Aminiya:
2025-06-23@20:16:41 GMT

Akwai ƙasashen da ke shirin bai wa Iran makaman nukiliya — Rasha

Published: 23rd, June 2025 GMT

Wani babban jami’in Rasha, Dmitry Medvedev ya yi iƙirarin cewa akwai wasu ƙasashe da ke shirin bai wa Iran makaman nukiliya domin kare kanta daga abokan gaba.

A ranar Lahadi, Dmitry Medvedev wanda tsohon Firaministan Rasha ya yi iƙirarin cewa wasu ƙasashe sun shirya domin bai wa Iran makaman nukiliya kai-tsaye bayan hare-haren Amurka kan tashoshin nukiliyarta.

Matashi ya yi wa maraya ɗan shekara 10 kisan gilla a Zariya Amurka ta roƙi China ta sa baki kada Iran ta rufe mashigar tekun Hormuz

“Wasu ƙasashe sun shirya domin bai wa Iran makaman nukiliyarsu kai-tsaye,” kamar yadda Medvedev, Mataimakin Majalisar Tsaron Rasha, ya bayyana a wasu jerin saƙonni da ya wallafa a  shafin X.

Medvedev ya ce da alama wuraren da aka kai wa hare-haren ba su lalace sosai ba, yana mai ƙarawa da cewa inganta makamashin Yuraniyum da kuma samar da makaman nukiliya ka iya ci gaba.

Ya yi gargaɗin cewa Amurka ta sake “shiga” wani babban rikici, a wannan karon “da alamar [za ta yi] wani aiki [hari] na ƙasa,” kuma ya ce shugabannin Iran sun ƙara ƙarfi sakamakon hare-haren.

“Mutane suna mara wa shugabancin addinin baya, har ma da waɗanda ba sa sonta [a da],” in ji shi.

Ya soki Shugaban Amurka Donald Trump kan sake ƙaddamar da wani yaƙi duk da cewa ya yi yaƙin neman zaɓe ne a matsayin wanda zai “samar da zaman lafiya,” inda ya yi watsi da yiwuwar shugaban na Amurka ya samu lambar yabon Nobel ta zaman lafiya.

Medvedev ya kuma yi iƙirarin cewa “yawancin ƙasashe” suna adawa da matakan Amurka da Isra’ila.

Ana iya tuna cewa a cikin daren ranar Asabar da ta gabata ce Trump ya ce jiragen yaƙin Amurka sun jefa bama-bamai kan cibiyoyin nukiliyar Iran guda uku, lamarin da ya ƙara girman yaƙin da ke gudana tsakanin Isra’ila da Iran.

Tuni wasu manyan hafsoshin sojan Iran sun yi barazanar mayar wa Amurka da martani mai tsanani kan hare-haren da ta kai.

Kafofin yaɗa labaran Iran sun saki wani bidiyo da ke nuna babban kwamandan sojojin ƙasar, Amir Hatami, yana magana da wasu manyan hafsoshi a cikin wani dakin tsare-tsare.

A cikin bidiyon, Hatami ya ce duk lokacin da Amurka ta aikata “laifuka” kan Iran a baya, sai ta samu martani mai tsanani, kuma wannan karon ma hakan zai faru.

A wani ɓangare kuma, babban hafsan hafsoshin sojan Iran, Abdolrahim Mousavi, ya fitar da wata sanarwa inda ya ce Amurka ta buɗe ƙofar daukar “kowanne irin mataki” kan dakarun ta. Ya ƙara da cewa Iran “ba za ta taɓa ja da baya ba.”

Kazalika, Ministan Harkokin Wajen Iran ya kai ziyara Rasha tare da rakiyar wasu jami’an gwamnatin ƙasarsa, inda ya je domin ganawa ta musamman da Shugaban Ƙasar Vladimir Putin.

Abbas Araghchi ya yaba wa shugaban na Rasha, wanda ya ce tarihi ba zai manta da shi ba bisa jajircewar da ya nuna wajen fitowa fili ya yi Allah-wadai da harin Amurka a cibiyar nukiliyar Iran.

Ministan ya zargi Amurka da yi wa dokokin duniya da yarjejeniyar makamin nukiliya ta Non-Proliferation Treaty (NPT) karan tsaye ta hanyar ɗaukar matakin kai harin.

