Aminiya:
2025-09-20@11:03:53 GMT

An sallami ƙarin ma’aikata 639 a tashar Muryar Amurka

Published: 21st, June 2025 GMT

Hukumar da ke kula da kafar yaɗa labarai ta Muryar Amurka (VOA) ta sallami ƙarin ’yan jarida da sauran ma’aikata 639 a ranar Juma’a.

Hukumar Kula da Harkokin Watsa Labarai ta Duniya ta Amurka (USAGM) ta bayyana cewa kawo yanzu an sallami ma’aikata 1,400 a wani bangare na shirin Shugaban Amurka Donald Trump na rage ma’aikata a hukumar zuwa mafi ƙarancin adadi kamar yadda doka ta tanada.

Hakan na nufin an kori mutum takwas a cikin kowane ma’aikata 10 da ke VOA a wata uku da suka gabata, a sakamakon wannan matakin Hukumar USAGM ta ɗauka.

Babbar Mashawarciya ga Hukumar, Kari Lake, ta bayyana cewa, “An aika wa ma’aikata 639 a VOA da USAGM da takardun kora a matsayin wani ɓangare na ƙoƙarin da ya kamata a yi tun da daɗewa don kawar da dimbin ma’aikata cima-zaune da kuma rashin riƙon amana a hukumar,” in ji sanarwar da ta fitar.

Yadda Iran ta lalata cibiyar kimiyya mafi muhimmanci a Isra’ila 2027: Manyan ’Yan adawa na neman rajistar sabuwar jam’iyya

Lake ta kuma tabbatar da cewa hukumar ta kasance “cike da jami’an da ba sa aiki komai, nuna son kai, da ɓarnatar da dukiya.”

Ta bayyana cewa wannan mataki na nufin USAGM yanzu tana aiki kusa da mafi ƙarancin ma’aikata 81 da doka ta tanada.

Ma’aikata 250 kuma za su ci gaba da zama a Ofishin Watsa Labarai na Cuba (OCB), wanda ke watsa labarai zuwa ƙasar Cuba mai mulkin kwaminisanci.

An lura cewa babu ko ɗaya daga cikin ma’aikata 33 na OCB da aka kora.

Wannan mataki mai yiwuwa alama ce ta kusan kawo ƙarshen wannan shahararren gidan rediyo VOA wanda miliyoyin mutane ke saurara tsawon shekara 50 a faɗin duniya.

VOA, wadda aka kafa a 1942 don yaƙar farfagandar Nazi, tana watsa shirye-shirye a kusan harsuna 50 kuma ta mutane miliyan 360 ke sauraron shirye-shiryenta a mako, a faɗin duniya.

A watan Mayu aka kori ma’aikatan kwangila kusan 600 na VOA.

Wasu ’yan jam’iyyar Republican a baya sun zargi tashar da sauran kafofin yaɗa labarai masu samun tallafin gwamnati da nuna son kai ga masu ra’ayin mazan jiya, suna masu kira da a rufe tashar a matsayin wani ɓangare na rage kashe kuɗin gwamnati.

Wata tashar USAGM, Radio Free Asia, wadda tuni aka rage ma’aikatanta sosai, ta sanar a cikin wani sakon imel ga ma’aikata a ranar Juma’a cewa tana aiwatar da karin hutun tilas a sassa daban-daban.

Ana ci gaba da shari’o’i daban-daban kan lamarin korar ma’aikatan na USAGM.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: koran ma aikata

এছাড়াও পড়ুন:

Murnar Maulidin Cikar Manzon Allah (SAW) Shekara 1,500 Da Haihuwa (2)

Sai yace “A’a ba haram ba ne, kawai dai mutanena ba su san shi ba ne.” Annabi (SAW) ya taɓa cewa kar a ci tafarnuwa a shigo masallaci, aka tambaye shi: “Ya Rasulallah haram ne?” Sai ya ce “A’a ba na haramta abin da Allah bai haramta ba, kawai dai ni ne ba na son shi”, ka ga bambancin ladabin malamai na wancan zamani da na yanzu, a yanzu duk abin da wani Malami ba ya so sai kawai ya haramta shi. Amma duk inda Allah ya ce “hurrimat…” To wannan na Azal da Abadan ne. Kuma dokokin ko wace ƙasa za ka ga duk abubuwan da Allah ya haramta a Alƙur’ani ɗin nan guda 38 su ma sun haramta shi a dokar ƙasarsu. To yanzu kuma halal ɗin nan, Allah ya yarda idan wani hali ya zo to hukumar majalisar dokoki za ta iya hanawa, ƙabila za ta iya hanawa, kai ma za ka iya hana kanka!

Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallam Ma’aikin Allah ne, Annabin Allah ne, sannan kuma shugaban ƙasa ne a wancan lokacin, shi yake tsara dokokin ƙasa (constitution) na ƙasarsa (Sallallahu Alaihi Wasallam), don haka yana hana wasu abubuwan kuma ya halatta wasu abubuwan, kamar yanda aka taɓa tambayar Abdullahi ɗan Abbas, sai ya ce: “to wallahi ni ma doka kaza da kaza ban sani ba na wucingadi ne ko kuwa na dindindin ne”. Don haka, majalisar dokoki ba za ta ce “na haramta kaza” ba, sai dai ta ce “na hana kaza saboda dalili kaza”, to duk ranar da wannan dalilin ya ɗauke sai ka ji an janye wannan hanin kuma.

Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallam shari’arsa ta zo a mai tafiya ce, shi cikamakon Ma’aika ne, cikamakon Annabawa ne, don haka komai nasa na har ƙarshen halitta ne, don haka ne ya zamo rahama ga halitta gaba ɗaya. Don haka babu wanda za ka je masa da faɗa ka tilasta masa ya karɓi ra’ayinka, Manzo ne, Ma’aiki ne ga duk duniya gaba ɗaya, ya zo ya daidaita addininsa a cikinmu, ya yaɗa zaman lafiya a cikinmu, ya yaɗa girmama ɗan Adam; dama abu biyu ne addini; Allah ya saka ma Shehu Ibrahim (RTA) da alheri, yana cewa: “abu biyu ne addini, Girmama Allah da tausayin ɗan Adam, wannan shine addini”, duk abin da za ka ga addini yana kira, za ka ga a kan waɗannan abubuwan biyun ne. Don haka suka ce: “duk addinin da ya kira ka zuwa cewa  kar ka tausaya ma ɗan Adam to ba daga Allah yake ba”. Domin Allah shi ya halicci ɗan Adam ɗin nan, shi ya busa masa ransa, to kuwa Allah Tabaraka wa Ta’ala ba zai wulaƙanta ɗan Adam ɗin nan ba. 

Mutum kansa idan ya ƙera tukwane, ba zai yadda haka kawai wani ya zo ya farfasa masa tukwanensa ba, haka idan ka sayi sabon abin hawa ba zaka yarda kawai wani ya zo ya farfasa maka shi ba, da yara sun zo suna wasan jifa a kusa da abin hawan ka zaka kore su ne, ba don kar su fasa maka kai ba ne, a’a, domin kar su fasa maka abin hawan nan naka, to ka ga ta yaya Allah shi kuwa zai bar halittarsa a zo ana aibata ta ana halaka ta? Wallahi mu ji tsoron Allah. Wannan ya jawo ake mayar da addininmu baya. Manzon Allah ya zo ya yaɗa zaman lafiya, ya yaɗa girmama ɗan Adam, ya yaɗa soyayya a tsakaninsu, ya yaɗa daidaito a tsakanin ƙabilu da jinsunan mu, ayar Alƙur’ani ta ce, “Ya ayyuhan nasu innaa khalaƙnakum min zakarin wa untha, wa ja’alnaakum shu’uban wa ƙaba’ila lita’arafu; inna akramakum indallahi atƙaakum”. Ma’anar wannan aya ta sama tana nufin ko da Bayahude ko Bamajuse ko kuma ɗan kowanne addini idan ya fi ka tsoron Allah, to fa ya fika a wajen Allah, domin Allah “ya ayyuhan nasu” ya ce ba “ya ayyuhal muslimuna” ba. 

Akwai wani Bature, ya karanta littafan Annabawa da suka gabata da duk sauran littafan da ake cewa Allah ne ya saukar dasu, ya dudduba ya yi nazari, sai da Allah ya kawo shi Misra, ya haɗu da abokinsa sai ya sami ganin Kur’ani ta wajen abokin nan nasa kuma abokin ya tabbatar masa cewa shi ma wannan littafi daga Allah ne, sai ya ce to a ba shi ya duba (watau Alkur’ani mai fassara zuwa Ingilishi). Yana fara karantawa sai kuwa ya ce: “Haba! Yanzu na ji Allah ne yake magana! Amma duk waɗancan sauran littafan ina jin wani mutum ne abokina ko wani sarki mutum ne yake magana!”

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Takari: Rayuwar baƙin haure ’yan Najeriya mazauna Saudiyya
  • An cafke mutum 6 kan tono gawa a kabari don yin asiri a Gombe
  • Murnar Maulidin Cikar Manzon Allah (SAW) Shekara 1,500 Da Haihuwa (2)
  • Ce-ce-kuce Kan Shirin Ƙara Wa Ƴan Siyasa Masu Riƙe Da Madafun Iko Albashi
  • Amurka ta hau kujerar-na-ƙi kan buƙatar MDD ta tsagaita wuta a Gaza
  • An yanke wa Soja hukuncin kisa ta hanyar rataya
  • Wani ya sace munduwar Fir’auna a gidan tarihin Masar
  • An kama sojan bogi da ɓarayin mota 2 a Jigawa
  • Shugabar Ma’aikata Ta Jihar Kaduna Ta Yi Kiran Amfani Da Fasahar AI.
  • Gwamna Namadi Ya Taya Malaman Makarantu Da Suka Yi Fice A Jihar Murna