Gwamnati ta gargaɗi jihohi 30 kan ambaliyar ruwa
Published: 11th, April 2025 GMT
Gwamnatin tarayyar Nijeriya ta yi hasashen za a yi ruwan sama mai ƙarfi da ambaliya a jihohi 30 da kuma babban birnin tarayya Abuja.
Jihohin da ake fargabar fama da ambaliyar ruwan sun haɗa da: Abia, Adamawa, Akwa Ibom, Anambra, Bauchi, Bayelsa, Benue, Borno, Cross-Riɓer, Delta, Ebonyi, Edo, Gombe, Imo, Jigawa, Kebbi, Kogi, Kwara, Lagos, Nasarawa, Niger, Ogun, Ondo, Osun, Oyo, Riɓers, Sokoto, Taraba, Yobe, Zamfara da kuma babban birnin tarayya.
Ministan albarkatun ruwa da tsaftar mahalli, Joseph Utsev, a ranar Alhamis, ya ce za a fuskanci ambaliyar ruwa a gaɓar teku da koguna a wasu sassan yankunan Kudu maso Kudu na ƙasar, sakamakon ƙaruwar ruwan teku.
Daga cikin waɗannan jahohin akwai: Bayelsa, Cross Riɓer, Delta, da Ribas yayin da Akwa-Ibom da Edo suka faza cikin jihohin da ake fargabar yin ambaliyar.
Utseɓ ya bayyana hakan ne a yayin da yake gabatar da taron shekara na 2025 (AFO) na hasashen ambaliyar ruwa da Hukumar Kula da Ruwa ta Nijeriya (NIHSA) ta gudanar a Abuja.
A taron na 2025 na Shekara-shekara kan Ambaliyar Ruwa (AFO) an raba su zuwa sassa uku don magance ƙalubalen iftila’in ambaliya da ba da bayanai don rage faruwar hakan, musamman a cikin unguwannin jama’a masu rauni.
Ministan ya bayyana cewa ambaliyar ruwa ta kasance ɗaya daga cikin ibtila’o’in da suka fi yin ɓarna a Nijeriya tare da sauyin yanayi da ke ƙara ƙaimi da tsanani.
Ya bayyana cewa unguwanni 1,249 a ƙananan hukumomi 176 a faɗin jihohi 30 da kuma babban birnin tarayya Abuja sun faɗa cikin yankunan da ake fama da ambaliyar ruwa a wannan shekarar, yayin da ƙarin unguwanni 2,187 a ƙananan hukumomi 293 ke fuskantar haɗarin ambaliya. Muhimman wuraren da ke da haɗarin sun haɗa da Abia, Benue, Lagos, Bayelsa, Riɓers, Jigawa, da dai sauransu.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Adamawa Akwa Ibom Anambra Bayelsa Jigawa Kwara Nasarawa Taraba Zamfara ambaliyar ruwa
এছাড়াও পড়ুন:
An kama mutum shida yayin da ‘yan sanda suka kubutar da mutane uku da aka yi garkuwa da su a Bauchi.
Rundunar ‘yan sandan jihar Bauchi ta kama wasu mutane shida da ake zargin masu garkuwa da mutane ne da ke gudanar da ayyukansu a karamar hukumar Toro ta jihar tare da ceto wasu mutane uku da aka sace ba tare da komi ba.
Jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan (PPRO), CSP Mohammed Ahmed Wakil, ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya raba wa manema labarai a Bauchi.
A cewar sanarwar, rundunar ‘yan sandan ta samu kiran gaggawa daga wani dan banga da ke kauyen Euga da misalin karfe 12:01 na safiyar ranar 29 ga watan Satumba, 2025, inda ya bayyana cewa wasu ‘yan bindiga da ba a san ko su wanene ba sun yi awon gaba da wasu mutane uku wato Idi Umar, Idi Lawan, da Musa Lawal.
Wakil ya ce “A martanin da aka mayar, an kaddamar da wani aiki na hadin gwiwa wanda ya hada da rundunar ‘yan sanda ta Toro, Toro Division, Nabordo Division, da kuma jami’an tsaro na cikin gida.”
Ya kara da cewa rundunar hadin guiwa ta bin diddigin wadanda ake zargin har zuwa wajen kauyen, inda suka gudanar da wani samame na dabara wanda ya kai ga ceto wadanda lamarin ya rutsa da su tare da kama wasu mutane shida da ake zargi.
Wadanda aka kama sun hada da Abubakar Usman, Adamu Alo, Abubakar Aliyu, Umar Habu, Abubakar Mamman Abubakar, da Shehu Sambo.
Karshen/Alhassan.