Shuwagabannin Afrika ta Kudu, Malasiya da kuma Colombia sun jaddada matsayinsu nah ana jiragen ruwa dauke da makamai zuwa HKI tsayawa a tashishin jiragen Ruwan kasashen su.

Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta nakalto ta nakalto shugaban Afirka ta kudu, Cyril Ramaphosa, Firaiministan kasar Malasiya Anwar Ibrahim da Shugaban kasar Colmbia Gustavo Petro suna fadar haka a wani rubutun hadin guiwa da aka buga a mujallar ‘Foreign Policy’ na wannan makon.

Shuwagabannin sun bayyana cewa yakin da HKI ta durawa Falasdinawa a Gaza, ya nuna yadda tsarin dokokin kasa da kasa suna gaza tabbatar da adalci a duniya.

Labarin ya kara da cewa : Ko mu hada kai mu tabbatar da dokokin kasa da kasa, ko kuma dukkan tsaron ya rushe.

Sun HKI ta aikata laifukan yaki a Gaza wadanda suka hada shafi al-umma a doron kasa, inda a cikin shekara guda ta kashe mutane kimani 61,000 tare da taimakon manya-manyan kasashen duniya ko kasashen yamma.

Kasashen Malasiya da Colombia dai suna cikin kasashen da suke goyon bayan karar da Afirka ta kudu da shigar kan HKI a kotun ICC, kuma ya zuwa yanzu kotun ta fidda sammacin kama shuwagabnnin HKI biyu, Wato Firay ministan kasar Benyamin Natanyaho da kuma tsohon ministan yakinsa Aut Galant.

Har’ila yau rubutun shuwagabannin uku ya yi tir da manufan shugaban kasar Amurka ta kwace Gaza ko kuma korar Falasdinawa daga kasarsu.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Sin Na Fatan Kwamitin Sulhun MDD Zai Goyi Bayan Kuduri Game Da Halin Da Iran Ke Ciki

Rahotanni sun bayyana cewa, kasashen Rasha, da Sin da Pakistan, sun gabatar da wani daftarin kudurin kwamitin sulhun MDD, kan halin da ake ciki a Iran. Game da hakan, kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin Guo Jiakun, ya shaidawa nuni taron manema labarai da aka saba yi a yau Litinin cewa, harin da Amurka ta kai kan wuraren da kasar Iran ta girke na’urorin nukiliya ya saba wa manufar tsarin dokokin MDD, tare da kara ta’azzara tashin hankali a yankin gabas ta tsakiya, don haka, dole ne kwamitin sulhun ya dauki mataki kan batun.

Kakakin ya kara da cewa, kasar Sin na sa ran mambobin kwamitin za su goyi bayan daftarin kudurin, tare da sa kaimin kwamitin ya taka muhimmiyar rawa wajen tabbatar da zaman lafiya, da tsaron kasa da kasa.

‘Yan Bindiga Sun Sace Dukkan Fasinjojin Motar Bas A Jihar Benuwe Yanzu-yanzu: Zanga-zanga Ta Ɓarke A Jami’ar Neja Bayan Kashe Ɗalibi

Dangane da goyon bayan da majalisar dokokin Iran ta nuna game da rufe mashigin tekun Hormuz, mashigin tekun Farisa, da yankin ruwan da ke kewaye da shi muhimmiyar hanyar cinikayyar kayayyaki da makamashi ce ta kasa da kasa. Kuma kasar Sin ta yi kira ga kasashen duniya da su kara kokarin sa kaimi ga kwantar da kurar rikici, don magance karin tasiri da tashin hankalin da ake fuskanta a shiyyar ka iya haifarwa ga gaban tattalin arzikin duniya.

Baya ga haka kuma, kakakin ya bayyana cewa, ‘yan kasar Sin 3,125 sun riga sun fice daga kasar Iran lami lafiya, kuma ofishin jakadancin kasar Sin dake Isra’ila, ya taimaka wa ‘yan kasar Sin sama da 500 barin Isra’ila yadda ya kamata, kana ya taimaka wa wasu ‘yan kasar Birtaniya, da Indiya, da Poland wajen barin kasar lami lafiya. (Mai fassara Bilkisu Xin)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Al’ummun Afrika Da Sin Ba Za Su Taba Mantawa Da Gudunmuwar Tawagar Jami’an Lafiya Ta Sin Ba
  • Sin Da Kasashen Musulmi Za Su Kara Zurfafa Dangantakarsu
  • An tura ’yan China 6 kurkuku kan laifin ta’addanci a Nijeriya
  • Sin Na Fatan Kwamitin Sulhun MDD Zai Goyi Bayan Kuduri Game Da Halin Da Iran Ke Ciki
  • Koriya ta Arewa za ta taimaka wa Iran gyara tashoshin nukiliyan da Amurka ta kai hari —Masani
  • Me Ya Sa Kamfanonin Kasa Da Kasa Ke Da Imanin Gudanar Da Harkokinsu A Kasar Sin?
  • Sin Ta Yi Matukar Allah Wadai Da Hare-Haren Da Amurka Ta Kaiwa Iran
  • Amurka za ta gamu da fushinmu kan shigar wa Isra’ila yaƙinta da Iran — Houthi
  • Me Zai Faru Idan Iran Ta Datse Mashigar Hormuz Sanadiyar Hare-Haren Isra’ila?
  • Firaministan Singapore: Jama’ar Sin Suna Da Kwarewar Kirkire-Kirkiren Fasahohi