Aminiya:
2025-09-24@14:18:45 GMT

Akwai ƙasashen da ke shirin bai wa Iran makaman nukiliya — Rasha

Published: 23rd, June 2025 GMT

Wani babban jami’in Rasha, Dmitry Medvedev ya yi iƙirarin cewa akwai wasu ƙasashe da ke shirin bai wa Iran makaman nukiliya domin kare kanta daga abokan gaba.

A ranar Lahadi, Dmitry Medvedev wanda tsohon Firaministan Rasha ya yi iƙirarin cewa wasu ƙasashe sun shirya domin bai wa Iran makaman nukiliya kai-tsaye bayan hare-haren Amurka kan tashoshin nukiliyarta.

Matashi ya yi wa maraya ɗan shekara 10 kisan gilla a Zariya Amurka ta roƙi China ta sa baki kada Iran ta rufe mashigar tekun Hormuz

“Wasu ƙasashe sun shirya domin bai wa Iran makaman nukiliyarsu kai-tsaye,” kamar yadda Medvedev, Mataimakin Majalisar Tsaron Rasha, ya bayyana a wasu jerin saƙonni da ya wallafa a  shafin X.

Medvedev ya ce da alama wuraren da aka kai wa hare-haren ba su lalace sosai ba, yana mai ƙarawa da cewa inganta makamashin Yuraniyum da kuma samar da makaman nukiliya ka iya ci gaba.

Ya yi gargaɗin cewa Amurka ta sake “shiga” wani babban rikici, a wannan karon “da alamar [za ta yi] wani aiki [hari] na ƙasa,” kuma ya ce shugabannin Iran sun ƙara ƙarfi sakamakon hare-haren.

“Mutane suna mara wa shugabancin addinin baya, har ma da waɗanda ba sa sonta [a da],” in ji shi.

Ya soki Shugaban Amurka Donald Trump kan sake ƙaddamar da wani yaƙi duk da cewa ya yi yaƙin neman zaɓe ne a matsayin wanda zai “samar da zaman lafiya,” inda ya yi watsi da yiwuwar shugaban na Amurka ya samu lambar yabon Nobel ta zaman lafiya.

Medvedev ya kuma yi iƙirarin cewa “yawancin ƙasashe” suna adawa da matakan Amurka da Isra’ila.

Ana iya tuna cewa a cikin daren ranar Asabar da ta gabata ce Trump ya ce jiragen yaƙin Amurka sun jefa bama-bamai kan cibiyoyin nukiliyar Iran guda uku, lamarin da ya ƙara girman yaƙin da ke gudana tsakanin Isra’ila da Iran.

Tuni wasu manyan hafsoshin sojan Iran sun yi barazanar mayar wa Amurka da martani mai tsanani kan hare-haren da ta kai.

Kafofin yaɗa labaran Iran sun saki wani bidiyo da ke nuna babban kwamandan sojojin ƙasar, Amir Hatami, yana magana da wasu manyan hafsoshi a cikin wani dakin tsare-tsare.

A cikin bidiyon, Hatami ya ce duk lokacin da Amurka ta aikata “laifuka” kan Iran a baya, sai ta samu martani mai tsanani, kuma wannan karon ma hakan zai faru.

A wani ɓangare kuma, babban hafsan hafsoshin sojan Iran, Abdolrahim Mousavi, ya fitar da wata sanarwa inda ya ce Amurka ta buɗe ƙofar daukar “kowanne irin mataki” kan dakarun ta. Ya ƙara da cewa Iran “ba za ta taɓa ja da baya ba.”

Kazalika, Ministan Harkokin Wajen Iran ya kai ziyara Rasha tare da rakiyar wasu jami’an gwamnatin ƙasarsa, inda ya je domin ganawa ta musamman da Shugaban Ƙasar Vladimir Putin.

Abbas Araghchi ya yaba wa shugaban na Rasha, wanda ya ce tarihi ba zai manta da shi ba bisa jajircewar da ya nuna wajen fitowa fili ya yi Allah-wadai da harin Amurka a cibiyar nukiliyar Iran.

Ministan ya zargi Amurka da yi wa dokokin duniya da yarjejeniyar makamin nukiliya ta Non-Proliferation Treaty (NPT) karan tsaye ta hanyar ɗaukar matakin kai harin.

