Shugaban Hukumar Makamashin Nukliya Ta Kasar Iran Ya Ce Dukka Ayyukan Makamashin Nukliya A Cikin Gida Suna Tafiya Da Karfinsu
Published: 12th, April 2025 GMT
Shugaban hukumar makamashin nukliya na kasar Iran ya ce kasashen wamma suna son kebe kansu da fasahar nukliya a tsakaninsu.
Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya nakalto Muhammad Eslamu shugaban hukumar AEOI yana fadar haka a jiya Jumma’a ya kuma kara da cewa kamfanin makamashin nukliya na kasar Iran ya kafa a kasar Iran kuma ba wanda ya isa ya kauda shi.
Ya ce JMI ta wuce wasu kasashen yamma a ayyuka da kuma sani da sarrafa makamashin Uranium, wanda ya tada hankalin wadannan kasashe, kuma suke sun han awasu kasashen duniya bin sawun kasar Iran na zama yentattu a wannan fage.
Islami ya kara da cewa kamfanin makamashin nukliya na kasar Iran ya kai wani matsayinda yana taiamakawa sauran kamfanoni na cikin gida ba tare da bukatar dogaro da kwararru ko kuma taimakon kasashen waje ba. Ya ce a halin yanzu iran na samar da wutan lantarki mai karfin magewats 20,000 tare da Makamashin Nukliya.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: makamashin nukliya na kasar Iran ya
এছাড়াও পড়ুন:
Hukumar Hisbah Ta Rufe Wani Wuri da Ake Zargin Ana Aikata Badala A Kano
Daga Khadijah Aliyu
Hukumar Hisbah ta Jihar Kano ta kama wasu samari bakwai da ke shiga irin ta mata da aikata badala a wani shahararren gurin nishadi da ke kan titin Zoo Road a karamar hukumar Kano Municipal.
Yayin tabbatar da faruwar lamarin ga Rediyon Nijeriya, Mataimakin Kwamanda Janar na hukumar Hisbah, Sheikh Mujahid Aminudeen Abubakar, ya ce an kama samarin da ke kasa da shekaru 23 bayan samun bayanan sirri daga wani mai kishin ƙasa.
Mai bayar da bayanan ya sanar da cewa mmatasn da aka fi sani da ‘Yan Daudu, suna yawan zuwa wurin, inda ake zargin cewa motocin mutane daban-daban ke zuwa su ɗauke su.
Sheikh Mujahid ya bayyana cewa binciken farko ya nuna cewa matasan sun fito ne daga jihohin Kogi, Bauchi da Kano.
Ya ƙara da cewa yayin gudanar da aikin, jami’an Hisbah sun kuma kama wani saurayi da wata budurwa da aka same su tare a cikin babur mai ƙafafu uku, sannan kuma an gano wata yarinya da aka ce ta bace a Sakkwato, aka kuma maida ta ga iyayenta.
Mataimakin Kwamanda Janar din ya ƙara da cewa hukumar za ta rufe wurin nishadin saboda zargin ɓoye ƙananan yara da ke aikata munanan ayyuka.
Ya ce za a mika matasan da aka kama tare da masu kula da wurin ga hukumomin da suka dace domin ci gaba da daukar mataki.
Sheikh Mujahid ya tabbatar da jajircewar Hisbah na kawar da dukkan nau’o’in munanan dabi’u a jihar, tare da kira ga jama’a da su rika kai rahoton duk wata matsala ko abin da suke shakku ga hukumar Hisbah ko wasu hukumomi da suka dace.