Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Hassa Al-Mujtaba (a) 107
Published: 12th, April 2025 GMT
107-Assalamu alaikum masu sauraro barkammu da warhaka barkammu da sake saduwa a cikin shirimmu na Kissoshin rayuwa shiri wanda yake kawo maku kissoshi wadanda suka zo cikin al-kur’ani mai girma ko cikin wasu littafan wadanda suka hada da Littafin Dastane Rastan na Aya. Shahid Muttahari, ko kuma cikin littafin Mathnawi na maulana Jalaluddin Rumi, ko kuma cikin wasu littafan.
///.. Madalla, masu sauraro idan kuna tare da mu a cikin shirimmu da ya gabata mun ci gaba da kawo maku sirar Imam Alhassan lamami na biyu daga limamai masu tsarki daga iyalan gidan manzon All…(s) kuma da na farko ga Fatimah (s) diyar manzon All..(s).
A cikin shirimmu da ya gabata mun bayyana yadda siyasar khalifa na uku na rabon kudade inda muka bayyana yadda ya kebe wasu daga cikin danginsa na kusa da shi da kudade masu yawa, wannan kuwa duk tare da korafe-korafen wasu daga cikin manya-manyan sahabban manzon All..(s).
Mun ji yadda ya ware kudade masu yawa ya bawa, danginsa banu Umayya wadanda suka hada da Abusufyan, Marwan dan hakan, Da Hakam din, da Abdullahi dan Abisarkh da da sauransu. Wadanda wasunsu sun cutar da manzon All..(s) saida ya la’anesu wasu ya koresu daga madina, wasu daga cikinsu ya bada umurnin a kashesu ko da an gansu rike da rigar dakin Kaaba.
Sannan ya nisanta dangin manzon All…(s) a cikin mafi yawan al-amuransa, sannan kamar yadda zamu gani, ya nisantar da wadanda suke tare da su. Ya kuma wulakantasu da sauransu.
Wani abin mamaki da khalifa Uthman yayi shi ne, ya dauki gonar Fadak, wacce ya ga yadda Zahra (d) diyar manzon All..(s) ta kai ruwa rana da Khalifa Abubakar ya mayar mata don hakkinta ne, wanda manzon All..(s) ya bata, kyauta gareta ga kuma yayanta a bayanta, ya bawa Marwan dan Hakan.
Idan kuda tare da mu a cikin shirye-shiryemmu na baya, mun bayyana cewa ayoyin alkur’ani ne suka sauka suka mallakawa manzon All..(s) gonar fadak sannan wasu ayoyin suka sauka suka mallakawa Zahrah(s) wannan gonar Amma Khalifa Abubakar ya kwace ta daga Zahrah (a) sannan daga karshe bayan shekaru kimani 16 gonar da Fadak ta zama mallakar dan wanda manzon All…(s) ya kora daga Madina.
Kamar yadda muka bayyana wannan halin da Khalifa Uthman ya kaiga, sahabban manzon All..(s) da dama sun koka a gabansa, sun bayyana masa cewa bai yi dai-dai.
Al-amarin ya kaiga, Andurrahman dan Auf, wanda ya zabe shi a matsayin Khalifa, bayan wafatin Khalifa na biyu, ya fahinci cewa yayi barna, ya je yana fadawa Aliyu dan Abitalib (a) kan cewa, ka dauka takobinka, ni ma zan dauki takobina, don ya sauya daga alkawalin da yayi mani. Sai Imam Ali (a) ya yi banza da shi. Sannan ya kai ga a lokacinda Abdurrahman dan Auf zai mutu ya bar wasiyya kada a bar Khalifa Uthman yayi masa sallah.
A lokacinda yake bada wannan kyauta da danginsa, yana cewa su dangi nane, sai suka ce masa, shin Abubakar da Umar basa da dangi ne?, sai ya amsa da cewa, Abubakar da Umar sune neman lada wajen All..saboda hana danginsu dukiyar jama’a dake hannunsu, amma ni kuma ina neman ladar amma da basu dukiyar.
A lokacinda sukar ta yi yawa, sai Khalifa Uthman ya nemi afwar mutane, kan dukiyar jama’a da ya bawa danginsa.
Amma yayi haka ba tareda ya dawo da dukiyoyin da ya basu ba, kuma bai san cewa ba’a kyauta sai da dukiyar da ya mallaka ba?.
Amirulmuminina (a) ya bada kekkyawar misala a lokacinda mutane suka dora masa khalifanci a bayan kissan Khalifa Uthman.
