An yi ma’aikatan ƙananan hukumomin Gombe ƙarin albashin N5,000
Published: 21st, June 2025 GMT
Gwamnatin Jihar Gombe ta amince da biyan ƙarin albashin Naira 5,000 ga ma’aikatan ƙananan hukumomi da Hukumar Ilimi ta Ƙananan Hukumomi (LGEA).
Ƙarin albashin zai fara aiki ne daga albashin watan Yuni na shekarar 2025
Wata sanarwa da Jibrin Yusuf ya sanya wa hannu a madadin Shugaban Ma’aikatan Gwamnati, Ahmed Abdullahi, ta ce cimma matsayar ne a wani taro na musamman da aka gudanar a ranar Talata.
Taron ya samu halartar Shugaban Ma’aikata tare da wakilan ƙungiyoyin kwadago da wasu manyan jami’an gwamnati.
Najeriya ta tura sojoji domin samar da zaman lafiya a Gambia Ministan Harkokin Wajen Iran ya isa taron Kungiyar OIC a TurkiyyaTa ce an amince da ƙatin Naira 5,000 ga ma’aikatan har sai an kammala aikin tantancewa da ake gudanarwa a halin yanzu.
Shugaban Ma’aikata ya umarci Ma’aikatar Kuɗi daCi-gaban Tattalin Arziki da ta gaggauta ɗaukar matakan da suka dace don ganin an aiwatar da wannan karin cikin lokaci.
Duk da wannan ƙarin, binciken da wakilinmu ya gudanar ya gano cewa har yanzu ma’aikatan ƙananan hukumomi 11 na jihar ba su fara cin gajiyar ƙarin albashi da aka yi ba.
Mataimakin Gwamnan Jihar, Dokta Manassah Jatau, tare da shugabannin ƙungiyoyin ƙwadago (NLC) reshen jihar, Yusuf Bello, sun amince cewa idan kuɗaɗen shiga sun ƙaru, za a fara biyan mafi karancin albashi na Naira dubu 70,000 ga ma’aikata.
A yayin bikin Ranar Ma’aikata da aka gudanar kwanan nan, Yusuf Bello ya yi kira ga gwamnatin jihar da ta fara aiwatar da biyan mafi karancin albashi ga ma’aikatan kananan hukumomi cikin gaggawa.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Ƙananan Hukumomi Ƙarin Albashi
এছাড়াও পড়ুন:
Rahoto: An gudanar da tattaunawa mai tsawo tsakanin Syria da Isra’ila a Landan
Kafofin yada labaran Isra’ila sun rawaito cewa, an gudanar da wani dogon zaman tattaunawa a birnin London a yammacin jiya tsakanin ministan harkokin wajen Syria Asaad al-Sheibani da ministan kula da tsare-tsare na Isra’ila Ron Dermer, tare da halartar jakadan Amurka na musamman Tom Barak.
Kafofin yada labaran Isra’ila sun bayyana cewa ganawar ta dauki tsawon sa’o’i biyar, inda bangaren Syria ya gabatar da martaninsa kan shawarar da Isra’ila ta gabatar na cimma yarjejeniyar tsaro, inda ta ce an samu ci gaba a tattaunawar.
A baya dai bangarorin biyu sun gana a zagaye na biyu da aka sanar, ban da kuma tarukan sirri da suka gudanar a lokuta daban-daban wand aba a sanar ba, da nufin kulla alaka ta siyasa da tsaro a tsakaninsu.
Shugaban rikon kwarya a kasar Syria, Ahmad al-Sharaa (Joulani) ya bayyana cewa, “Tattaunawar tsaro da Isra’ila za ta iya haifar da sakamako a cikin kwanaki masu zuwa,” duba da cewa “yarjejeniyar tsaro da Isra’ila ta zama wajibi kuma dole ne a mutunta sararin samaniyar Siriya da kuma yankunanta.”
Tun da farko majiyoyin Syria da Isra’ila sun bayyana cewa, wakilin Amurka Tom Barrack ne ya jagoranci taron, wanda ya gana da bangarorin biyu fiye da sau daya a wani yunkuri daidaita alaka tsakanin Syria da Isra’ila.
Jaridar Haaretz ta Isra’ila ta bayar da rahoton da ke cewa, daya daga cikin muhimman abubuwan da aka tattauna a taron tsakanin Dermer-Sheibani shi ne hana kungiyar Hizbullah ko sojojin Iran ko kuma duk wata kungiya da ake ganin tana adawa da Isra’ila kasancewa a kudancin Siriya.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Sheikh Qassem: Harin Pager jarabawa ce wadda ta kara wa masu gwagwarmaya kwarin gwiwa September 18, 2025 Pezeshkian: Iran da Masar suna da tsohon tarihi a duniya September 18, 2025 Iran ta samu Zinariya, Azurfa, da Tagulla a Gasar Kokawa ta Duniya September 18, 2025 Iran Ta Yi Nasarar Gwajin Tauraron Dan’adam Da Zai Samar Da “Internet” Ga Yankunan Karkara September 17, 2025 Za A Kada Kuri’ar Raba Gardama Akan Sabon Tsarin Mulki A Kasar Guinea September 17, 2025 Larijani: Iran Da Saudiyya Za Su Bunkasa Aiki Tare A Fagagen Kasuwanci Da Tsaro September 17, 2025 Hukumar Tarayyar Turai Ta Gabatar Da Shawarar Jingine Aiki Da Yarjejeniyar Kasuwanci Da HKI September 17, 2025 Gaza: HKI Tana Ci Gaba Da Yi Wa Falasdinawa Kisan Kiyashi A Gaza September 17, 2025 Ma’aikatar Shari’ar Iran Ta Sanar Da Rataye Dan Leken Asirin Hukumar Mossad Ta Isra’ila September 17, 2025 Hamas Ta Zargi HKI Da Shirga Karya Don Kare Muggan Manufofinta September 17, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci