Shugaban Hukumar Makamashin Nukliya Ta Kasar Iran Ya Ce Dukka Ayyukan Makamashin Nukliya A Cikin Gida Suna Tafiya Da Karfinsu
Published: 12th, April 2025 GMT
Shugaban hukumar makamashin nukliya na kasar Iran ya ce kasashen wamma suna son kebe kansu da fasahar nukliya a tsakaninsu.
Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya nakalto Muhammad Eslamu shugaban hukumar AEOI yana fadar haka a jiya Jumma’a ya kuma kara da cewa kamfanin makamashin nukliya na kasar Iran ya kafa a kasar Iran kuma ba wanda ya isa ya kauda shi.
Ya ce JMI ta wuce wasu kasashen yamma a ayyuka da kuma sani da sarrafa makamashin Uranium, wanda ya tada hankalin wadannan kasashe, kuma suke sun han awasu kasashen duniya bin sawun kasar Iran na zama yentattu a wannan fage.
Islami ya kara da cewa kamfanin makamashin nukliya na kasar Iran ya kai wani matsayinda yana taiamakawa sauran kamfanoni na cikin gida ba tare da bukatar dogaro da kwararru ko kuma taimakon kasashen waje ba. Ya ce a halin yanzu iran na samar da wutan lantarki mai karfin magewats 20,000 tare da Makamashin Nukliya.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: makamashin nukliya na kasar Iran ya
এছাড়াও পড়ুন:
Iyaye Sun Yi Fitowar Farin Dango Don Yi Wa “Yayansu Allurar Rigakafi a Sule-Tankarkar
Daga Usman Muhammad Zaria
Aikin rigakafin watan Disamba a karamar hukumar Sule-Tankarkar ta jihar Jigawa ya samu gagarumar nasara, yayin da iyaye suka fito kwansu da kwarkwata domin tabbatar da cewa an yi wa ’ya’yansu cikakken rigakafi.
Wasu daga cikin iyayen da suka kawo ’ya’yansu domin karbar rigakafin yau da kullum da na shan inna sun bayyana jin dadinsu kan yadda aka gudanar da aikin cikin kwanciyar hankali.
Daya daga cikinsu, Malama Ummahani Danbala, ta ce an wayar da kan jama’a sosai ta hannun mata ’yan sa-kai a unguwarsu, inda aka karfafa gwiwar iyaye mata su kawo ’ya’yansu domin karbar rigakafin yau da kullum da na shan inna.
Malam Yunusa, wani mai sa ido a karamar hukumar, ya bayyana gamsuwarsa da yadda aka gudanar da aikin rigakafin a yankin.
A cewarsa, aikin wayar da kan jama’a ya yi matukar tasiri, domin mutane na kawo ’ya’yansu da kansu ba tare da kin amincewa da rigakafin ba.
Yunusa ya bayyana cewa duk da kasancewar karamar hukumar tana kan iyaka, aikin ya gudana cikin nasara, sakamakon hadin gwiwar da aka samu daga dukkan masu ruwa da tsaki.
Ya kara da cewa ana sa ran rigakafin yara kusan 45,221, inda aka yi niyyar kai rigakafin makarantu da wuraren ibada domin gano yaran da ba a musu ba.
Rediyon Najeriya ya ruwaito cewa karamar hukumar na da cibiyoyin lafiya guda 28, kuma aikin rigakafin ya gudana cikin kwanciyar hankali a al’ummomin Ablasu, Kings, Amanda, Togai, Nagwamatse da Hannun Giwa.
Ana sa ran kammala zagayen rigakafin shan inna na watan Disamba a ranar Juma’a a fadin kananan hukumomi 27 na jihar Jigawa.