An kashe matar aure, manomi ya jikkata a wani sabon hari a Kaduna
Published: 22nd, June 2025 GMT
Wasu da ake zargin ‘yan bindiga ne sun kai hari wasu ƙauyuka biyu da ke Ƙaramar Hukumar Kajuru a Jihar Kaduna.
A yayin harin, wata matar aure ta rasu, yayin da wani manomi ya samu rauni.
’Yan bindiga sun sace babban alƙali a Bayelsa Dole a ɗauki mataki kan waɗanda suka kashe ’yan ɗaurin aure a Filato — Uba SaniHarin farko ya faru ne da misalin ƙarfe 2 na daren ranar Asabar, 21 ga watan Yuni, 2025, a ƙauyen Ungwan Sarkin Hausa da ke Rimau.
Ana zargin maharan sun gudu da shanun da suka sato daga Ƙaramar Hukumar Kauru.
A lokacin harin, sun kashe wata mata mai suna Misis Alheri Danzaria.
Sun kuma sace wasu mutum biyu, amma daga baya suka sake su.
Hari na biyu ya faru ne da safiyar ranar Lahadi da misalin ƙarfe 7 a ƙauyen Kallah.
A nan ne suka harbi wani manomi mai suna Mista Iliya Barde, yayin da yake kan hanyarsa ta zuwa gona.
An garzaya da shi asibiti inda yake samun kulawar likitoci.
Shugaban gundumar Kufana, Mista Stephen Maikori, ya ce hare-haren da ake yawan kai wa sun haddasa tsoro da damuwa a tsakanin mazauna yankin.
Ya buƙaci gwamnati da ta ɗauki matakin gaggawa wajen ƙara tsaro a yankin.
Da aka tuntuɓi kakakin rundunar ‘yan sandan jihar, DSP Mansir Hassan, ya ce zai bincika lamarin sannan ya bayar da amsa, amma har zuwa lokacin haɗa wannan rahoto bai yi ƙarin haske ba.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: hari Ƙauyuka matar aure
এছাড়াও পড়ুন:
Abin Da APC Za Ta Yi Da Rinjayen Kashi Biyu Bisa Uku A Majalisar Tarayya
Samun rinjayen da APC ta yi na kaso biyu bisa uku a dakunan majalisa biyu yana da babban tasiri ga tsara dokoki, gyaran kundin tsarin mulki da kuma tsarin iko a cikin majalisar tarayya.
Dangane da gyare-gyaren kundin tsarin mulki, bisa sashe na 9 (2) da (3) na kundin tsarin mulki na 1999 (kamar yadda aka gyara), kowane kudiri da ke neman canza kundin tsarin mulki dole ne ya sami goyon bayan akalla kashi biyu cikin uku na dukkan mambobin kowanne majalisa kuma a tabbatar da kashi biyu cikin uku na majalisun jihohi 36 (jihohi 24).
Bisa adadin mambobinta a yanzu, cikin sauki APC na iya tura dokokin gyaran kundin tsarin mulki a majalisar tarayya, ko da yake amincewar matakin jiha na ci gaba da kasancewa wani shinge da ake bukata.
Haka kuma, dangane da tsige shugaban kasa ko mataimakinsa, sashe na 143 (4) da (9) na kundin tsarin mulki na bukatar rinjaye na kaso biyu bisa uku a dukkan majalisu biyu don cire shugaban kasa ko mataimakin shugaban kasa saboda aikata laifuka masu tsanani. A hali ynzu dai, jam’iyyar APC tana iya kare shugaban kasa daga kowace yunkurin tsige shi, domin ‘yan majalisa na adawa ba su da yawan da za su iya yunkurin tsige shugaban kasa ko mataimakinsa.
Kazalika, dangane da cire duk wani babbab jami’an gwamntin kuwa, sashe na 50 (2)(c) da 92 (2)(c) na kundin tsarin mulki sun tanadi cewa shugaban majalisar dattawa da shugaban majalisar wakilai ko mataimakansu za a iya cire su ne kawai da rinjaye na kashi biyu cikin uku na majalisunsu. Wannan yana nufin cewa a halin yanzu manyan jami’an gwamnati na iya samun goyon bayan rinjayen APC mai yawa wajen samun kariya daga kokarin korarsu daga mukamansu.
Idan za a ayyanawa ko tsawaita dokar ta-baci a jiha, sashe na 305 (6) na kundin tsarin mulki yana bukatar rinjaye na kashi biyu bisa uku na kowanne majalisar domin shugaban kasa ya sanar ko tsawaita dokar ta-baci a jiha. Bisa samun gagarumin rinjaye, APC ka iya jagorantar majalisa na amincewa da irin wannan bukata cikin sauki, wanda ke ba shugaban kasa karin iko wajen harkokin tsaro na kasa ko rikice-rikicen siyasa.
Idan za a iya tunawa a lokacin muhawarorin da suka shafi ayyana dokar ta-baci a Jihar Ribas, majalisar dattawa ta fara dakatarwa saboda rashin samun yawan kuri’u kashi biyu bisa uku, yayin da majalisar wakilai ta amince da shi ne bayan cike ka’idojin aiki.
