Sudan Ta Kai Karar HDL A Gaban Kotun Kasa Da Kasa Ta MDD
Published: 11th, April 2025 GMT
Kasar Sudan ta kai kukan HDL a gaban kotun MDD cewa ta keta dokar hana kisan kiyashi ta hanyar taimakawa dakarun kai daukin gaggawa.
A jiya Alhamis kasar ta Sudan din ta bukaci kotun ta kasa da kasa dake karkashin MDD da ta ta fitar da hukunci na gaggawa na bayar da umarni ga HDL da ta kawo karshen kisan kiyashin da aka yi wa kabilar Masalit da sauran al’ummu a cikin tsawon shekaru biyu na yakin basasar kasar.
Ministan shari’a na kasar Sudan Muawia Usman ya bayyana cewa: Kisan kiyashin da dakarun kai daukin gaggawa su ka yi wa al’ummar Masalit da su ka kunshi larabawan yankin Darfur, ya faru ne ta hanyar taimakon kasar Hadaddiyar Daular Larabawa.”
Bayan da ministan na Sudan ya gama shigar da kara, gwamnatin HDL ta bayyana cewa, koken da Sudan din ta yi a kanta bai cika ka’idoji ba, kuma babu dalilai da za su tabbatar da abinda take fada.
Dukkanin kasashen biyu na Sudan da HDL suna cikin wadanda suka rattaba hannu akan yarjejeniyar 1948 wacce ta haramta kisan kiyashi, sai dai kuma kasar ta HDL ta nuna dari-dari akan wasu daga cikin bangarorin yarjejeniyar.
Kotun ta bayyana cewa; dari-darin da kasar ta HDI ta nuna akan wani sashe na yarjejeniyar zai iya hana ci gaba da gudanar da shari’ar.
Tun a cikin watan Aprilu na 2023 ne kasar ta Sudan ta fada cikin yakin basaasa.MDD ta ce fiye da mutane 24,000 ne su ka kwanta daya, yayin da wasu miliyan 14 su ka zama ‘yan gudun hijira, da hakan yake a matsayin kaso 30% na jumillar mutanen kasar.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Shugaban Kasar Azerbaijan Ya Tattauna Da Wakiliyar CMG
Kwanan nan, wakiliyar CMG ta zanta da shugaban kasar Azerbaijan Ilham Aliyev wanda ya kawo ziyarar aiki a kasar Sin. A yayin zantawar, shugaba Aliyev ya waiwayi dadadden tarihin cudanyar kasashen biyu da ma zumuncin da ke tsakaninsu, kuma ya yi imanin da cewa, kasancewar dukkansu kasashe masu tasowa ne, kasashen biyu za su hada hannu wajen bayar da karin gudummawa wajen kiyaye zaman lafiya da ci gaba a duniya.
Shugaba Aliyev ya ce, “Muna ganin kasar Sin jagora ce ga kasashe masu tasowa na duniya, kuma tana taka rawar gani a wajen hada kan kasa da kasa, musamman ma wajen yayata ruhin Bangdun, ciki har da martaba ikon mulki da cikakkun yankunan kasa na sauran kasashe, da rashin tsoma baki cikin harkokin gidan kasashe, da kiyaye zaman daidaito da cudanyar bangarori daban daban, da nuna kin yarda da babakere da sauran danniya a duniya daga kowace kasa ko kungiya.”(Lubabatu)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp