Aminiya:
2025-12-03@05:00:37 GMT

’Yan kasuwa da dama sun mutu bayan kifewar kwalekwale a Kogin Neja

Published: 11th, April 2025 GMT

Ana fargabar matafiya da dama sun rasu bayan kifewar wani  kwalekwale ɗauke da ’yan kasuwa a yankin Kogin Neja.

Hatsarin kwalekwalen ya auku ne ƙauyen Sokun da ke yankin Ƙaramar Hukumar Lapai, a sakamakon iska mai ƙarfi da ta haddasa juyawar igiyar ruwan.

Shaidu sun ce hatsarin ya auku ne a yayin da kwalekwalen ke ɗauke da fasinjoji da kuma buhunan shinkafa kimanin 200 daga ƙauyen Bugge na Jihar Kogi a zuwa ƙauyen Sokun na Jihar Neja a ranar Laraba da dare.

Wani mazaunin yankin, Baba Alhassan, ya shaida wa wakilinmu cewa, ba a kai ga tantance ainihin yawan fasinjojin da ke cikin kwalwkwalen a lokacin da lamarin ya faru ba, amma an yi asarar duk buhunan shinkafar a hastarin.

NAJERIYA A YAU: Yadda Faɗuwar Farashin Ɗanyen Mai Zai Shafi Rayuwar ’Yan Najeriya

Ya bayyana cewa daga cikin mamatan har da wani mai sana’ar POS da ƙaninsa ’yan asalin ƙauyen Alaba da ke Ƙaramar Hukumar Lapai

Daraktan Hukumar ba da Agajin Gaggawa na Jihar Neja (NSEMA), Abdullahi Baba Arah, ya tabbatar da aukuwar lamarin, yana mai cewa ana ci gaba da aikin ceto da ƙoƙarin gano ainihin musabbabin hatsarin da kuma irin asarar da ta haifar.

Mazauna yankin sun bayyana cewa, “Sufurin ruwa shi ne kaɗai hanyar da ta rage da muke amfani da ita domin kai kayanmu kasuwanni saboda hanyar ta yi mummunan lalacewa.”

Wata ’yar kasuwa a yankin mai suna Fatima Muhammad, ta bayyana cewa, saboda nisan tafiyar, fasinjoji sukan yi tafiyar dare domin su isa kasuwa washegari da safe.

Fatima ta ce, “Babban ƙalubalen da muke fuskanta shi ne sufuri. Da kwalekwale muka dogara wajen kai kayanmu kasuwa. Wani lokaci kwalekwalen na ɗaukar lodi fiye da kima. Sai ka ga kwalekwale mai ƙarfin ɗaukar mutane 100 ya kwashi sama da haka. Amma ban ga laifin fasinjojin ba, musamman masu son su isa da wuri.”

Jama’ar yankin sun yi kira ga Gwamnatin Jihar Neja da ta Tarayya da su samar da wadatattun rigunan kariya da jiragen ruwa na zamani sannan su aiwatar da tsauraran hukunci kan masu karya doka.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: kasuwa kwalekwale Matafiya

এছাড়াও পড়ুন:

Mutum 6 sun jikkata a rikici manoma da makiyaya a Jigawa

Aƙalla mutum shida ne suka jikkata bayan da wani rikici ya ɓarke tsakanin manoma da makiyaya a ƙauyen Kangire da ke Ƙaramar Hukumar Birnin Kudu a Jihar Jigawa.

Ishak Ibrahim Fanini, mai taimaka wa shugaban Ƙaramar Hukumar Birnin Kudu, Muhammad Uba, ya tabbatar da faruwar lamarin a wani saƙo da ya wallafa a shafinsa na Facebook.

Sojoji sun ceto mutum 7 da ’yan bindiga suka sace a Kano DSS ta gayyaci Datti Baba-Ahmed kan zargin kalaman tayar da hankali

A cewarsa, an zargi makiyaya da shigar da dabbobinsu cikin gonakinsu wasu manoma.

Wannan ya haddasa faɗa tsakanin manoma da makiyayan.

Ya ƙara da cewa shugaban Ƙaramar Hukumar ya gudanar da taron sulhu tsakanin ɓangarorin biyu, inda ya gargaɗi su kan tayar da rikici a yankin.

Wannan sabon rikici ya faru makonni kaɗan bayan irin wannan ya auku a watan Oktoba, inda mutane uku suka mutu sakamakon rikicin manoma da makiyaya a Ƙaramar Hukumar Birniwa.

Rikicin manoma da makiyaya ya zama babban matsala a Jigawa da sauran yankunan Arewa.

Masana sun ce wannan rikici na yawan faruwa ne saboda matsalolin muhalli, tsadar rayuwa.

Sun bayyana cewa sauyin yanayi da yaɗuwar hamada a Arewacin Sahel sun tilasta wa makiyaya da dama yin ƙaura don ciyar da dabbobnsu.

Sai dai shigarsu yankunan da ake noma a Jigawa, ya haifar da rikici saboda lalata gonaki.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Mutane 9,854 na ɗauke da cutar AIDS a Yobe 
  • Wani Dan Adawa Da Gwamnatin Paul Biya Ya Mutu A Gidan Yari A Kasar Kamaru
  • ’Yan sanda sun gano zinaren N23m bayan shekara 13 da ɓacewarsu a Borno
  • ’Yan sanda sun gano zinaren N23m bayan shekara 12 da ɓacewarsu a Borno
  • Gwamnatin Kano Ta Kara Jaddada Dokar Haramcin Yin Haya da Babur a Jihar
  • Nijar : zamu sayar da uranium dinmu ga wanda muka ga dama_ Janar Tiani
  • Jihar Jigawa Ta Mayar da Rarar Kudi Sama da Naira Miliyan 50 Ga Maniyyatan Aikin Hajjin 2026
  • Sojoji sun ceto ’yan mata 12 da ISWAP suka sace a Borno
  • Mutum 6 sun jikkata a rikici manoma da makiyaya a Jigawa
  • ’Yan bindiga sun kashe tsohuwa, sun sace mutum 3 a Kano