An kashe matar aure, manomi ya jikkata a wani sabon hari a Kaduna
Published: 22nd, June 2025 GMT
Wasu da ake zargin ‘yan bindiga ne sun kai hari wasu ƙauyuka biyu da ke Ƙaramar Hukumar Kajuru a Jihar Kaduna.
A yayin harin, wata matar aure ta rasu, yayin da wani manomi ya samu rauni.
’Yan bindiga sun sace babban alƙali a Bayelsa Dole a ɗauki mataki kan waɗanda suka kashe ’yan ɗaurin aure a Filato — Uba SaniHarin farko ya faru ne da misalin ƙarfe 2 na daren ranar Asabar, 21 ga watan Yuni, 2025, a ƙauyen Ungwan Sarkin Hausa da ke Rimau.
Ana zargin maharan sun gudu da shanun da suka sato daga Ƙaramar Hukumar Kauru.
A lokacin harin, sun kashe wata mata mai suna Misis Alheri Danzaria.
Sun kuma sace wasu mutum biyu, amma daga baya suka sake su.
Hari na biyu ya faru ne da safiyar ranar Lahadi da misalin ƙarfe 7 a ƙauyen Kallah.
A nan ne suka harbi wani manomi mai suna Mista Iliya Barde, yayin da yake kan hanyarsa ta zuwa gona.
An garzaya da shi asibiti inda yake samun kulawar likitoci.
Shugaban gundumar Kufana, Mista Stephen Maikori, ya ce hare-haren da ake yawan kai wa sun haddasa tsoro da damuwa a tsakanin mazauna yankin.
Ya buƙaci gwamnati da ta ɗauki matakin gaggawa wajen ƙara tsaro a yankin.
Da aka tuntuɓi kakakin rundunar ‘yan sandan jihar, DSP Mansir Hassan, ya ce zai bincika lamarin sannan ya bayar da amsa, amma har zuwa lokacin haɗa wannan rahoto bai yi ƙarin haske ba.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: hari Ƙauyuka matar aure
এছাড়াও পড়ুন:
Wani ya kashe mahaifiyarsa mai shekara 71 a Akwa Ibom
Rundunar ’yan sandan Jihar Akwa Ibom ta kama wani mutum mai suna Alexander Peter bisa zarginsa da kashe mahaifiyarsa mai suna Madam Atiny Peter mai shekara 71 da adda.
Lamarin ya faru ne a ƙauyen Ikot Inyang da ke ƙaramar hukumar Oruk Anam a Jihar Akwa Ibom.
Yin sulhu da ’yan bindiga dabara ce ba gazawa ba — Gwamnatin Sakkwato Katolika ta horar da shugabannin al’umma da na addini kan zaman lafiyaKwamishinan ’yan sandan jihar, CP Baba Mohammed Azare ne ya tabbatar da kamen a yayin ganawa da manema labarai a ranar Alhamis, a hedikwatar ’yan sanda da ke Ikot Akpan Abia, a Uyo.
Kwamishinan ’yan sandan ya bayyana cewa, an kama wanda ake zargin Alexander ne a ranar 10 ga watan Yuni, kuma a halin yanzu ana ci gaba da gudanar da bincike don gano musabbabin wannan ɗanyen aikin.
“Mummunan lamarin ya faru ne a ƙauyen Ikot Inyang da ke ƙaramar hukumar Oruk Anam, inda rahotanni suka ce wanda ake zargin ya yi amfani da adda ne wajen yi wa mahaifiyarsa kisan gillar,” in ji Kwamishinan, inda ya ce rundunar ’yan sandan na ƙoƙarin bankaɗo lamarin tare da gano musabbabin wannan aika-aika.
Kwamishinan ya kuma bayyana cewa, an kama mutane 54 da ake zargi a faɗin jihar a cikin makonni shidan da suka gabata bisa aikata laifuka daban-daban.
Bugu da ƙari, rundunar ta ƙwato makamai da alburusai sama da 50 a wannan lokacin.
Kisan ya haifar da damuwa a cikin al’ummar yankin, inda mazauna yankin suka kaɗu matuƙa game da kisan da ɗan tsohuwar ya yi wa mahaifiyarsa da hannunsa.
‘Yan sanda sun ce za a samu ƙarin bayani yayin da ake ci gaba da gudanar da bincike.