Matsalolin Rayuwa: Matasan Suleja Na Buƙatar Ƙarfafa Gwuiwa
Published: 22nd, June 2025 GMT
A can ne na hadu da wani matashi mai hazaka da kwazo, Faisal Ibrahim Abdullahi, wanda ya shaida min cewa; ya je Jihar Legas ne domin koyon fasahar ‘Epody Resin’, wato kera kayan ado da kayan daki na zamani da ake yi da sinadaran resin. Har yanzu, shi ne kadai daga yankinmu da ya mallaki wannan fasaha.
Na tsaya ina kallon kayan da ya nuna min na daki da ado, wanda na dauka cewa; ana yin su ne daga kasashen waje. Sai na ji cewa, “toh, dama a Suleja ake wannan?” Gaskiya wannan irin kwazo yana da bukatar tallafi, ba yabo kadai ba.
Bayan haka, taron ya kunshi gasa da horo a harkokin kasuwanci ta yanar gizo, inda matasa da dama suka samu kyaututtuka masu daraja daga ciki har da wata budurwa mai suna Blessing Paul da ta lashe kyautar mota da wasu da suka samu kyautar kudi.
Amma abin da ya dada daga min hankali shi ne, yadda galibin matasan da ke cin moriyar wannan dandali ba ’yan asalin Suleja ba ne. Wadanda suka fi mayar da hankali su ne daga wasu jihohi, suna rungumar dama da hannuwa biyu. Amma mu dai har yanzu muna ganin wadannan matasa kamar ‘yan damfara ne.
Wasu daga cikin masu rike da madafun iko ma sun yi watsi da gayyatarsu, idan ban da Mataimakin Shugaban karamar Hukumar Suleja da na Shiroro. Wasu daga cikin manyan sun yi wa su Coach Naseer mumunar fahimta, har suna yi musu kallon ‘Yahoo boys’ ne.
Ina ganin lokaci ya yi da za mu farka daga barci. Wadannan matasa suna kokari ne wajen gyara rayuwarsu ba tare da aikata laifi ba. Wajibi ne shugabanni da masu hannu da shuni da kuma masu zurfin tunani su rungumi irin wannan dandali, domin amfanin kowa da kowa.
Ga wasu daga cikin fa’idojin wannan dandalin talla na yanar gizo (affiliate marketing):
1- karfafa Matasa: Yana koya musu dogaro da kai da kuma dabarun kasuwanci.
2- Rage Aikata Laifuka: Matashin da ke da abin yi ba zai shiga yin shaye-shaye ko damfara ba.
3- Ci Gaban Al’umma: Nasarar mutum daya tana karfafa gwiwar wasu.
4- Samar Da Arziki: Wasu matasan da ke amfani da wannan dandali sun fara daukar ma’aikata, domin hannunsu ya fara maikon shuni.
5- Shiga Duniya: Matasanmu na iya fafatawa da sauran kasashen duniya daga cikin gida.
Don haka, ina kira ga Shuwagabannin Jihar Neja da na Suleja, ’yan kasuwa, manyan malamai da shugabannin gargajiya, da su bayar da goyon baya ga irin wannan yunkuri. Wannan dama ce ta fita daga kangin dogaro da gwamnati da kuma sauya tunanin cewa; dole sai an yi bariki ko kuma damfara kafin a samu kudi.
Haka zalika, kuna iya tallafa wa Faisal; domin ya koyar da matasa. Kuna kuma iya bayar da kayan aiki ko kudin horo. Amma mafi muhimmanci shi ne, ba su karfin gwiwa.
A nan ne, zan yi kira ga adali, manomin Gwamnan Jihar Neja; da ya bude wa wannan matashi kofar masana’antar Ladi Kwali, domin koyar da matasa wannan fasaha.
Yanzu duniya ta koma ta yanar gizo, wanda bai da fasahar zamani; kamar wanda bai iya karatu ba ne. Muna da zabi: mu goyi bayan irin su Coach Naseer da Faisal, ko kuma mu ci gaba da zargin su har su bar mu su tafi su samu nasara a inda ake mutunta fasaha irin tasu.
Daga Suleja nake kawo muku wannan labari mai dadi. Labarin harsashen nasara, ci gaba da inganci da ke kusa da mu, sai dai kash! Yawancinmu, ba ma ganin abin a haka.
