An kashe matar aure, manomi ya jikkata a wani sabon hari a Kaduna
Published: 22nd, June 2025 GMT
Wasu da ake zargin ‘yan bindiga ne sun kai hari wasu ƙauyuka biyu da ke Ƙaramar Hukumar Kajuru a Jihar Kaduna.
A yayin harin, wata matar aure ta rasu, yayin da wani manomi ya samu rauni.
’Yan bindiga sun sace babban alƙali a Bayelsa Dole a ɗauki mataki kan waɗanda suka kashe ’yan ɗaurin aure a Filato — Uba SaniHarin farko ya faru ne da misalin ƙarfe 2 na daren ranar Asabar, 21 ga watan Yuni, 2025, a ƙauyen Ungwan Sarkin Hausa da ke Rimau.
Ana zargin maharan sun gudu da shanun da suka sato daga Ƙaramar Hukumar Kauru.
A lokacin harin, sun kashe wata mata mai suna Misis Alheri Danzaria.
Sun kuma sace wasu mutum biyu, amma daga baya suka sake su.
Hari na biyu ya faru ne da safiyar ranar Lahadi da misalin ƙarfe 7 a ƙauyen Kallah.
A nan ne suka harbi wani manomi mai suna Mista Iliya Barde, yayin da yake kan hanyarsa ta zuwa gona.
An garzaya da shi asibiti inda yake samun kulawar likitoci.
Shugaban gundumar Kufana, Mista Stephen Maikori, ya ce hare-haren da ake yawan kai wa sun haddasa tsoro da damuwa a tsakanin mazauna yankin.
Ya buƙaci gwamnati da ta ɗauki matakin gaggawa wajen ƙara tsaro a yankin.
Da aka tuntuɓi kakakin rundunar ‘yan sandan jihar, DSP Mansir Hassan, ya ce zai bincika lamarin sannan ya bayar da amsa, amma har zuwa lokacin haɗa wannan rahoto bai yi ƙarin haske ba.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: hari Ƙauyuka matar aure
এছাড়াও পড়ুন:
An Cafke Wani Magidanci Da Lafin Sojan Gona A Katsina
“A yayin binciken motar, an samu waɗannan abubuwa daga hannun wanda ake zargin: bindiga ta gida guda ɗaya, harsashi guda huɗu, harsashi biyu da aka harba a baya, katin shaida na ƴ an sanda na bogi, da kuma ƙarin lambar rijistar mota ta (Kano FGE 68).”
“Wanda ake zargin yana tsare a hannun jami’an tsaro yayin da ake ci gaba da gudanar da bincike don gano ainihin dalilan mallakar bindiga, katin shaida na bogi, da sauran abubuwan da aka kama daga gare shi.”
“Ƙungiyar jami’an tsaro, bisa ƙarin lura da dabarun tsaron zamani, ta dakatar da wani motar Toyota Corolla, launin toka, mai lambar rijista Lagos GGE 473 BH, wanda wanda ake zargi ya ke tukawa. Bayan an yi masa tambayoyi, bai iya bayar da cikakken bayani kan kansa ko motar ba, lamarin da ya sa aka gudanar da bincike nan take.
“A yayin binciken motar, an samu waɗannan abubuwa daga hannun wanda ake zargin: bindiga ta gida guda ɗaya, harsashi guda huɗu, harsashi biyu da aka harba a baya, katin shaida na ƴ an sanda na bogi, da kuma lambar rijista ta ƙari (Kano FGE 68).”
“Wanda ake zargin yana tsare a hannun jami’an tsaro yayin da ake ci gaba da gudanar da bincike don gano ainihin dalilan mallakar bindiga, katin shaida na bogi, da sauran abubuwan da aka kama daga gare shi.”
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp