Aminiya:
2025-08-05@16:26:00 GMT

Iran ta lalata cibiyar kimiyya mafi daraja a Isra’ila

Published: 21st, June 2025 GMT

Iran ta lalata cibiyar binciken kimiyya mafi muhimmanci a Isra’ila, wato cibiyar kimiyya ta Weizmann Institute of Science da ke birnin Tel Aviv.

Cibiyar, wadda ke da alaƙa da binciken harkokin sojin Isra’ila, ta sanar da cewa harin da Iran ta kawo ɗin ya yi sanadiyar ɓarnar da ta kai kimanin Dala miliyan 500.

Makaman Iran sun lalata gine-gine da dama a cibiyar, lamarin da ya sanya masu bincike faɗi-tashi don ceto samfurin bincike a cikin ɓaraguzan gini, a yayin da gobarar ke ci.

Wani makami mai linzami ya tarwatsa wani gini mai ɗauke da ɗakunan gwaje-gwaje na zamani da dama, a yayin harin na ramuwar gayya, bayan da Isra’ila ta kashe masana kimiyyar nukiliya na Iran.

Makamin ya faɗo kan cibiyar ne kafin wayewar garin ranar Lahadi, amma babu wanda ya ji rauni domin cibiyar ba kowa a cikinta a lokacin.

Fira Ministan Isra’ila, Benjamin Netanyahu ya ziyarci wurin, inda ya ce, “wannan harin ne dalilin da ya sa Isra’ila ba za a taɓa barin Iran ta mallaki makaman nukiliya ba.”

Idan ba a manta ba, Isra’ila ce ta fara kai hari kan Iran a ranar 13 ga Yuni, bisa hujjar cewa abokiyar gabar tata tana dab da ƙera makaman nukiliya.

Iran, wadda ta dage cewa shirin nukiliyarta don dalilai na zaman lafiya ne kawai, ta mayar da martani da hare-haren makamai masu linzami da na jirage marasa matuƙa a kan Isra’ila.

Hare-haren Isra’ila sun yi sanadiyar mutuwar wasu manyan masana kimiyyar nukiliya na Iran, da manyan shugabannin sojojin Iran, da fararen hula tare da lalata gidaje da tashoshin nukiliya da ababen more rayuwa.

Duk da cewa yawancin binciken cibiyar Weizmann sun danganci fannin gas magunguna da ilimin kimiyya ne, amma tana kuma da alaka da tsaro.

A watan Oktoba na 2024, ta sanar da haɗin gwiwa da babban kamfanin tsaro na Isra’ila, Elbit, kan “kayayyakin da aka samo daga halittu don aikace-aikacen tsaro.”

Cibiyar binciken kimiyya mafi muhimmanci a Isra’ila, tana da ƙungiyoyin bincike 286, masana kimiyya ma’aikata 191, da daruruwan dalibai.

Iran ta sanar a ranar Juma’a cewa ba za ta tattauna makomar shirin nukiliyarta ba yayin da take fama da hare-hare daga Isra’ila.

Duk ƙoƙarin ƙasashen Turai na jan hankalin Tehran zuwa tattaunawa bai nuna alamun nasara ba.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Iran Isra ila nukiliya

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnatin Kano Ta Karɓi Rahoton Binciken Kwamishinan Sufuri Kan Belin Wanda Ake Zargi Da Safarar Kwayoyi

Gwamnatin Jihar Kano ta karɓi rahoton kwamitin bincike da aka kafa domin bincikar zargin da ake yi wa Kwamishinan Sufuri, Ibrahim Namadi, kan hannu da yake da shi a ceto wani da ake zargi da safarar miyagun kwayoyi, Sulaiman Aminu Danwawu.

Shugaban kwamitin kuma mai bai wa Gwamna Shawara kan Harkokin Shari’a da Tsarin Mulki, Barrister Aminu Hussain, ne ya mika rahoton ga Sakataren Gwamnati na Jiha, Alhaji Umar Farouk Ibrahim.

Barrister Hussain ya bayyana cewa kwamitin ya gudanar da bincike bisa gaskiya da adalci, da kuma bin hujjoji, ba tare da son rai ba.

Ya bayyana cewa an gayyato Kwamishinan Sufuri domin karin bayani, inda ya kuma gabatar da rubutaccen jawabi ga kwamitin.

Sauran da aka tattauna da su sun hada da Abubakar Umar Sharada, Mataimaki na Musamman kan Wayar da Kan Jama’a, da kuma Musa Ado Tsamiya, Mataimaki na Musamman kan magudanan ruwa.

Don tabbatar da ingancin rahoton, kwamitin ya tuntubi hukumomin tsaro da shari’a kamar DSS, NDLEA da Kungiyar Lauyoyi ta Najeriya (NBA). An kuma duba sahihan takardu da suka danganci lamarin tare da sharuddan doka da suka dace.

Barrister Hussain ya yabawa Gwamna Abba Kabir Yusuf bisa kin tsoma baki da ya yi a lokacin gudanar da binciken, yana mai cewa hakan ya nuna irin shugabanci nagari da girmama tsarin doka.

Da yake karɓar rahoton, Sakataren Gwamnati ya nuna godiya kan yadda kwamitin ya gudanar da aikinsa bisa kwazo da kwarewa, duk da matsin lamba daga jama’a.

Ya jinjina musu kan jajircewa da tsayuwa akan gaskiya, tare da tabbatar da cewa za a mika rahoton ga Gwamna domin nazari da daukar matakin da ya dace.

Ya kara da cewa Gwamnatin Kano za ta duba cikakken rahoton tare da daukar matakan da suka dace bisa shawarar da kwamitin ya bayar.

 

Abdullahi Jalaluddeen

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Iran Ta Kafa Kwamitin Tsaron Kasa Wanda Zai Kula Da Sabbin Matsalolin Tsaro
  • Ɗaruruwan Tsaffin Jami’an Tsaron Isra’ila Sun Roki Trump Ya A Dakatar Da Yakin Gaza
  • UNICEF: Akalla yara 28 ne ke mutuwa a kowace rana a Gaza sakamakon harin Isra’ila da yunwa
  • Gwamnatin Kano ta karɓi rahoton binciken Kwamishinan da ya yi belin Danwawu
  • Gwamnatin Kano Ta Karɓi Rahoton Binciken Kwamishinan Sufuri Kan Belin Wanda Ake Zargi Da Safarar Kwayoyi
  • Ruwan Wuta Ne Kawai Maganin ‘Yan Ta’adda Ba Sasanci Ba – Mataimakin Gwamnan Zamfara
  • Sojojin Isra’ila Sun Kashe Falasɗinawa A Wurin Rabon Abinci A Gaza
  • Gwamnan Neja Ya Bada Umarnin Sake Bude Jami’ar Ibrahim Badamasi Babangida, Lapai.
  • Gwamnatin Haramtacciyar Kasar Isra’ila Tana Kokarin Boye Barnarta A Zirin Gaza
  • Shugabar Tanzania Ta Kaddamar Da Cibiyar Cinikayya Da Jigila Da Sin Ta Gina A Kasar