Dmitry Medvedev tare da Shugaba Vladimir Putin

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Dmitry Medvedev Iran Rasha bai wa Iran makaman nukiliya

এছাড়াও পড়ুন:

An sallami ƙarin ma’aikata 639 a tashar Muryar Amurka

Hukumar da ke kula da kafar yaɗa labarai ta Muryar Amurka (VOA) ta sallami ƙarin ’yan jarida da sauran ma’aikata 639 a ranar Juma’a.

Hukumar Kula da Harkokin Watsa Labarai ta Duniya ta Amurka (USAGM) ta bayyana cewa kawo yanzu an sallami ma’aikata 1,400 a wani bangare na shirin Shugaban Amurka Donald Trump na rage ma’aikata a hukumar zuwa mafi ƙarancin adadi kamar yadda doka ta tanada.

Hakan na nufin an kori mutum takwas a cikin kowane ma’aikata 10 da ke VOA a wata uku da suka gabata, a sakamakon wannan matakin Hukumar USAGM ta ɗauka.

Babbar Mashawarciya ga Hukumar, Kari Lake, ta bayyana cewa, “An aika wa ma’aikata 639 a VOA da USAGM da takardun kora a matsayin wani ɓangare na ƙoƙarin da ya kamata a yi tun da daɗewa don kawar da dimbin ma’aikata cima-zaune da kuma rashin riƙon amana a hukumar,” in ji sanarwar da ta fitar.

Yadda Iran ta lalata cibiyar kimiyya mafi muhimmanci a Isra’ila 2027: Manyan ’Yan adawa na neman rajistar sabuwar jam’iyya

Lake ta kuma tabbatar da cewa hukumar ta kasance “cike da jami’an da ba sa aiki komai, nuna son kai, da ɓarnatar da dukiya.”

Ta bayyana cewa wannan mataki na nufin USAGM yanzu tana aiki kusa da mafi ƙarancin ma’aikata 81 da doka ta tanada.

Ma’aikata 250 kuma za su ci gaba da zama a Ofishin Watsa Labarai na Cuba (OCB), wanda ke watsa labarai zuwa ƙasar Cuba mai mulkin kwaminisanci.

An lura cewa babu ko ɗaya daga cikin ma’aikata 33 na OCB da aka kora.

Wannan mataki mai yiwuwa alama ce ta kusan kawo ƙarshen wannan shahararren gidan rediyo VOA wanda miliyoyin mutane ke saurara tsawon shekara 50 a faɗin duniya.

VOA, wadda aka kafa a 1942 don yaƙar farfagandar Nazi, tana watsa shirye-shirye a kusan harsuna 50 kuma ta mutane miliyan 360 ke sauraron shirye-shiryenta a mako, a faɗin duniya.

A watan Mayu aka kori ma’aikatan kwangila kusan 600 na VOA.

Wasu ’yan jam’iyyar Republican a baya sun zargi tashar da sauran kafofin yaɗa labarai masu samun tallafin gwamnati da nuna son kai ga masu ra’ayin mazan jiya, suna masu kira da a rufe tashar a matsayin wani ɓangare na rage kashe kuɗin gwamnati.

Wata tashar USAGM, Radio Free Asia, wadda tuni aka rage ma’aikatanta sosai, ta sanar a cikin wani sakon imel ga ma’aikata a ranar Juma’a cewa tana aiwatar da karin hutun tilas a sassa daban-daban.

Ana ci gaba da shari’o’i daban-daban kan lamarin korar ma’aikatan na USAGM.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Babu dalilin kai wa Iran farmaki — Putin
  • Koriya ta Arewa za ta taimaka wa Iran gyara tashoshin nukiliyan da Amurka ta kai hari —Masani
  • Fim Babbar Hanya Ce Ta Nishaɗantar Da Al’umma -D Malam Dan Bola (2)
  • Harin Amurka A Wurare 3 Na Nukiliyar Iran: Babu Wani Lahani A Harin Bama-baman – Iran
  • Za mu ci gaba da yi wa Isra’ila luguden wuta — Shugaban Iran
  • An sallami ƙarin ma’aikata 639 a tashar Muryar Amurka
  • Yadda Iran ta lalata cibiyar kimiyya mafi muhimmanci a Isra’ila
  • Iran ta lalata cibiyar kimiyya mafi muhimmanci a Isra’ila
  • Iran ta lalata cibiyar kimiyya mafi daraja a Isra’ila