Daruruwan mutane ne suka halarci taron bikin bauta na Fuxi, wanda yake zaman kakan al’adun gargajiyar kasar Sin, a birnin New Taipei na yankin Taiwan na kasar a yau Asabar.

An gudanar da taron bautar ne a daidai lokacin da aka yi irinsa a birnin Tianshui dake arewa maso yammacin lardin Gansu, inda ake kyautata zaton a nan ne aka haifi Fuxi.

Wannan dai ita ce shekara ta 12 a jere da al’ummomin bangarori biyu na mashigin tekun Taiwan ke gudanar da bukukuwan bauta a lokaci guda ga fitaccen jarumin, tun bayan da aka fara gudanar da ire-iren wannan bikin a shekarar 2014. (Mai fassara: Abdulrazaq Yahuza Jere)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnonin APC Sun Nemi Tinubu Ya Ƙirkiri ‘Yansandan Jihohi Don Yaƙar Matsalar Tsaro

Ya ce duk da cewa akwai damuwa kan yadda za a aiwatar da hakan, Gwamnatin Tarayya na da damar tsara ƙa’idoji da dokoki na musamman ga kowace jiha don hana amfani da ‘yansandan wajen cin zarafi.

A halin yanzu, gwamnonin jihohi daga faɗin Nijeriya na gudanar da wani taron gaggawa a Babban Birnin Tarayya, wanda ke gudana a sakatariyar Ƙungiyar Gwamnonin Nijeriya (NGF).

Taron ya samu halartar gwamnonin jihohi da mataimakansu daga dukkanin jihohi 36 na ƙasar.

Koda yake ba a bayyana cikakken ajandar taron ba, kasancewar mai bai wa shugaban ƙasa shawara kan harkokin tsaro, Nuhu Ribadu, da Ministan Tsaro, Mohammed Badaru, na cikin mahalarta taron, ya nuna cewa batutuwan tsaro ne ke kan gaba a tattaunawar.

Taron na gaggawa na zuwa ne a daidai lokacin da tsaro ke taɓarɓarewa a sassa da dama na ƙasar, lamarin da ke ƙara haifar da kira daga al’umma da shugabanni domin ɗaukar matakin gaggawa da haɗin gwiwa tsakanin jihohi da Gwamnatin Tarayya.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ministan Harkokin Wajen Iran ya isa taron Kungiyar OIC a Turkiyya
  • Rundunar PLA Ta Soki Birtaniya Bisa Zuzuta Abun Da Ya Wakana Yayin Da Jirgin Ruwan Sintirinta Ya Keta Ta Zirin Taiwan 
  • Tinubu Zai Zaɓi Mataimakinsa Bayan Taron Jam’iyya – Fadar Shugaban Ƙasa 
  • 2027: ‘Sai bayan babban taron APC Tinubu zai bayyana wanda za su yi takara tare’
  • Bikin Ranar Muhalli Ta Duniya: Akwai Babban Aiki A Gaban Nijeriya
  • Sin Na Son Taka Rawar Gani Wajen Maido Da Kwanciyar Hankali A Yankin Gabas Ta Tsakiya Cikin Sauri
  • Daga Xi’an Zuwa Astana: Me Muka Koya Daga Taron Kolin Sin Da Kasashen Tsakiyar Asiya
  • Tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa, Namadi Sambo Ya Karyata Sauya Sheƙa Zuwa APC
  • Gwamnonin APC Sun Nemi Tinubu Ya Ƙirkiri ‘Yansandan Jihohi Don Yaƙar Matsalar Tsaro