Inda yayansa Akili dan Abitalib ya zo wajensa a kufa, cikin talaucinsa, ya bukaci Amirul muminina (a) ya bashi dukiya daga baitul malin musulmi kamar yadda Khalifa Usman yake yi don ya biya basussukan da ake binsa.
Sai nawa ne basussukan da ake binka? Sai yace . Dinari dub 100.
Sai Imam (a) yace, bani da su, amma ka jira idan an yi albashi in baka wani abu daga cikinsa.
Sai Akil yace masa, baitul Mali yana hannunka amma kana cewa sai ka rabon albashinka ya fita? Sai Imam yace masa, kana umurtata in baka dukiyar musulmi, bayan sun sanyani amintaccensu a kanta?. Har zuwa karshen maganarsu.
Kunji yadda shugaban kuma khalifan musulmi yakamata ya kasance.
Banda haka hadisai da dama sun tabbata daga manzon All..(s) wadan nan wadanda Khalifa Uthman yake rabawa dukiyar musulmi, la’ananu ne a cikin alkur’ani mai girma.
An karbo Hadisi daga Hakika ibnu Abihatin ya rawaito daga Ibn Amru daga manzon All..(s) yana cewa : Na yi mafarkin yayan Hakam dan Abi Ass sun haw kan mimbarori kamar birrai, sai All..ya sauka da iyar da take cewa {Kuma bamu sanya mafarkin da muka nuna maka ba face fitinah, ga mutane, da kuma la’ananniyar itaciya}…yana nufin Hakam da yakan da yayansa,
Ummulmuminina A’isha ta fadawa Marwan dan Hakam kan cewa na ji manzon All..(s). yana fadawa babanka, (Abil Ass dan Umayya) Ku ne itaciyar da aka la’anta a cikin alkur’ani, kuma hakika ya hana son wadanda suke adawa da shi, ya haramta sadar da zumunci da su. All..T yana cewa: {Ba zakat aba samun mutanen wadanda suka yi Imani da All..da ranar lahira suna son wanda suke kiyayya da All..da manzonsa (s).ko da kuwa sun kasance iyayensu, ko yayansu, ko yan uwansu ko kuma danginsu ba}. Akwai hadisai da dama da suka yi magana a kan wanna sanna.
Sannan dangane da walid dan uqba wanda khalifa na uku ya sa a matsayin walin Kufa, a baya mun bayyana yadda ya sami sabani da Abdullahi dan Masa’ud wanda ya kasance mai kula da baulmalin musulmi a Kufa, amma daga baya khalifa ya fadawa masa cewa shi mai ajiya ne amma bai da iko ya fadi inda za’a kashe kudaden.
A nan ne ya bar aikin ya kuma koma madina.
To wannan Walid din da nassan Al-kur’ani shi fasiki, inda All..Ta yake cewa : {..idan fasiki ya zo maku da labari ku nemi bayani ..}. Mazon All..ya aike shi zuwa karban Zakka a wajen Banu Mustalak, ya karbi zakka, amma sai ya je ya zagaya ya dawo yace aiki sun ki su bayar, sai manzon All..(s) ya shirya yaki zuwa can, kafin ya isa wannan ayar ta sauka ta kira shi fasiki.
Banda haka walid mutum ne mai cike da kiyayyan ga musulunci saboda mahaifinsa Ukbatu dan Abi rabii, ya cutar da manzon All…(s) a makama, inda ya tofa yau a faskansa ya zageshi, sannan manzon All..(s) ya ce masa idan na sameka a wajen makka sai na kashe ka.
Sai gashi ya je yakin Badar aka kama shi a cikin fursinonin yaki, manzon All..(s) ya fidda shi daga sauran fursinoni ya kuma sa Aliyu ya sare wuyarsa ya kashe shi. Don haka wadannan al-amura suka hadu suka sanya walid mikiyin manzon All..(s) da Aliyu (a) da ma addinin musulunci, to yaya Khalifa Uthman zai bashi shigabanci a kan musulmi, a kuma manya manyan birane kamar Kufa?
Garin kufa babban gari ne wanda ya tattara baki daga cikin sabbin musulunta da bayi wadanda suke bukatar sahabbai koprarro a cikin sanin hukunce hukuncen addini don ko koya masu addinin, su nuna masu halaye masu kyua na addini, wadanda basu musulunta daga cikinsu su jawosu zuwa ga addinin musulunci, da halaye masu kyau ko hikimomi na addini. Irin wadanan musulmi idan sun ga abinda Walid yayi ko yake yi, ina zasu yi sha’awar shiga addinin musulunci.?
Maganar walida bata karewa, don bayan ya sha giya sannan ya bada sallar asubaha yana cikin maye, sannan yayi masu sallar asubaha raka’o’ii 4 sannan ya juya y ace masu in kara maku ne? banda haka ya yi aman giya a mihrabin sallah. Sai mutanen kufa suka ga cewa ba zasu iya ba.
Suka cire zubensa na zinari suka je madina suka kai kararsa wajen Khalifa. Khalifa Uthman bai ji dadi ba, sai suka garzaya zuwa wajen Imam Aliyu dan Abitalib (a), wanda ya shiga wajen Khalifa ya yi masa magana, a nan ne ba da sonsa ba, ya aikawa walid ya dawo Madina, da ya dawo, wadan mutane suka zo suka shaida kan cewa ya sha giya. Sannan walida ya kasa musanta hakan. Sai hadda ya tabbata a kansa. Amma aka rasa wa zai zo ya yi masa bulala 80 wanda shi ne haddin All..ga wanda ya sha giya aka kasa, samu saboda an san irin kusancinsa da Khalifa.
A nan ne sai Aliyu dan Abitalib (a) ya zo ya dauki bulala ya zaneshi, ya zartar masa da hadda, Khalifa yana turmude da fuskansa, har yana tsawo ga Aliyu kada ka masa haka, kada ka masa haka..!.
Ana gama wannan sai Khalifa ya tausaya masa, ya bashi aikin karbo zakka daga kabilar Kalb, ya je ya karbo zakka, ya dawo Khalifa ya bashi dukkan abinda ya karbo, kamar yadda muka yi bayani a baya.
Sannan abin mamaki sai Khalifa ya tura Sa’id dan Ass wanda shi ma matashi ne daga cikin matasan banu umayya. Sannan halayensa mai yuwa kadan ne ya fi Walid. Shima ya je yayi tasa barnan a kufa.
Kada ku manta Imam Hassan (a) wanda muke kawo maku sirarsa yana sane da wadannan abubuwa, kuma yana rike da su. Saboda su zama masa darasi kan yadda zai tafiyar da al-amura a lokacinda khalifanci zai shiga hannunsa.
Ya san yadda zai fuskance wadannan mutane, wadanda suka zama fitina babba a cikin musulmi kawo ke tsammani.
Masu sauraro a nan zamu dasa aya a cikin shirimmu nay au sai kuma wata fitowa idan All…ya kaimu wassalamu alaikum wa rahmatullahi wa barakatuhu.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: Khalifa Uthman ya wadanda suka masu sauraro kamar yadda
এছাড়াও পড়ুন:
’Yan bindiga sun kai wa sojoji hari a ranar da ake zaman sulhu
Sojoji biyu sun ji rauni bayan wani harin kwanton baya da ’yan bindiga suka kai kan ayarin motocin Kwamandan kwamandan Rundunar Sojoji ta 382 Ƙaramar Hukumar Faskari ta jihar Katsina.
Lamarin ya faru ne a ƙauyen Ruwan Godiya, kan hanyar Sheme–Kankara, lokacin da tawagar Operation Fansan Yamma (OPFY) ke wucewa.
Ganau sun ce sojojin na kan hanyar ziyartar sansanonin sojoji a yankunan Faskari da Mabai da Ɗan Ali lokacin da aka kai musu hari.
Sai dai sun yi nasarar tunkarar ’yan bindigar har suka kuvuta, kodayake sojoji biyu sun samu raunuka na harbi kuma aka kai su asibitin sojoji domin jinya.
An kai wa sojojin harin ne a rana ɗaya da shugabannin al’ummar Faskari suka zauna da wakilan ’yan bindiga domin rattaba hannu kan yarjejeniyar zaman lafiya.
’Yan bindiga sun sace mutum 40 a masallaci a Zamfara Hauhawar farashi ya ragu a watan Agusta — NBSHakan ya sanya Faskari zama ƙaramar hukuma ta baya-bayan nan da ta shiga irin wannan sulhu bayan ƙananan hukumomin Ɗanmusa da Jibia, Batsari da Ƙanƙara, Kurfi da Musawa.
Yarjejeniyar na neman kawo ƙarshen tashin-tashina, garkuwa da mutane da kuma ƙaura da ake fama da su a jihar.
Amma akwai shakku kan ɗorewar ta, domin wasu daga cikin shugabannin ’yan bindigar sun bayyana cewa sulhun ya shafi ƙananan hukumomin da suka shiga yarjejeniyar kawai, lamarin da ya janyo tsoron cewa sauran wuraren da ba su rattaba hannu ba, suna iya ci gaba da fuskantar hare-hare.
