafin ranar, akalla na’urar ta kasance mai ma’unin yanayi daga 5 zuwa 10°C.
2- Sanya Na’urar Sanya Daki:
Domin samun saukin yanayin zafin rana, ana bukatar mai kiwo ya sanya musu na’ura a dakin kwanansu, domin rika sanyaya dakin, yadda jikinsu zai rika yin sanyi.
Ana kuma bukatar masu kiwon, su rika sanya musu Fanka a dakin kwanansu, wanda hakan zai ba su damar samun wadatacciyar iska.
3- Shayar Da Su Wadataccen Ruwan Sha:
Tanadar musu da wadataccen ruwan sha, na taimaka musu wajen samun sinadaran da za su kara inganta rayuwarsu da kuma jurewa tsananin zafin rana.
Kazalika, ana bukatar masu kiwon su rika zuba musu garin sinadarin ‘glucose da amino acids’, domin kara musu karsashi da kuma kara karfafa garkuwar jikinsu.
4- Sama Musu Da Sauyin Ciyar Da Su Abinci:
Ana bukatar masu kiwonsu, su rika ciyar da su abinci mai dauke da sinadari kamar na ‘Bitamin E da selenium’, wadanda za su taimaka wa lafiyarsu.
Wadannan sinadarai, na matukar bayar da gudunmawa wajen ba su kariya daga jin tsananin zafin rana.
5- Sanya Ido Kan Yiwuwar Barkewar Wata Cuta:
Ana bukatar mai kiwon kajin ya tabbatar yana yawan sanya ido kan kajin, domin gano wasu alamomin da za su iya sanya su ji tsananin zafin rana ko kuma kamuwa da wasu kwayoyin cuta, musamman domin daukar matakan gaggawa na kare lafiyarsu.
Ana kuma bukatar mai kiwonsu ya tabbatar yana ciyar da su abinci mai gina jiki, wanda hakan zai taimaka musu daga saurin kamuwa da kwayoyin cututtuka.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: a dakin kwanansu bukatar mai Ana bukatar ana bukatar
এছাড়াও পড়ুন:
Amurka za ta tallafa wa Nijeriya daƙile matsalar tsaro
Gwamnatin Najeriya ta ce Amurka ta amince za ta ƙara faɗaɗa haɗin gwiwar tsaro tsakaninsu, wanda ya haɗa da samar da karin bayanan sirri, makamai da sauran kayan yaƙi, domin ƙarfafa yaƙi da ’yan ta’adda da ƙungiyoyin masu tayar da kayar baya a ƙasar.
Hakan na ƙunshe ne cikin wata sanarwa da Mashawarci na Musamman ga Shugaban Ƙasa Bola Tinubu kan Bayar da Bayanai da Tsara Dabaru, Bayo Onanuga ya fitar a ranar Litinin.
Atiku ya karɓi katin jam’iyyar ADC a hukumance Jarumin fina-finan Indiya Dharmendra ya rasuWannan dai ya biyo bayan jerin tattaunawa da aka gudanar a Washington tsakanin manyan jami’an Najeriya da na Amurka, domin zurfafa dangantakar tsaro da ƙulla sabbin hanyoyin haɗin gwiwa.
Tawagar Najeriya ƙarƙashin jagorancin mai ba shugaban ƙasa shawara kan tsaro, Nuhu Ribadu, ta gana da jami’an majalisar dokokin Amurka, Fadar White House, ma’aikatar harkokin waje, da hukumomin tsaro na ƙasar.
A cikin tawagar akwai Antoni Janar na Tarayya, Lateef Fagbemi; Shugaban Ma’aikatan Tsaro, Janar Olufemi Oluyede; Shugaban Leƙen Asirin Tsaro, Laftanar Janar Emmanuel Undiandeye; da Sufeto Janar na ’Yan Sanda, Kayode Egbetokun, tare da wasu wakilai daga ofishin mai ba shugaban ƙasa shawara kan tsaro.
A yayin ganawar, tawagar Najeriya ta ƙaryata zargin da Shugaban Amurka Donald Trump ya yi na cewa ana kashe Kiristoci a ƙasar, tana mai cewa matsalolin tsaron ƙasar babu wanda suka ƙyale domin kuwa suna shafar al’ummomi daban-daban ba tare da la’akari da addini ko ƙabila ba.
Zargin na Trump ya haifar da ƙalubale da dama a cikin ƙasar, inda hannayen jari suka zube, baya ga ta’azzarar matsalolin da ake gani a ’yan kwanakin nan.