An Cafke Mutum 22 Kan Kisan ‘Yan Ɗaurin Aure A Filato – Uba Sani
Published: 24th, June 2025 GMT
Wasu kuma sun jikkata a harin.
Gwamna Sani ya ce kisan rashin imani ne, kuma ya bayyana cewa ya tattauna da Gwamnan Filato, Caleb Mutfwang, da Shugaban Ƙasa Bola Tinubu don tabbatar da cewa an hukunta waɗanda suka aikata wannan aika-aika.
Ya kai ziyara ga waɗanda suka tsira daga harin a Asibitin Rundunar Sojin Naieriya na 44 da ke Kaduna, sannan ya yaba wa jama’ar Kaduna kan zaman lafiya da kaucewa fitina.
Ya kuma roƙi shugabannin Filato da su hana faruwar irin wannan mummunan lamari.
Gwamnan ya buƙaci hukumomin tsaro da su hanzarta kama masu laifin tare da gurfanar da su a gaban kotu.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: Yan Ɗaurin Aure
এছাড়াও পড়ুন:
An shafe wata 8 ana mulki babu mataimakin gwamna a Tataba
Mataimakin Gwamnan Jihar Taraba, Alhaji Aminu Alkali, ya yi ɓatan dabo inda ya shafe tsawon watanni takwas ba tare da an gan shi ba.
Alkali, na fama da rashin lafiya tun a bara wanda hakan ya sa bai sake bayyana a bainar jama’a ba.
Majalisa ta buƙaci ƙirƙirar sabbin ƙananan hukumomi a Bauchi Gwamna ya yi wa iyalan ’yan wasan Kano da suka rasu a hatsari goma ta arzikiAn fara kula da lafiyarsa a Asibitin Ƙasa da ke Abuja, daga baya aka kai shi ƙasar Masar domin ci gaba da jinya.
Gwamna Agbu Kefas, ya naɗa Emmanuel Lawson, ɗaya daga cikin mataimakansa, domin taimakawa wajen gudanar da ayyukan ofishin mataimakin gwamnan.
A wata wasiƙa da Sakataren Gwamnatin Jiha ya sanya wa hannu, an ce naɗin zai taimaka wajen tabbatar da ingantaccen shugabanci.
Sai dai wasu na ganin Lawson bai cancanci riƙe wannan ofishi ba saboda ba zaɓar shi aka yi ba.
Gwamnati ta ce yana murmurewaGwamnatin jihar ta bayyana cewa Alhaji Aminu Alkali na murmurewa daga ciwon shanyewar ɓarin jiki da ya shafi lafiyarsa da yanayin maganarsa.
Kwamishinan Lafiya na jihar, Bordiya Buma, ya kai masa ziyara a watan Maris kuma ya ce yana samun sauƙi.
“Muna farin ciki da samun sauƙi da yake yi kuma muna fatan zai dawo nan ba da jimawa ba.”
Sai dai har yanzu bai dawo bakin aiki ba.
Wasu rahotanni na cewa yana Abuja yana ci gaba da jinya, wasu kuma na cewa yana zaune a wani gida a unguwar Wuse.
A gefe guda kuma, ma’aikatansa sun ce ba sa ganinsa ba.
’Yan adawa na neman ba’asiWasu ‘yan siyasa da jama’a suna buƙatar gwamnati ta bayyana gaskiyar halin da mataimakin gwamnan jihar ke ciki.
“Mutanen Taraba suna da ‘yancin sanin inda mataimakin gwamna yake da halin da lafiyarsa ke ciki,” in ji Alhaji Hassan Jika Ardo, tsohon shugaban jam’iyyar APC a jihar.
Ya ce gwamnati ta daina wasa da hankalin jama’a a kan batun da dokar ƙasa ta bayyana a fili.
Dalilin da ya sa ba a sauke shi baSashe na 189 na Kundin Tsarin Mulkin Najeriya ya bayyana cewa za a iya tsige mataimakin gwamna ne kawai idan kwamitin likitoci ya tabbatar cewa ba shi da ƙoshin lafiyar da zai iya kataɓus.
Wannan na buƙatar ƙuri’a daga kashi biyu bisa uku na majalisar zartarwa ta jihar.
Har yanzu ba a ɗauki wannan matakin ba.
Siyasa ta hana a ɗauki matakiWasu majiyoyi sun ce ana matsa wa gwamnan jihar lamba kan ya sauke mataimakin nasa, amma yana tsoron kada hakan ya rushe tsarin rabon madafun iko tsakanin yankunan jihar.
Sauya mataimakin gwamnan na iya janyo rikicin siyasa a jihar.
An taɓa fuskantar irin wannan rikici a TarabaA shekarar 2012, Gwamna Danbaba Suntai, ya yi hatsarin jirgin sama kuma bai samu sauƙi ba na tsawon watanni.
Rikici ya ɓarke saboda ba a bayyana halin da yake ciki ba, kuma bai miƙa wa majalisa wasiƙar cewa ba zai iya ci gaba da aiki ba.
Wannan ya janyo rikici da rarrabuwar kawuna tsakanin masu goyon bayan gwamnan da na mataimakinsa.
Ra’ayoyin lauyoyi sun bambantaWasu lauyoyi sun ce lokaci ya yi da gwamnati za ta aiwatar da dokar ƙasa.
“Rashin lafiyar mataimakin gwamna ta shafi ci gaban jihar. Idan ba zai iya aiki ba, ya kamata ya sauka,” in ji lauya mai kare haƙƙin bil’adama, Malachy Ugwumadu.
Amma wani babban lauya, Richard Ahonaruogho (SAN), ya ce jihar ba ta cikin matsala dangane da rashin lafiyarsa.
“Muddin gwamna bai koka cewa ba zai iya aiki ba, babu buƙatar ɗaukar mataki,” in ji shi.
Jama’a sun fara gajiyaYayin da aka shafe tsawon lokaci babu mataimakin gwamnan, mutane da dama a jihar suna fara nuna damuwa.
Wasu na ganin rashin bayyana gaskiya yana nuna rashin girmama masu kaɗa ƙuri’a.
Yanzu dai idanun mutane sun karkata ne kan gwamnan da majalisar dokokin jihar domin su bayyana gaskiya ko su ɗauki matakin doka.