A yanzu APC na da ikon yanke hukunci a dukkan majalisun biyu, jam’iyyar mai mulki tana da damar zartar da muhimman hukunci bisa karancin bangaren ‘yan adawa.
A yayin da yake yin sharhi kan samun rinjayar jam’iyyar APC mai mulki da kuma ikonta a majalisar tarayya kafin zaben 2027, wani masanin siyasa, Farfesa Gbade Ojo, ya yi gargadi kan kalubalen da makomar dimokuradiyyar Nijeriya zai iya fuskanta.
“Abin da muke shaidawa shi ne, ci gaba da fadada jam’iyyar APC mai mulki. Duk da cewa hakan na iya bayyana a matsayin karfin siyasa a fili, tasirinsa ga dimokuradiyya abin damuwa ne sosai,” in ji shi.
Ya yi gargadin cewa a irin wannan yanayi, majalisar kasa na iya rasa ‘yancinta tare da zama ‘yar amshin shadar bangaren zartarwa. Ya ce idan har ‘yan adawa ba su tashi tsaye ba, to dimokuradiyyar Nijeriya za ta ci gaba da zama cikin hadari.
2027: Rikicin PDP Ya Kara Kazanta Yayin Da Aka Sake Samun Rarrabuwar Kai A Jam’iyyar
Jam’iyyar PDP ta sake fuskantar kazamin rikici bayan da babbar kotun tarayya a Abuja ta dakatar da hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC), daga amincewa da shirya babban taron jam’iyyar da aka shirya a Ibadan, Jihar Oyo.
Alkali James Omotosho ya bayar da umarnin hana wasu ayyuka yayin da yake yanke hukunci kan wani kara da ya kalubalanci halaccin taron da aka shirya, hukuncin dai ya sake sama tsofaffin raunuka jam’iyyar tare da janyo kazamin rarrabuwan kawuna a cikin babban jam’iyyar adawar ta Nijeriya.
Duk da hukuncin, shugabannin PDP sun dage cewa taron zai gudana kamar yadda aka tsara, suna bayyana hukuncin a matsayin cin fuska ga dimokuradiyya ta cikin gida da kuma tauye hakkin kundin tsarin mulkinsu na gudanar da harkokinsu na jam’iyya.
A cikin martanin kwamitin gudanarwa na kasa na jam’iyyar, ya sanar da dakatar da manyan jami’ai, ciki har da sakataren jam’iyyar na kasa, Samuel Anyanwu da sakataren shirye-shiryenta na kasa, Umar Bature da mashawarcin shari’a na kasa, Kamaldeen Ajibade da mataimakin mashawarcin shari’a na kasa, Okechukwu Osuoha saboda zargin karya kundin tsarin jam’iyyar.
Amma lamarin ya dauki sabon salo lokacin da wani bangare na jam’iyyar ya fitar da nasa jerin sunayen wadanda ya dakatar, wannan karon yana nufin shugaban jam’iyyar na kasa, Umar Damagum da sakatar yada labarai, Debo Ologunagba da wasu mutum hudu duk an dakatar da su, wanda lamarin ya kara rikitarwa game da wanda yake da cikakken iko a cikin PDP.
Wasu majiyoyi daga cikin PDP sun nuna cewa hana tsohon gwamnan Jigawa, Sule Lamido, takarar shugabancin jam’iyyar na daya daga cikin musabbabin sabon rikicin.
“Lamido yana daya daga cikin wadanda suka ki shiga ayyukan PDP a baya har sai an dakatar da Wike. Yanzu an gan shi yana hada kai da masu goyon bayan Wike, wanda ke nuna inda sababbin rikicin ya sake kunno kai,” in ji wata majiya.
A cewar wata majiya ta daban, yunkurin Lamido na sayen fam din takarar shugaban jam’iyyar a makare wata alama ce na cewa akwai lauje cikin nadi.
“Ana sayar da fam a Gidan Legacy, ba a Wadata Plaza ba. An fara sayar da fam din ne tun a ranar 2 ga Satumba kuma an rufe a ranar 22 ga Satumba, tare da kara lokacin mika fam din har zuwa 27 ga Oktoba. To ta yaya mutum zai iya zuwa a ranar karshe ya yi ikirarin cewa bai samu fam ba?” in ji majiyar.
Yayin da PDP ke fama da shari’o’I a kotu, dakatar da juna da kuma tawaye na rarrabuwar kai, masu ruwa da tsaki a jam’iyya suna cewa babban kalubale yanzu shi ne sake gina sahihancin jam’iyyar da hadin kai kafin 2027.
Manyan jiga-jigan jam’iyya sun yi gargadin cewa idan ba a samu sulhu da jagoranci mai kyau ba, jam’iyyar adawa na iya fuskantar karin rarrabuwan kawuna kafin zaben 2027.
Ga jam’iyyar adawa mafi shahara a Nijeriya ta PDP, a halin yanzu aikin ya wuce kawai shirya babban taro, yana da alaka da dawo da aminci da hadin kai da kuma karfafa alaka kafin zaben 2027.
ShareTweetSendShare MASU ALAKA