A wannan rana a filin jirgin saman Legas, Babafemi ya ce jami’an ‘yansanda sun kama wata ‘yar asalin kasar Ghana mai shekaru 20, mai suna Parker Darren Hazekia Osei, mai shekaru 20 da haihuwa, dauke da fakiti 36 na Loud—wani nau’in tabar wiwi mai karfin gaske, a cikin wata katuwar jakar tafiya mai nauyin kilogiram 19.

40.

Ya ce wanda ake zargin wanda ya bayyana kansa a matsayin dalibin Kimiyyar Kwamfuta a Jami’ar Gabashin Landan, ya taso ne daga birnin Bangkok na kasar Thailand ta hanyar jirgin Ethiopian Airlines, ya kuma amince ya dauko kayan a Bangkok domin kai wa Nijeriya.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Jami’an tsaro sun kama masu garkuwa da mutane 7 a Gombe

Rundunar ’Yan Sandan Jihar Gombe, tare da haɗin gwiwar maharba, sun samu nasarar tarwatsa gungun masu garkuwa da mutane, tare da kama mutum bakwai da ake zargi da aikata laifuka a Jihohin Gombe, Bauchi, Yobe da Adamawa.

Rundunar ta samu nasarar ne bayan kama Abdullahi Ibrahim, mai shekaru 40 daga ƙauyen Tilde a Funakaye, a ranar 23 ga watan Nuwamba 2025.

An harbe manomi saboda rikici kan filin kiwo a Borno DSS ta kama likitan da ke duba ’yan bindiga a dazukan Kwara

An kama shi ne bayan samun bayanan sirri kan hulɗa da masu satar shanu.

Abdullahi, ya amsa cewa yana da hannu a garkuwa da mutane tare da bayyana sunayen waɗanda suke aikata laifin tare.

A cewar kakakin rundunar, DSP Buhari Abdullahi, jami’an Operation Hattara tare da maharba ne suka kai samame maɓoyarsu a ranar 28 ga watan Nuwamba 2025, inda suka kama mutum shida bayan yin artabu.

Waɗanda aka kama sun haɗa da; Usman Mohammed, Hussain Idris, Adamu Tukur,  Ya’u Abdullahi, Ali Umar, Hassan Usman da Abdullahi Ibrahim.

Rundunar ta ce waɗanda ake zargin sun amsa cewa suna da hannu a garkuwa da mutane tare karɓar kuɗin fansa kusan Naira miliyan 150.

Jami’an sun shiga dajin Gadam, inda suka samu bindiga ƙirar GPMG mai jigida guda ɗaya da harsasai takwas bayan wata musayar wuta da suka yi wasu ’yan ta’adda da suka tsere.

Haka kuma an gano suna da hannu wajen garkuwa da wani mutum a ƙauyen Barderi a Akko, a ranar 15 ga watan Janairun 2025.

Sun tsare mutumin na tsawon makonni biyu kafin karɓar Naira miliyan 15 a matsayin kuɗin fansa.

DSP Buhari, ya ce ana cigaba da bincike, kuma za a gurfanar da su a kotu.

Ya roƙi jama’a da su ci gaba da bai wa rundunar sahihan bayanai domin inganta harkokin tsaro.

Rundunar ‘Yan Sandan Gombe ta ce za ta ci gaba da kare rayuka da dukiyoyin al’umma a faɗin jihar.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Jirgin Sojin Saman Najeriya Ya Yi Wani  Hatsari a Neja
  • Iran Ta Zama Zakaran  Duniya A Wasan “Taekwondo” Na Masu Shekaru Kasa Da 21
  • Mutane Biyar Ne Suka Mutu A Wata Musayar Wuta Tsakanin Sojojin Afghanistan Da Pakistan
  • Nakiya ta hallaka yara 4 a Borno
  • Kwastam ta kama jirgin ruwan Brazil ɗauke da hodar iblis a Legas
  • Sabuwar Dokar CBN: Nawa Za a Iya Cirewa a ATM da POS?
  • Shettima Ya Taya Sarkin Gumel Murna Tare da Jinjinawa Gwamna Namadi Bisa Bunkasa Bangaren Noma
  • Jami’an tsaro sun kama masu garkuwa da mutane 7 a Gombe
  • An harbe manomi saboda rikici kan filin kiwo a Borno
  • ’Yan sandan Borno sun kama matashin da ake zargi da kashe makwabciyarsa da wuƙa