Leadership News Hausa:
2025-08-06@18:36:49 GMT

Matsalolin Rayuwa: Matasan Suleja Na Buƙatar Ƙarfafa Gwuiwa

Published: 22nd, June 2025 GMT

Matsalolin Rayuwa: Matasan Suleja Na Buƙatar Ƙarfafa Gwuiwa

A can ne na hadu da wani matashi mai hazaka da kwazo, Faisal Ibrahim Abdullahi, wanda ya shaida min cewa; ya je Jihar Legas ne domin koyon fasahar ‘Epody Resin’, wato kera kayan ado da kayan daki na zamani da ake yi da sinadaran resin. Har yanzu, shi ne kadai daga yankinmu da ya mallaki wannan fasaha.

Amma yana da burin koyar da sauran matasa muddin aka tallafa masa.

Na tsaya ina kallon kayan da ya nuna min na daki da ado, wanda na dauka cewa; ana yin su ne daga kasashen waje. Sai na ji cewa, “toh, dama a Suleja ake wannan?” Gaskiya wannan irin kwazo yana da bukatar tallafi, ba yabo kadai ba.

Bayan haka, taron ya kunshi gasa da horo a harkokin kasuwanci ta yanar gizo, inda matasa da dama suka samu kyaututtuka masu daraja daga ciki har da wata budurwa mai suna Blessing Paul da ta lashe kyautar mota da wasu da suka samu kyautar kudi.

Amma abin da ya dada daga min hankali shi ne, yadda galibin matasan da ke cin moriyar wannan dandali ba ’yan asalin Suleja ba ne. Wadanda suka fi mayar da hankali su ne daga wasu jihohi, suna rungumar dama da hannuwa biyu. Amma mu dai har yanzu muna ganin wadannan matasa kamar ‘yan damfara ne.

Wasu daga cikin masu rike da madafun iko ma sun yi watsi da gayyatarsu, idan ban da Mataimakin Shugaban karamar Hukumar Suleja da na Shiroro. Wasu daga cikin manyan sun yi wa su Coach Naseer mumunar fahimta, har suna yi musu kallon ‘Yahoo boys’ ne.

Ina ganin lokaci ya yi da za mu farka daga barci. Wadannan matasa suna kokari ne wajen gyara rayuwarsu ba tare da aikata laifi ba. Wajibi ne shugabanni da masu hannu da shuni da kuma masu zurfin tunani su rungumi irin wannan dandali, domin amfanin kowa da kowa.

Ga wasu daga cikin fa’idojin wannan dandalin talla na yanar gizo (affiliate marketing):

1- karfafa Matasa: Yana koya musu dogaro da kai da kuma dabarun kasuwanci.

2- Rage Aikata Laifuka: Matashin da ke da abin yi ba zai shiga yin shaye-shaye ko damfara ba.

3- Ci Gaban Al’umma: Nasarar mutum daya tana karfafa gwiwar wasu.

4- Samar Da Arziki: Wasu matasan da ke amfani da wannan dandali sun fara daukar ma’aikata, domin hannunsu ya fara maikon shuni.

5- Shiga Duniya: Matasanmu na iya fafatawa da sauran kasashen duniya daga cikin gida.

Don haka, ina kira ga Shuwagabannin Jihar Neja da na Suleja, ’yan kasuwa, manyan malamai da shugabannin gargajiya, da su bayar da goyon baya ga irin wannan yunkuri. Wannan dama ce ta fita daga kangin dogaro da gwamnati da kuma sauya tunanin cewa; dole sai an yi bariki ko kuma damfara kafin a samu kudi.

Haka zalika, kuna iya tallafa wa Faisal; domin ya koyar da matasa. Kuna kuma iya bayar da kayan aiki ko kudin horo. Amma mafi muhimmanci shi ne, ba su karfin gwiwa.

A nan ne, zan yi kira ga adali, manomin Gwamnan Jihar Neja; da ya bude wa wannan matashi kofar masana’antar Ladi Kwali, domin koyar da matasa wannan fasaha.

Yanzu duniya ta koma ta yanar gizo, wanda bai da fasahar zamani; kamar wanda bai iya karatu ba ne. Muna da zabi: mu goyi bayan irin su Coach Naseer da Faisal, ko kuma mu ci gaba da zargin su har su bar mu su tafi su samu nasara a inda ake mutunta fasaha irin tasu.

Daga Suleja nake kawo muku wannan labari mai dadi. Labarin harsashen nasara, ci gaba da inganci da ke kusa da mu, sai dai kash! Yawancinmu, ba ma ganin abin a haka.

Mu tashi tsaye. Mu goyi bayan kwazon matasanmu, kafin lokaci ya kure mana, ko wani ya zo ya amfana da su, mu kuma mu zauna muna ta faman korafi maras amfani.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Rayuwa

এছাড়াও পড়ুন:

Batun Ceto Wanda Ake Zargi Da Kwaya: Kwamishinan Kano Ya Yi Murabus

Kwamishinan Sufuri na Jihar Kano, Alhaji Ibrahim Ali Namadi, ya ajiye aikinsa bayan Gwamna Abba Kabir Yusuf ya karɓi rahoton kwamitin bincike da ke duba rawar da ya taka a batun ceto wani da ake zargi da safarar miyagun kwayoyi, Sulaiman Aminu Danwawu.

Wannan matakin na murabus ana kallonsa a matsayin wani muhimmin cigaba da ke nuna jajircewar gwamnatin jihar wajen kare gaskiya, bayyana ta da kuma ɗaukar nauyin ayyukanta a bainar jama’a.

A cikin wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Sunusi Bature Dawakin Tofa ya fitar, Kwamishinan ya bayyana cewa ya yanke shawarar murabus ne duba da muhimmancin al’amuran da suka shafi jama’a da kuma halin da ake ciki.

Ya ce: “A matsayina na ɗaya daga cikin masu fada-a-ji a wannan gwamnati da ke yaki da sha da fataucin miyagun kwayoyi, ya dace na ɗauki wannan mataki, koda kuwa zai sosa zukata.
“Ko da yake ina ci gaba da musanta hannuna a lamarin, ba zan iya watsi da irin yadda jama’a ke kallon batun ba, da kuma bukatar kare ƙimar gwamnati da muka ginata tare.” In ji shi.

Alhaji Namadi ya nuna godiya ta musamman ga Gwamna Abba Kabir Yusuf saboda ba shi damar yi wa jiharsa hidima, tare da jaddada aniyarsa ta ci gaba da bin manufofin gwamnatin.

Ya ƙara da cewa: “A matsayina na ɗan ƙasa nagari, dole ne in ci gaba da kare amana da hangen nesan da muka haɗa kai wajen shimfiɗawa a  jiharmu. Zan ci gaba da kasancewa mai biyayya ga akidun da suka kawo wannan gwamnati kan mulki.”

Gwamna Abba Kabir Yusuf ya karɓi murabus ɗin cikin farin ciki, tare da yi masa fatan alheri a duk wani yunƙurinsa na gaba.

Gwamnan ya sake jaddada kudirin gwamnatinsa wajen tabbatar da adalci, ladabi, da kuma yaki da miyagun dabi’u da laifukan da suka shafi kwayoyi da sauran matsalolin da ke shafan matasa da al’umma baki ɗaya.

Ya kuma ja hankalin duk masu rike da mukaman siyasa da su kasance masu hikima da taka-tsantsan wajen hulɗa da al’amuran jama’a, tare da neman izini daga hukumomi mafi girma kafin su shiga cikin wani lamari da ke da tasiri a bainar jama’a.

 

Abdullahi Jalaluddeen

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Batun Ceto Wanda Ake Zargi Da Kwaya: Kwamishinan Kano Ya Yi Murabus
  • DAGA LARABA: Me Ke Sa Matasa Zama Karnukan Farautar ‘Yan Siyasa A Kafafen Sadarwa Na Zamani?
  • Nafisa ta cancanci kyautar Dala 100,000 da gida da OON — Pantami
  • Ɗaliba ’yar shekara 15 daga Yobe ta lashe Gasar Muhawara ta Duniya
  • Nafisa ta cancaci kyautar Dala 100,000 da gida da OON —Pantami
  • Sanata Buba ya ƙaddamar da allurar rigakafin dabbobi kyauta
  • BUA Siminti Ya Ƙaddamar Da Shirin Horas Da Matasan Sakkwato
  • Wasu Kungiyoyi Sun Yi Kira Ga Dan Majalisa Aminu Sani Jaji Ya Fito Takarar Gwamnan Zamfara 
  • Gwamna Yusuf Ya Kaddamar da Shirin Dashe Itatuwa Don Yaki da Matsalolin Muhalli
  • Gwamnatin Jigawa Ta Dauki Manyan Matakan Kare Jihar Daga Ambaliyar Ruwa