An Cafke Mutum 22 Kan Kisan ‘Yan Ɗaurin Aure A Filato – Uba Sani
Published: 24th, June 2025 GMT
Wasu kuma sun jikkata a harin.
Gwamna Sani ya ce kisan rashin imani ne, kuma ya bayyana cewa ya tattauna da Gwamnan Filato, Caleb Mutfwang, da Shugaban Ƙasa Bola Tinubu don tabbatar da cewa an hukunta waɗanda suka aikata wannan aika-aika.
Ya kai ziyara ga waɗanda suka tsira daga harin a Asibitin Rundunar Sojin Naieriya na 44 da ke Kaduna, sannan ya yaba wa jama’ar Kaduna kan zaman lafiya da kaucewa fitina.
Ya kuma roƙi shugabannin Filato da su hana faruwar irin wannan mummunan lamari.
Gwamnan ya buƙaci hukumomin tsaro da su hanzarta kama masu laifin tare da gurfanar da su a gaban kotu.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: Yan Ɗaurin Aure
এছাড়াও পড়ুন:
Taron Canada: Haɗin Gwiwa Afirka Ke Buƙata Ba Agaji Ba – Gwamnan Zamfara
Sanarwar ta ƙara da cewa, Gwamna Lawal ya jaddada cewa tsarin dimokuraɗiyyar Kanada, ƙarfafan tattalin arziƙi, hakar ma’adinai ta hanyar da ta dace, da kuma harkokin kasuwanci masu zaman kansu masu kirkire-kirkire sun sanya ta zama abokiyar haɗin guiwar da ta ta dace ga Afrika.
Ya ce, “Idan Afrika za ta cika burinta gaba ɗaya, dole ne mu gane cewa ci gaba ba wai kawai batun manufofin ƙasa bane; yana kuma buƙatar aikace-aikacen matakan jihohi da ƙananan hukumomi.
“Yayin da Gwamnatocin Tarayya ke ba da jagorar manufofi, a matakin Jihohi, larduna, da Ƙananan Hukumomi ake fassara alƙawuran kasuwanci, zuba jari da ci gaba zuwa ainihin gaskiya.
“Matakan jihohi sune inda manoma ke noma abincin da ke ciyar da ƙasashe, inda aikin haƙar ma’adinai ke yin nasara ko faɗuwa, inda matasa ke neman dama, da inda masu zuba jari ke bukatar tsari mai bayyana, kwanciyar hankali, da dawowa mai adalci. Wannan shi ya sa kasancewata a nan a matsayin Gwamnan Zamfara ba da gangan bane, illa da nufin ƙarfafawa. Yana nuna cewa tashin hankali na Afrika zai samo asali ne daga jihohi da larduna kamar yadda zai fito daga manyan birane.”
Gwamnan ya ƙara da cewa gwamnatinsa na canza tsarin mulki a Zamfara da yanayin saka jari don jawo hankalin abokan hulɗa masu gaskiya waɗanda ke da darajar gaskiya, rikon amana, da ci gaba mai ɗorewa.
“Noma shi ne ginshiƙin tattalin arziƙinmu. Fiye da kashi 70 na ƙasar mu tana da filin noma, Zamfara na iya zama amfanin gona ga Nijeriya da ma nahiyar Afrika. Muna neman haɗin kai a fannonin injina, ban ruwa, kula da amfanin gona bayan girbi, ajiya, da sarrafa kayan gona. Kwarewar Kanada, haɗe da jajircewar manomanmu, na iya samar da sabon tsarin tsaron abinci ga Afrika.
“Baya ga noma, Zamfara na da ma’adinai masu daraja kamar zinariya, lithium, manganese, da granite waɗanda suke da muhimmanci ga sauyin makamashi. Muna ƙoƙarin koyon darasi daga kurakurai na baya, domin tabbatar da cewa arzikin albarkatu ya fassaru zuwa ci gaba, ba wai fitarwa kawai ba. Muna ƙarfafa dokoki, inganta hakar ma’adinai na gaskiya, da tabbatar da amfanin al’umma.”
“Ina kira ga abokanmu na Kanada da su duba bayan manyan biranen Afrika zuwa yankuna, gonaki, makarantun, masana’antu, da al’ummomi, inda ainihin haɗin kai zai bunƙasa. Ku ƙarfafa shugabannin Afrika, ciki har da ni, wajen yin garambawul, ƙarfafa mulki, tsayawa kan gaskiya, da gina muhalli mai kyau ga haɗin kai.”
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp