Shugaban hukumar makamashin nukliya na kasar Iran ya ce kasashen wamma suna son kebe kansu da fasahar nukliya a tsakaninsu.

Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya nakalto Muhammad Eslamu shugaban hukumar AEOI yana fadar haka a jiya Jumma’a ya kuma kara da cewa kamfanin makamashin nukliya na kasar Iran ya kafa a kasar Iran kuma ba wanda ya isa ya kauda shi.

Sabanin abinda kasashen yamma suke so na hana sauran kasashen duniya mallaka fasahar nukliya, da kuma dogara da su kadai, su bada abinda suka ga dama ko  su hana gaba daya.

Ya ce JMI ta wuce wasu kasashen yamma a ayyuka da kuma sani da sarrafa makamashin Uranium, wanda ya tada hankalin wadannan kasashe, kuma suke sun han awasu kasashen duniya bin sawun kasar Iran na zama yentattu a wannan fage.

Islami ya kara da cewa kamfanin makamashin nukliya na kasar Iran ya kai wani matsayinda yana taiamakawa sauran kamfanoni na cikin gida ba tare da bukatar dogaro da kwararru ko kuma taimakon kasashen waje ba. Ya ce a halin yanzu iran na samar da wutan lantarki mai karfin magewats 20,000 tare da Makamashin Nukliya.

     

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: makamashin nukliya na kasar Iran ya

এছাড়াও পড়ুন:

Hajjin Bana: Kamfanoni 4 da za su yi jigilar maniyyata — NAHCON

Hukumar Alhazai ta Nijeriya NAHCON ta sanar da soma jigilar maniyyatan bana zuwa Saudiyya daga ranar 9 ga watan Mayu yayin da take tabbatar da kammala shirye-shirye aikin Hajjin bana.

Hukumar ta bayyana hakan ne bayan wata ganawa da shugabanta da wakilan majalisar gudanarwa suka yi da Mataimakin Shugaban Ƙasa Kashim Shettima.

An daƙile yunƙurin juyin mulki a Burkina Faso Abubuwa 5 da ya kamata ku sani kan mutuwar Fafaroma Francis

Mataimakin shugaban kasar ne ya gayyaci shugaban hukumar, Farfesa Abdullah Saleh Usman da wakilan sashen gudanarwa zuwa ganawar a ofishinsa domin sanar da shi inda aka kwana game da shirye-shiryen aikin hajjin.

“Mun yi masa bayani game da shirye-shiryenmu a Makkah da Madina da Arafa kuma ya gamsu, har ma ya ba mu umarnin yadda za mu haɗa kanmu mu yi aikin har zuwa ƙarshensa.”

Kazalika, shugaban ya ce suna sa ran kammala aikin kwashe maniyyatan a ranar 24 ga watan Mayu.

Hukumomi sun ce mutum 43,000 ne za su je aikin Hajjin daga Nijeriya a wannan shekara yayin da a bara mutum kusan 95,000 ne suka yi ibadar.

“A shekarar da ta wuce muna da alhazai 95,000, kamfonin jigila uku muka bai wa aiki. Yanzu da muke da alhazai 43,000, mun ɗauki kamfonin huɗu. To ina maganar ƙarancin jirage a nan?,” in ji farfesan.

Bayanai sun ce kamfonin sufurin jiragen da za su yi jigilar maniyyatan sun hada da Airpeace — 5,128 da Flynas — 12,506, sai Max Air — 15,203 da kuma Umza Air — 10,163.

A ’yan makonnin nan ne ’yan majalisar gudanarwar hukumar suka rubuta wa Kashim Shettima koke, suna zargin shugaban NAHCON, Farfesa Abdullah Saleh da mayar da su saniyar ware wajen gudanar da lamurran hukumar, zargin da shugaban ya musanta.

Hotunan ganawar wakilan NAHCON da mataimakin shugaban kasa:

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kasar Sin Ta Goyi Bayan Rawar Da Hukumar IAEA Ke Takawa Wajen Warware Batun Nukiliyar Iran Ta Hanyar Diflomasiyya
  • Hajji 2025: Hukumar Alhazan Yobe ta gudanar da taro don mahajjata
  • Shugaban Amurka Ya Ce: Natenyahu Ba Zai Hadi Fada Da Jamhuriyar Musulunci ta Iran Ba
  • Jigawa Ta Bude Sabon Babi: Maniyyata Za Su San Masaukansu Tun Daga Gida Najeriya
  • Duniyarmu A Yau: Shiri Kasashen Yamma Na Kashe Dukkan Falasdinwa A Gaza
  • Tabbas Amurka Za Ta Cije A Yakin Haraji Da Ta Kaddamar A Duniya
  • Iran Ta Sami Lambobin Yabo  8 A Wasan Taekwondo Na Duniya
  • Rage Mace-Macen Mata Da Jarirai: Kasar Sin Ta Ba Da Kyakkyawan Misali Ga Kasashe Masu Tasowa
  • CONMEBOL ta buƙaci a faɗaɗa Gasar Kofin Duniya ta 2030
  • Hajjin Bana: Kamfanoni 4 da za su yi jigilar maniyyata — NAHCON