Dmitry Medvedev tare da Shugaba Vladimir Putin

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Dmitry Medvedev Iran Rasha bai wa Iran makaman nukiliya

এছাড়াও পড়ুন:

Ya Kamata Sin Da Amurka Su Hau Turbar Hadin Gwiwa Da Samun Moriyar Juna A Sabon Lokaci

A daren ranar 19 ga wannan wata, shugaban kasar Sin Xi Jinping da takwaransa na kasar Amurka Donald Trump sun tattauna ta wayar tarho, inda shugaba Xi ya jaddada cewa, alakar Sin da Amurka na da matukar muhimmanci, Sin da Amurka na iya cimma nasarar bai daya da wadata tare, ta yadda za su amfani kawunansu, da ma sauran sassan duniya baki daya. A nasa bangare kuwa, shugaba Trump cewa ya yi, alakar Amurka da Sin ita ce mafi muhimmancin dangantaka a duniya, yana mai cewa, aiki tare tsakanin kasashen biyu ka iya haifar da manyan abubuwa da za su ingiza zaman lafiya da daidaito a duniya. Ya yi fatan wanzar da babbar dangantaka mai armashi ta dogon lokaci tsakanin kasarsa da Sin.

A cikin wannan tattaunawar, shugaba Xi ya bayyana ra’ayi da matsayin Sin kan batutuwan dake shafar dangantakar kasashen biyu, ya yi nuni da cewa, ya kamata Sin da Amurka su yi kokari da hadin gwiwa, kana kasar Amurka ta magance daukar matakan kayyade ciniki daga bangare daya, ta haka za a magance kawo illa ga nasarorin da kasashen biyu suka samu yayin shawarwarinsu a zagaye da dama. Game da batun TikTok, ana son ganin kamfanoni su tattauna bisa tushen ka’idojin kasuwanci, da cimma daidaito bisa dokokin kasar Sin da ka’idojin daidaiton samun moriya, ana fatan Amurka za ta samar da yanayin ciniki mai bude kofa da adalci da rashin nuna bambanci ga kamfanonin Sin da suka zuba jari a Amurka. Shugaba Trump ya bayyana cewa, Amurka tana fatan za a ingiza hadin gwiwar tattalin arziki da cinikayya a tsakanin kasashen biyu, kuma zai nuna goyon baya ga tawagogin kasashen biyu da su yi shawarwari don daidaita batun TikTok yadda ya kamata.

Akwai sharhin da aka yi game da cewa, tattaunawar dake tsakanin shugabannin kasashen biyu ta shaida cewa, Sin da Amurka sun samu muhimmin ci gaba kan cimma yarjejeniyar daidaita batun TikTok. Direktan ofishin nazarin siyasar kasa da kasa na kungiyar masana masu nazarin manufofin duniya na kwalejin ilmin zamantakewar al’ummar kasar Sin Zhao Hai ya yi fatan cewa, idan Sin da Amurka suka iya daidaita batun TikTok, to za a samar da sharadi ga kamfanonin kasashen biyu a kan yadda za su yi harkokin kasuwanci a kasuwar kasashen biyu, inda ta hakan za a sa kaimi ga Sin da Amurka wajen ganin sun daidaita sauran batutuwan tattalin arziki da cinikayya baki daya. (Zainab Zhang)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Larijani: Iran Tana Nazarin Shawarwarin Turai Da Na Rasha Domin Kare Muradunta
  • Groosi: Masu Binciken Hukumar Kula Da Makamashin Nukiliya Suna Hanyar Zuwa Iran
  • Burkina Faso, Mali da Nijar sun fice daga Kotun ICC
  • Iran Da Rasha Zasu Rattaba Hannun Kan Batun Gina Wasu Tashoshin Nukiliya.
  • CORET Ta Yaba Da Nasarar Shirin Ciyarda Daliban Makarantun Makiyaya
  • Iran ta la’anci harin da aka kai kan wani masallaci a Sudan
  • Pezeshkian: Kasashen Da Ba Su Cika Alkawura Da Suka Dauka Ba Suke Zargin Iran Kan Rashin Mutanta Yarjejeniyar Nukiliya
  • Dakarun IRGC: Iran Za Ta Tarwatsa Makiya Tare Da Mayar Da Martani Kan Duk Wani Zalunci
  • Lokaci Yayi Da Shugabannin Arewa Za Su Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Yankin –  ACI
  • Ya Kamata Sin Da Amurka Su Hau Turbar Hadin Gwiwa Da Samun Moriyar Juna A Sabon Lokaci