Aminiya:
2025-04-26@05:19:29 GMT

Za a mayar da tubabbun ’Yan Boko Haram cikin al’umma – Gwamna Buni

Published: 11th, April 2025 GMT

Gwamnatin Yobe ta bayyana shirinta na mayar da tubabbun mayaƙan Boko Haram cikin al’ummarsu da aka yi wa shirin kawar da tsattsauran ra’ayi, gyara da sake haɗewa da iyalansu ƙarƙashin rundunar Operation Safe Corridor (OPSC).

Gwamnan Jihar Yobe, Mai Mala Buni ne ya bayyana haka a ranar Alhamis a Damaturu lokacin da ya karɓi baƙuncin tawagar rundunar OPSC ƙarƙashin jagorancin babban hafsan tsaron Nijeriya Janar Christopher Musa.

Hisbah ta warware rigingimu 565 da lalata katan 51 na barasa a Yobe Trust Radio 92.7FM za ta fara shirye-shiryen gwaji

Gwamna Buni, wanda ya samu wakilcin mataimakinsa, Alhaji Idi Gubana ya bayyana ziyarar a matsayin wata dama ta tuntuɓar juna da haɗin gwiwa tsakanin jami’an tsaro da gwamnatin jihar.

Ya koka da yadda rikicin da aka kwashe sama da shekaru 15 ana yi ya laƙume rayukan dubban mutane a Yobe, da lalata dukiyoyin jama’a da na masu zaman kansu tare da raba magidanta da dama da garuruwansu na asali.

Gwamnan ya ce gwamnatin jihar ta gane cewa, ba dukkan ’yan ƙungiyar ta’addancin ne ke shiga cikin kisan kai ba, yana mai cewa tsarin kishin ƙasa ya ba da damar ceto da kuma mayar da waɗanda suka nuna nadama ya zuwa ga al’ummominsu.

“Mun yi imanin cewa, an tura wasu mutane shiga cikin ’yan ta’adda ta hanyar ƙarfi ko koyarwar aƙida.”

“Tare da ci gaba da ƙoƙarinsu, za su iya tuba, gyarawa da komawa rayuwa ta yau da kullun a matsayin ‘yan ƙasa da ke da ‘yanci.” In ji Buni.

Gwamnan ya ce tubabbun ‘yan Boko Haram 390 da suka haɗa da ‘yan asalin Jihar Yobe 54 ne za su kammala karatu tsakanin ranakun 14 zuwa 19 ga Afrilu.

Ya ce, jihar ta samar da wasu tsare-tsare ta hanyar ma’aikatar Jinƙai da kula da bala’o’i domin tabbatar da sake dawo da su cikin al’umma yadda ya kamata.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Baoko Haram Gwamna Buni

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnatin Katsina Ta Sauya Masu Yi Wa Alhazai Hidima A Saudiyya

Gwamnan ya bayyana cewa ba za a yi amfani da kudin al’umma ba ga mutanen da ba za su iya kula da mahajjata yadda ya kamata ba.

 

Gwamna Radda ya kara da cewa ya yi taro da shugabannin kananan hukumomi guda 34 domin tabbatar da cewa malaman da suka cancanta ne kadai aka zaba a matsayin masu koyarwa a ayyukan aikin hajjin bana.

 

Ya kuma yi alkawarin kafa kwamitin yada labarai domin yada ayyukan aikin hajjin tare da ba da kulawa ta musaman kan shawarwarin da aka bayar kan rahoton da kwamitin aiki hajjin ya gabatar.

 

Da yake gabatar da rahoton, tsohon mataimakin gwamnan Jihar Katsina kuma Amirul Hajj, Alhaji Tukur, ya bayyana wasu muhimman batutuwa da ke bukatar kulawa.

 

Ya kuma bayyana bukatar tallafa wa hukumar kula jin dadin alhazai wurin tantance malamai. Yana mai cewa mafi yawancin shugabannin kananan hukumomi sun sanya malaman da ba su da kwarewar yadda za su koyar da mahajjatan.

 

Amirul Hajja ya nuna damuwarsa bisa yadda ake samu wadanda ba ‘yan Nijeriya ba a cikin mahajjatan jihar tare da ba da shawarar inganta hanyoyin da ake bi wurin tantance mahajjatan.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnatin Katsina Ta Sauya Masu Yi Wa Alhazai Hidima A Saudiyya
  • Gwamnan Kano ya kafa sabbin hukumomi 4
  • Zulum Ya Taya MNJTF Da Gwamnatin Alihini Bayan Harin Boko Haram A Wulgo
  • Yobe na ɗaya daga cikin jihohin Najeriya mafi zaman lafiya – Buni
  • An fara raba wa almajirai tabarma da gidan sauro a Yobe
  • Tallafa Wa Al’umma: Ya Dace Gwamnoni Su Yi Koyi Da Jihar Zamfara – UNDP
  • 2025: NAHCON Ta Ware Kujerun Aikin Hajji 1,407 Ga Jihar Taraba
  • An Bayyana Filin Jirgin Sama Minna a Matsayin Mafita Ga Jiragen da ke sauka Abuja
  • Ya isa haka: Tinubu ya umarci shugabannin tsaro su kawo ƙarshen kashe-kashe
  • Gwamna da jiga-jigan siyasa a Delta sun fice daga PDP zuwa APC