Aminiya:
2025-05-21@17:18:36 GMT

Za a mayar da tubabbun ’Yan Boko Haram cikin al’umma – Gwamna Buni

Published: 11th, April 2025 GMT

Gwamnatin Yobe ta bayyana shirinta na mayar da tubabbun mayaƙan Boko Haram cikin al’ummarsu da aka yi wa shirin kawar da tsattsauran ra’ayi, gyara da sake haɗewa da iyalansu ƙarƙashin rundunar Operation Safe Corridor (OPSC).

Gwamnan Jihar Yobe, Mai Mala Buni ne ya bayyana haka a ranar Alhamis a Damaturu lokacin da ya karɓi baƙuncin tawagar rundunar OPSC ƙarƙashin jagorancin babban hafsan tsaron Nijeriya Janar Christopher Musa.

Hisbah ta warware rigingimu 565 da lalata katan 51 na barasa a Yobe Trust Radio 92.7FM za ta fara shirye-shiryen gwaji

Gwamna Buni, wanda ya samu wakilcin mataimakinsa, Alhaji Idi Gubana ya bayyana ziyarar a matsayin wata dama ta tuntuɓar juna da haɗin gwiwa tsakanin jami’an tsaro da gwamnatin jihar.

Ya koka da yadda rikicin da aka kwashe sama da shekaru 15 ana yi ya laƙume rayukan dubban mutane a Yobe, da lalata dukiyoyin jama’a da na masu zaman kansu tare da raba magidanta da dama da garuruwansu na asali.

Gwamnan ya ce gwamnatin jihar ta gane cewa, ba dukkan ’yan ƙungiyar ta’addancin ne ke shiga cikin kisan kai ba, yana mai cewa tsarin kishin ƙasa ya ba da damar ceto da kuma mayar da waɗanda suka nuna nadama ya zuwa ga al’ummominsu.

“Mun yi imanin cewa, an tura wasu mutane shiga cikin ’yan ta’adda ta hanyar ƙarfi ko koyarwar aƙida.”

“Tare da ci gaba da ƙoƙarinsu, za su iya tuba, gyarawa da komawa rayuwa ta yau da kullun a matsayin ‘yan ƙasa da ke da ‘yanci.” In ji Buni.

Gwamnan ya ce tubabbun ‘yan Boko Haram 390 da suka haɗa da ‘yan asalin Jihar Yobe 54 ne za su kammala karatu tsakanin ranakun 14 zuwa 19 ga Afrilu.

Ya ce, jihar ta samar da wasu tsare-tsare ta hanyar ma’aikatar Jinƙai da kula da bala’o’i domin tabbatar da sake dawo da su cikin al’umma yadda ya kamata.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Baoko Haram Gwamna Buni

এছাড়াও পড়ুন:

Mawaƙan APC sun zargi gwamnati da watsi da su a Jigawa

Wasu mawaƙan jam’iyyar APC da ke Jihar Jigawa, sun bayyana ɓacin ransu kan yadda gwamnatin jihar ta yi watsi da su, duk da irin gudunmawar da suka bayar wajen samun nasarar jam’iyyar a zaɓen 2023.

Mawaƙan wajen su 35, sun gudanar da wani taro, inda suka bayyana damuwarsu da kuma sanar da cewa sun janye daga duk wata hulɗa da gwamnatin jihar, har sai an ba su kulawar da ta dace.

Hajji: Gwamnan Gombe ya yi bankwana da maniyyata 966, ya bai wa kowa kyautar Riyal 200 NAJERIYA A YAU: Mece ce Makomar Dimokuraɗiyya Idan Aka Wajabta Kada Kuri’a?

Shugaban mawaƙan jihar, Lawan Gujungu Mai Babban Gandu ne, ya jagoranci taron, inda ya shaida wa manema labarai cewa tun bayan da sabon gwamnan ya hau mulki sama shekara biyu, har yanzu ba su sharɓi romon dimokuraɗiyya ba.

Ya ce mawaƙan sun yi haƙuri na tsawon lokaci suna sa ran za a saka musu, amma abin ya gagara.

A cewarsa: “Mun shiga mawuyacin hali. Muna cikin APC tun asali, mun yi wa jam’iyya hidima sosai a lokacin yaƙin neman zaɓe, mun ƙirƙiri waƙoƙi da dama don tallata manufofin jam’iyyar da kwatanta cancantar ’yan takararta.

“Amma yanzu da muka ci zaɓe kuma muka kafa gwamnati, an watsar da mu tamkar ba mu da wata ƙima.”

Lawan, ya ƙara da cewa daga yanzu mawaƙan za su nisanci duk wani taro ko aikin da ya shafi gwamnati, har sai an saurare su tare da mutunta su da irin gudunmawar da suka bayar.

Wannan bore ya fito fili ne a daidai lokacin da ake buƙatar jituwa da haɗin kai tsakanin masu ruwa da tsaki a cikin jam’iyyar da kuma gwamnatin jihar domin ci gaban al’umma.

Wasu daga cikin mawaƙan da suka halarci taron sun bayyana cewa suna fatan gwamnan zai ji ƙorafinsu kuma ya ɗauki matakin da ya dace, domin ci gaba da gina jam’iyya da gwamnatin da kowa ke alfahari da ita.

Tuni dai wannan batu ya jawo ce-ce-ku-ce a cikin jam’iyyar APC a Jihar Jigawa, inda wasu ke ganin cewa ya kamata gwamnati ta sake duba rawar da waɗanda suka ba da gudunmawa kafin kafa gwamnati, domin gudun fuskantar tawaye.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sojoji da ’yan siyasa na taimaka wa Boko Haram da bayanai — Zulum
  • Zulum zai saya wa sojoji da ’yan sa-kai ƙarin motoci don yaƙar Boko Haram
  • Kwara Ta Kafa Tutar Hadin Kai Mai Mita 70 A Ilorin
  • Uwargidar Gwamnan Zamfara Ta Sake Jaddada Kudurin Dakile Tu’ammali Da Miyagun Kwayoyi A Jihar
  • Zulum ya roƙi Gwamnatin Tarayya ta kai wa Marte ɗauki
  • Mawaƙan APC sun zargi gwamnatin Jigawa da yin watsi da su
  • Mawaƙan APC sun zargi gwamnati da watsi da su a Jigawa
  • Gwamna Abdulrazaq Ya Jajanta Wa Wadanda Hatsarin Jirgin Ruwan Gbajibo Ya Rutsa Da Su
  • Boko Haram ta kashe manoma 90 a Borno cikin wata 5
  • Hajji: Gwamnatin Katsina ta biya wa maniyyata 2000 kuɗin hadaya