Yankin Taiwan Ya Yi Taron Bikin Bauta Na Kakan Gargajiyar Sin Fuxi
Published: 22nd, June 2025 GMT
Daruruwan mutane ne suka halarci taron bikin bauta na Fuxi, wanda yake zaman kakan al’adun gargajiyar kasar Sin, a birnin New Taipei na yankin Taiwan na kasar a yau Asabar.
An gudanar da taron bautar ne a daidai lokacin da aka yi irinsa a birnin Tianshui dake arewa maso yammacin lardin Gansu, inda ake kyautata zaton a nan ne aka haifi Fuxi.
Wannan dai ita ce shekara ta 12 a jere da al’ummomin bangarori biyu na mashigin tekun Taiwan ke gudanar da bukukuwan bauta a lokaci guda ga fitaccen jarumin, tun bayan da aka fara gudanar da ire-iren wannan bikin a shekarar 2014. (Mai fassara: Abdulrazaq Yahuza Jere)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
Isra’ila na ci gaba da ragargaza Birnin Gaza ta sama da ƙasa
Dakarun sojan Isra’ila na ƙara nausawa cikin wani yanki mai cike da jama’a a birnin Gaza, yayin da suke ci gaba da kai farmaki ta ƙasa domin ƙwace iko da babban birnin mafi cunkoson jama’a.
Ana iya ganin yadda hayaƙi ya turnuke sararin samaniya yayin da sojojin ke harba makaman atilare da luguden bama-bamai.
Dubban mutane sun gudu, wasu kuma sun maƙale saboda haɗarin da ke tattare da guduwar. Sama da mutane sittin ne aka ce an kashe a jiya kadai.
Isra’ila ta ce tana gudanar da bincike kan rahotannin da ke cewa dakarunta sun kai hari kan asibitin yara na Gazan.
Ta ce tana son kubutar da mutanenta da Hamas ta rike da su, da kuma fatattakar mayaƙan Hamas 3,000 a wurin da ta bayyana a matsayin “tungar mayaƙan ta ƙarshe”.