Aminiya:
2025-08-06@04:35:42 GMT

An kashe uban ango da ɗan uwansa a harin Filato

Published: 21st, June 2025 GMT

Mahaifin ango da ƙanin ango na daga cikin mutanen da aka kashe lokacin da wasu suka kai musu hari a Jihar Filato.

Rahotanni sun nuna cewa mutum 31 ne ke cikin wata babbar mota mai ɗaukar fasinja 18 daga Jami’ar Ahmadu Bello Zariya (ABU), yayin da aka kai musu hari.

Ɗan ƙunar baƙin wake ya kashe mutum 10 da bam a Borno An yi wa ma’aikatan ƙananan hukumomin Gombe ƙarin albashin N5,000

Mutanen sun fito ne daga unguwar Basawa da ke Ƙaramar Hukumar Zariya a Jihar Kaduna, yayin da suke kan hanyarsu ta zuwa garin Pau da ke Jihar Filato domin ɗaurin aure.

Mutum 12 sun rasu a sakamakon harin, yayin da 19 suka jikkata kuma ana kula da su a Asibitin Gwamnati na Mangu.

Ɗaya daga cikin waɗanda suka tsira, Ibrahim Umar, ya ce: “Mahaifi da ƙanin ango duk sun rasu a harin.

“Angon daga Zariya yake, amma yana aiki a matsayin malami a wata makaranta a yankin. A nan ne ya haɗu da matar da zai aura.

“Muna ɗauke da goro da sauran kayayyakin da ake kai wa wajen aure. Mun shaida wa waɗanda suka tare mu cewa ba ‘yan yankin ba ne, kuma mu ba ma faɗa, sai dai ba su saurare mu ba,” in ji shi.

Ya yaba da yadda sojojin da ke kusa da wajen suka kai musu ɗauki.

“Sojojin sun taimaka mana sosai. Da ba su zo ba, da abin ya fi haka muni,” in ji shi.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Ɗan Uwan Ango Ɗaurin Aure hari Matafiya

এছাড়াও পড়ুন:

Xizang Ya Cimma Nasarorin Tattalin Arziki Da Zamantakewa Da Suka Kafa Tarihi Cikin Shekaru Fiye Da 60

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ruftawar gini ta kashe uwa da ’ya’yanta 5 a Katsina
  • Xizang Ya Cimma Nasarorin Tattalin Arziki Da Zamantakewa Da Suka Kafa Tarihi Cikin Shekaru Fiye Da 60
  • Buni ya shirya bikin karrama daliban da suka lashe gasar duniya
  • UNICEF: Akalla yara 28 ne ke mutuwa a kowace rana a Gaza sakamakon harin Isra’ila da yunwa
  • WAEC ta saki sakamakon jarabawar 2025
  • ‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutane Da Dama A Kauyukan Zamfara
  • Gwamnatin Sakkwato Za Ta Kashe fiye da Naira Miliyan 200 Wajen Gyara Tashar Talabijin Ta Kasa NTA
  • Shirin kashe N712bn kan gyaran filin jirgin Legas ya tayar da ƙura
  • Kashe N712bn Kan Gyaran Filin Jiragen Saman Legas Rashin Sanin Ya Kamata Ne – ADC 
  • Sojojin HKI, Daga Jiya Zuwa Yau lahadi Kadai Sun Kashe Falasdinawa 62