Aminiya:
2025-06-30@21:53:49 GMT

Gwamnati ta gargaɗi jihohi 30 kan ambaliyar ruwa

Published: 11th, April 2025 GMT

Gwamnatin tarayyar Nijeriya ta yi hasashen za a yi ruwan sama mai ƙarfi da ambaliya a jihohi 30 da kuma babban birnin tarayya Abuja.

Jihohin da ake fargabar fama da ambaliyar ruwan sun haɗa da: Abia, Adamawa, Akwa Ibom, Anambra, Bauchi, Bayelsa, Benue, Borno, Cross-Riɓer, Delta, Ebonyi, Edo, Gombe, Imo, Jigawa, Kebbi, Kogi, Kwara, Lagos, Nasarawa, Niger, Ogun, Ondo, Osun, Oyo, Riɓers, Sokoto, Taraba, Yobe, Zamfara da kuma babban birnin tarayya.

An kama masu garkuwa da mutane biyu a Yobe Ruwan sama ya lalata gidaje da yawa a Kebbi

Ministan albarkatun ruwa da tsaftar mahalli, Joseph Utsev, a ranar Alhamis, ya ce za a fuskanci ambaliyar ruwa a gaɓar teku da koguna a wasu sassan yankunan Kudu maso Kudu na ƙasar, sakamakon ƙaruwar ruwan teku.

Daga cikin waɗannan jahohin akwai: Bayelsa, Cross Riɓer, Delta, da Ribas yayin da Akwa-Ibom da Edo suka faza cikin jihohin da ake fargabar yin ambaliyar.

Utseɓ ya bayyana hakan ne a yayin da yake gabatar da taron shekara na 2025 (AFO) na hasashen ambaliyar ruwa da Hukumar Kula da Ruwa ta Nijeriya (NIHSA) ta gudanar a Abuja.

A taron na 2025 na Shekara-shekara kan Ambaliyar Ruwa (AFO) an raba su zuwa sassa uku don magance ƙalubalen iftila’in ambaliya da ba da bayanai don rage faruwar hakan, musamman a cikin unguwannin jama’a masu rauni.

Ministan ya bayyana cewa ambaliyar ruwa ta kasance ɗaya daga cikin ibtila’o’in da suka fi yin ɓarna a Nijeriya tare da sauyin yanayi da ke ƙara ƙaimi da tsanani.

Ya bayyana cewa unguwanni 1,249 a ƙananan hukumomi 176  a faɗin jihohi 30 da kuma babban birnin tarayya Abuja sun faɗa cikin yankunan da ake fama da ambaliyar ruwa a wannan shekarar, yayin da ƙarin unguwanni 2,187 a ƙananan hukumomi 293 ke fuskantar haɗarin ambaliya. Muhimman wuraren da ke da haɗarin sun haɗa da Abia, Benue, Lagos, Bayelsa, Riɓers, Jigawa, da dai sauransu.

 

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Adamawa Akwa Ibom Anambra Bayelsa Jigawa Kwara Nasarawa Taraba Zamfara ambaliyar ruwa

এছাড়াও পড়ুন:

Adadin Mambobin JKS Na Karuwa Yayin Da Rassanta A Matakin Farko Ke Karuwa

Adadin mambobin JKS na ci gaba da karuwa, inda rassanta ke ci gaba da ingantuwa. Baya ga haka, sassanta a matakin farko na kara karfi.

Wannan na kunshe ne cikin rahoton kididdiga da sashen shirye-shirye na kwamitin kolin jam’iyyar ya fitar yau Litinin, gabanin bikin cika shekaru 104 da kafuwar jam’iyyar.

Zuwa karshen 2024, jam’iyyar na da mambobi sama da miliyan 100.27, karuwar kusan miliyan 1.09 kan na shekarar 2023.

Zuwa karshen 2024 kuma, JKS na da sassa miliyan 5.25 a matakin farko, karuwar 74,000 idan aka kwatanta da shekarar 2023. (Mai fassara: Fa’iza Mustapha)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Miƙa Saƙon Ta’aziyyar Shugaba Tinubu A Gidan Ɗantata Na Madina
  • Sin Ta Kammala Aikin Agajin Gaggawa A Yankin Da Ambaliyar Ruwa Ta Afku
  • Adadin Mambobin JKS Na Karuwa Yayin Da Rassanta A Matakin Farko Ke Karuwa
  • Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Isa Saudiyya Don Halartar Jana’izar Ɗantata
  • Iran Ta Bawo Mayakan Huthi Fasahar Kera Makamai Masu Linzami Daga Cikin Ruwa
  • Sojoji Sun Kashe Shugaban Ƴan Ta’adda Mai Dada
  • Sharrin Ƴan Adawa Ne, Gwamnati Ta Ƙaryata Labarin Cire SGF Akume 
  • Mutanen Sakkwato na neman ɗaukin gwamnati game da Bello Turji
  • Gyaran Tsarin Mulki: Majalisa Ta Shirya Sauraron Jin Ra’ayoyin Jama’a A Wasu Sassan Nijeriya
  • Za a birne Aminu Ɗantata a Madina – Iyalansa