Aminiya:
2025-06-21@17:12:43 GMT

An yi ma’aikatan ƙananan hukumomin Gombe ƙarin albashin N5,000

Published: 21st, June 2025 GMT

Gwamnatin Jihar Gombe ta amince da biyan ƙarin albashin Naira 5,000 ga ma’aikatan ƙananan hukumomi da Hukumar Ilimi ta Ƙananan Hukumomi (LGEA).

Ƙarin albashin zai fara aiki ne daga albashin watan Yuni na shekarar 2025

Wata sanarwa da Jibrin Yusuf ya sanya wa hannu a madadin Shugaban Ma’aikatan Gwamnati, Ahmed Abdullahi, ta ce cimma matsayar ne a wani taro na musamman da aka gudanar a ranar Talata.

Taron ya samu halartar Shugaban Ma’aikata tare da wakilan ƙungiyoyin kwadago da wasu manyan jami’an gwamnati.

Najeriya ta tura sojoji domin samar da zaman lafiya a Gambia Ministan Harkokin Wajen Iran ya isa taron Kungiyar OIC a Turkiyya

Ta ce an amince da ƙatin Naira 5,000 ga ma’aikatan har sai an kammala aikin tantancewa da ake gudanarwa a halin yanzu.

Shugaban Ma’aikata ya umarci Ma’aikatar Kuɗi daCi-gaban Tattalin Arziki da ta gaggauta ɗaukar matakan da suka dace don ganin an aiwatar da wannan karin cikin lokaci.

Duk da wannan ƙarin, binciken da wakilinmu ya gudanar ya gano cewa har yanzu ma’aikatan ƙananan hukumomi 11 na jihar ba su fara cin gajiyar ƙarin albashi da aka yi ba.

Mataimakin Gwamnan Jihar, Dokta Manassah Jatau, tare da shugabannin ƙungiyoyin ƙwadago (NLC) reshen jihar, Yusuf Bello, sun amince cewa idan kuɗaɗen shiga sun ƙaru, za a fara biyan mafi karancin albashi na Naira dubu 70,000 ga ma’aikata.

A yayin bikin Ranar Ma’aikata da aka gudanar kwanan nan, Yusuf Bello ya yi kira ga gwamnatin jihar da ta fara aiwatar da biyan mafi karancin albashi ga ma’aikatan kananan hukumomi cikin gaggawa.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Ƙananan Hukumomi Ƙarin Albashi

এছাড়াও পড়ুন:

Bom ya kashe mutum 5 a Kano — ’Yan sanda

Ana fargabar mutum biyar sun mutu a sakamakon tashin bom a Jihar Kano a ranar Asabar.

Kwamishinan ’Yan Sandan Jihar Kano, Ibrahim Adamu Bakori, ba bayyana cewa bom ɗin soja ne ya tashi.

Kwamishinan ya ce akwai yiwuwar kuskure wurin safara ko kuma wurin kula da abin fashewan.

Ya bayyana haka ne a yayin ziyarar gani da ido da ya kai wurin da abin ta tashi.

 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Bom ya kashe mutum 5 a Kano — ’Yan sanda
  • Hajjin Bana: Jihohi 11 Sun Kashe Naira Biliyan 6.2 Kan Mahajjata
  • An sallami ƙarin ma’aikata 639 a tashar Muryar Amurka
  • Duk Da Jihohin Nijeriya Sun Fara Biyan Mafi Ƙarancin Albashi Na 70,000, Ana Ci Gaba Da Fuskantar Matsin Rayuwa
  • Ba Tsoro Ne Yasa Muka Amince Da Sulhu Da Ƴan Bindiga Ba – Gwamnatin Sokoto
  • Nico Williams Ya Amince Da Komawa Barcelona Akan Kwantiragin Shekaru 6
  • Tinubu na ƙaddamar da wasu ayyuka a Jihar Kaduna
  • Kotun Amurka ta daure ’yan Najeriya 5 shekaru 159 kan aikata damfara
  • Nijeriya za ta fara fitar ta tataccen mai zuwa Asia — Matatar Dangote