Mu tashi tsaye. Mu goyi bayan kwazon matasanmu, kafin lokaci ya kure mana, ko wani ya zo ya amfana da su, mu kuma mu zauna muna ta faman korafi maras amfani.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: Rayuwa
এছাড়াও পড়ুন:
Katolika ta horar da shugabannin al’umma da na addini kan zaman lafiya
Cibiyar Adalci, Ci gaba da Jinƙai ta mabiya ɗarikar Katolika (JDPC) reshen Kafanchan, tare da haɗin guiwar Majalisar Matan Katolika, ta shirya taron horaswa ga shugabannin addini da na gargajiya daga ƙananan hukumomin Jama’a da Zangon Kataf a Kudancin Jihar Kaduna.
Taron, wanda aka gudanar a garin Kafanchan a ƙarƙashin shirin Community Action for Peace and Socio-Economic Development (CAPSED), ya mayar da hankali ne kan zaman lafiya da kuma noma mai ɗorewa, musamman ma yadda ake amfani da takin gargajiya wajen noman citta.
Kotu ta daure mutumin da yake yada bidiyon tsiraici shekara 76 a kurkuku Kotu ta aike da dan TikTok din da ke wanka a kan titi a Kano gidan yariTaron wanda Hukumar Agajin Katolika ta Ƙasashen Waje (CAFOD) ta ɗauki nauyi na da nufin magance abubuwan da ke haifar da rikici da kuma inganta hanyoyin noma na zamani domin samar da zaman lafiya da ci gaba mai ɗorewa a yankin.
A cikin jawabinsa, Rabaran Dakta James Movel Wuye ya jaddada muhimmancin magance mummunan fahimta da ƙyashi tsakanin al’umma.
Ya ce, “Idan muka magance waɗannan matsalolin yadda ya kamata, za mu samu damar rage ƙiyayya da gaba tsakanin ƙabilu da addinai daban-daban a ƙasarmu.” Ya ja kunnen mahalarta game da faɗin kalaman ƙiyayya, yana mai cewa hakan na iya haifar da rikici da kuma cutar da lafiyar ƙwaƙwalwar wanda ake faɗawa hakan.
Da yake jawabi a ɓangaren noma, Dakta Barak Zebedee ya yi bayani ne kan amfani da hanyoyin fasaha wajen gudanar da noma na gargajiya musamman a ɓangaren noman citta. Ya bayyana cewa kakar noma ta shekarar 2023 ta zo da ƙalubale iri-iri na cututtukan citta inda ya shawarci manoma da su rungumi sababbin hanyoyin da ke da kariya daga cutar don samun ribar noma da ɗorewar amfanin gona.
Da yake nasa jawabin tunda farko, shugaban shirin CAPSED, Rabaran Fr. Onuh Ladi, ya bayyana cewa matakin farko na shirin ya samu gagarumin tasiri, musamman wajen ƙarfafa dangantaka tsakanin mabiya addinai a cikin al’umma.
Ya ce, wannan zagaye na biyu zai ƙara jaddada batun lafiyar ƙwaƙwalwa da kuma gabatar da sabbin dabarun sasanci ba tare da zuwa kotu ba.
Ya ce, “Manufarmu ita ce, mu ba shugabanni ƙarfin gwiwa da dabarun magance rigingimu cikin gaggawa kafin lamarin ya gagari kundila. A ɓangaren noma kuma, mun ƙarfafa sauya fasalin daga amfani da sinadarai zuwa ga taki na gargajiya, musamman a noman citta,” in ji Fr. Ono.
Ya kuma bayyana cewa, mahalarta za su ci gaba da yaɗawa da koyar da abin da suka koya a cikin al’ummominsu don saƙon ya game sauran manoman da ba su samu damar halartar bitar ba.
Wasu daga cikin mahalarta da suka tattauna da wakilinmu sun nuna godiya da farin ciki da horon da suka samu, inda suka ce ya faɗaɗa fahimtarsu game da koyarwar addinin Musulunci da na Kiristanci kan zaman lafiya da haƙuri. Haka kuma, sun ce zaman ya taimaka musu wajen warware wasu tunanin ba su da tushe a cikin sahihan koyarwar addinansu.