Wasu mazauna Ruwan Godiya sun ce ayyukan ’yan bindiga na ƙara ta’azzara a sassan Katsina duk da yarjejeniyar sulhun da aka ƙulla da wasu daga cikin shugabanninsu.
Masana sun bayyana cewa hakan ya nuna raunin irin waɗannan tsare-tsare na sulhu, tare da tabbatar da buƙatar ƙarin sa-ido a yankunan da ke fuskantar barazana.
Sulhun Faskari da ’yan bindigaƘaramar Hukumar Faskari ta zama ta baya-bayan nan a Jihar Katsina da ta shiga yarjejeniyar zaman lafiya da ’yan bindiga, domin kawo ƙarshen kashe-kashe, garkuwa da mutane da kuma ƙaura da ake fama da su a yankin.
Kamar sauran sulhunan da aka kulla a ƙananan hukumomi guda shida, sharuddan yarjejeniyar sun ba wa ’yan bindiga damar shiga garuruwa da kasuwanni da asibitoci.
Haka kuma, za su sako duk wanda aka yi garkuwa da shi ba tare da sharaɗin ba. A sakamakon haka, al’umma za su iya komawa gona da kasuwanni cikin kwanciyar hankali ba tare da fargabar farmaki ba.
Yarjejeniyar ta biyo bayan taron al’umma da aka yi a Faskari, inda fitaccen shugaban ’yan bindiga, Ado Aliero, wanda ake nema ruwa a jallo, ya tabbatar wa manoma tsaronsu.
“Daga yau kowa ya koma gona cikin kwanciyar hankali; ba abin da zai faru a Faskari baki ɗaya,” in ji Aliero cikin wani bidiyo da Aminiya ta gani.
Aliero ya ɗora laifin rushewar yarjejeniyar da aka yi a baya kan cafke ɗansa, yana mai cewa ya bi duk hanyoyin lumana, amma abin ya gagara, kafin ya koma tayar da hankali.
A wani bidiyo daban kuma, wani ɗan bindiga da aka gani sanye da rigar harsashi ya zargi hukumomi da nuna wariya da rashin adalci, yana mai cewa sulhu na gaskiya zai tabbata ne kawai idan aka yi adalci ga kowa.
Sai dai duk da rahotannin da ke cewa jami’an gwamnati da na tsaro sun halarci taron, gwamnatin Jihar Katsina ta nesanta kanta daga wannan yarjejeniyar.
Akwai masu kawo cikas — Gwamna RaɗɗaGwamnan Jihar Katsina, Malam Dikko Umar Raɗɗa, ya ce duk da irin ƙalubalen tsaro da ake fuskanta, gwamnatinsa na samun ci-gaba, sai dai akwai masu ƙoƙarin kawo cikas.
Ya bayyana haka ne a wani taron shawarwari da aka gudanar a Katsina ranar Lahadi, wanda ya tattaro manyan masu ruwa da tsaki ciki har da sarakunan gargajiya da shugabannin siyasa da shugabannin tsaro da masana, ’yan kasuwa da shugabannin addini.
Gwamnan ya ce tsaro ne ginshiƙin ajandar ci-gabansa tare da ilimi da noma da kiwon lafiya da kuma tallafa wa ƙanana da matsakaitan ’yan kasuwa.
Ya sanar da cewa gwamnati za ta gina gidaje 152 ga iyalan da aka raba da muhallansu a Jibia, tare da shirya shirin tallafa wa tubabbun ’yan ta’adda da suka domin kada su koma ɓarna.
Haka kuma ya yaba wa jami’an sa-kai da ƙungiyoyin tsaro na gari da suka taimaka wajen dawo da ƙwarin gwiwa a tsakanin jama’a.
Cikin manyan da suka halarci taron akwai tsohon Gwamna Aminu Bello Masari da dattijo Sanata Abu Ibrahim da fitaccen dan kasuwa Alhaji Ɗahiru Mangal da Sarkin Daura Alhaji Faruk Umar Faruk da tsohon Ministan Sufurin Jiragen Sama, Hadi Sirika, Ministan Gidaje Arc. Ahmed Ɗangiwa, da kuma Hadiza Bala Usman mai ba shugaban ƙasa shawara kan tsare-tsare.
Sauran sun hada da tsohon Daraktan DSS Alhaji Lawal Daura, tsohon Daraktan NIA Ambasada Ahmed Rufai, tsohon Shugaban Kamfanin na NNPC Injiniya Abubakar Yar’adua da Babban Alƙalin jihar Alhaji Musa Ɗanladi, da kuma manyan hafsoshin soja da dama da suka yi ritaya.
Hakazalika, an samu halartar manyan jami’ai, malamai daga jami’o’i da ƙungiyoyin ƙwadago da ƙungiyoyin farar hula da ’yan kasuwa da sauran shugabanni daga sassa daban-daban na jihar.
Gwamna Radda ya jaddada cewa zai ci gaba da karɓar suka da shawarwari daga masu kishin ƙasa, tare da kira ga haɗin kai domin shawo kan matsalolin tsaro da tattalin arziki da jihar ke fama da su.
A nasa vangarenm Mataimakin Gwamnan Jihar Katsina, Faruk Lawal Joɓe, ya bayyana cewa gwamnatin Raɗɗa ta samar da sama da ayyuka 35,903 a fannoni daban-daban ta karkashin manufar “Gina Makomarka.”
Joɓe ya bayyana ce an samar da ayyukan ne ta hanyar ɗaukar malamai da shugabannin unguwanni da jami’an tsaro na sa da mafarauta da sauransu domin su riƙa taka rawa wajen wanzar da zaman lafiya.
Ya kuma yi ƙarin haske kan aikin Sabunta Birane na Katsina State Urban Renewal da ya lashe Naira biliyan 74.9 wanda ya shafi manyan ayyuka a Daura da Funtua da Katsina.
Ayyukan sun haɗa da gina sabuwar hanyar Eastern Bypass mai tsawon kilomita 24, titi mai hannu biyu a cikin Katsina, gyaran tituna a Daura da Funtua, da kuma kammala wasu muhimman hanyoyin karkara.
A nasa jawabin, Kwamishinan Tsaro na Cikin Gida, Dakta Nasir Muazu, ya ce gwamnatin Raɗɗa ta ɗauki matakin rashin tattaunawa da ’yan bindiga.
Ya ce abubuwan da ke haifar da ta’addanci sun haɗa da son zuciya da rikice-rikicen albarkatu da sauyin yanayi, da kuma rashin adalci a cikin al’umma.
Ya ƙara da cewa daga 2011 zuwa 2015 matsalar ta tsaya a ƙananan hukumomi biyar, amma ta bazu zuwa 25 a lokacin tsohon Gwamna Aminu Masari bayan shirin afuwa ya faskara.
Kwamishinan ya bayyana cewa hare-haren soji sun lalata maɓoyar ’yan bindiga da dama, sun buɗe manyan hanyoyi, sannan mutum 628 da suka tsira daga hare-hare sun samu kulawar lafiya a bana.
Ya ce yanzu dakarun Community Watch, masu aikin sa-kai da ’yan banga suna mara baya ga jami’an tsaro da ke amfani da jirage marasa matuƙa da makamai da motocin aiki.
Shugaban Ƙungiyar ƙwadago (TUC) na jihar, Muntari Abdu Ruma, ya gargaɗi gwamnati ta yi taka-tsantsan da yarjejeniyar zaman lafiya da ’yan bindiga lura da yarjejeniyar Kankara ta 2016 da ta gagara.
Haka kuma, shugaban ƙungiyoyin farar hula na jihar, Malam Abdulrahman Abdullahi, ya ce akwai buƙatar ƙarin haɗin kai tsakanin jihohin Arewa maso Yamma wajen yaki da ’yan bindiga. Ya yi nuni da cewa ziyarar da dattawan Katsina suka kai wa Shugaba Bola Ahmed Tinubu a bisa jagorancin Gwamna Raɗɗa ta fara haifar da sakamako mai kyau a Ƙanƙara da Faskari, amma dole a ci gaba da ayyuka cikin tsari.
A nasa ɓangaren, Sanata Ibrahim Tsauri na jam’iyyar adawa PDP, ya ce taron ya fi karkata wajen bayyana nasarorin gwamnati fiye da ba wa mahalarta dama su yi sharhi.
Duk da haka ya ce idan aka ci gaba da irin waɗannan taruka, za su iya kawo sauyi ga jihar bayan shekaru 15 na ƙalubale.
An ce mahalarta taron sun yi alkawarin mara wa gwamnati baya wajen shawo kan matsalar samari, musamman shaye-shaye da sauran laifuka.
Sauran muhimman shawarwarin sun haɗa da haɗe hanyoyin sadarwa a wuri guda da nufin samun nasarar wannan abu da aka sanya a gaba.