An kashe uban ango da ɗan uwansa a harin Filato
Published: 21st, June 2025 GMT
Mahaifin ango da ƙanin ango na daga cikin mutanen da aka kashe lokacin da wasu suka kai musu hari a Jihar Filato.
Rahotanni sun nuna cewa mutum 31 ne ke cikin wata babbar mota mai ɗaukar fasinja 18 daga Jami’ar Ahmadu Bello Zariya (ABU), yayin da aka kai musu hari.
Ɗan ƙunar baƙin wake ya kashe mutum 10 da bam a Borno An yi wa ma’aikatan ƙananan hukumomin Gombe ƙarin albashin N5,000Mutanen sun fito ne daga unguwar Basawa da ke Ƙaramar Hukumar Zariya a Jihar Kaduna, yayin da suke kan hanyarsu ta zuwa garin Pau da ke Jihar Filato domin ɗaurin aure.
Mutum 12 sun rasu a sakamakon harin, yayin da 19 suka jikkata kuma ana kula da su a Asibitin Gwamnati na Mangu.
Ɗaya daga cikin waɗanda suka tsira, Ibrahim Umar, ya ce: “Mahaifi da ƙanin ango duk sun rasu a harin.
“Angon daga Zariya yake, amma yana aiki a matsayin malami a wata makaranta a yankin. A nan ne ya haɗu da matar da zai aura.
“Muna ɗauke da goro da sauran kayayyakin da ake kai wa wajen aure. Mun shaida wa waɗanda suka tare mu cewa ba ‘yan yankin ba ne, kuma mu ba ma faɗa, sai dai ba su saurare mu ba,” in ji shi.
Ya yaba da yadda sojojin da ke kusa da wajen suka kai musu ɗauki.
“Sojojin sun taimaka mana sosai. Da ba su zo ba, da abin ya fi haka muni,” in ji shi.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Ɗan Uwan Ango Ɗaurin Aure hari Matafiya
এছাড়াও পড়ুন:
Karramawar LEADERSHIP Gare Ni, Zaburantarwa Ce Ga Ci Gaba Da Kyawawan Manufofin Mu – Gwamna Lawal
Ya ƙara da cewax gwamnatinsa ta fara gyara daga tushe, inda ilimi ya zama ginshiƙin farko. “Shekaru takwas kafin mu hau mulki, ɗalibanmu ba su samun takardun WAEC, sannan tsawon shekaru biyu suna fama da matsalar NECO. Na biya Naira Biliyan huɗu don magance wannan matsala,” inji shi.
Gwamnan ya bayyana irin matsalolin da ya gada, yana mai cewa: “Na samu asusun gwamnati da naira miliyan huɗu kacal. Ma’aikata suna karɓar albashi cikin rashin tabbas, babu ruwa, asibitoci kuwa suna cikin mummunan yanayi.”
Lawal ya ce, ya sake fasalin tsarin gwamnati, inda ya rage yawan kwamishinoni da manyan sakatarorin don rage ɓarna da ƙara inganci. “Yanzu muna daga cikin jihohi mafi ci gaba wajen tara haraji, inda kuɗaɗen shiga suka ƙaru da fiye da kaso 300 cikin 100,” inji shi.
Ya bayyana cewa gwamnatin sa ta gina ko ta gyara makarantu sama da 500, tare da aiwatar da ayyukan da kuɗinsu ya kai biliyan N10 a kowace ƙaramar hukuma. Duk da cewa ana cire biliyan 1.2 a kowane wata daga kuɗaɗen gwamnati don biyan basussuka, an biya bashin fansho da giratuti na fiye da biliyan N13.6 da aka tara tun shekarar 2011.
A ɓangaren tsaro, Lawal ya ce jihar ta ɗan sami sauƙi bayan kafa rundunar tsaron gida, yayin da gwamnati ke ƙoƙarin tabbatar da amfanin mulki ya kai ga talaka.
A nasa jawabin, Babban Editan LEADERSHIP, Azu Ishiekwene, ya ce an bai wa gwamnan wannan lambar yabo ne saboda irin nasarorin da ya samu a fannonin tsaro, ilimi, lafiya da gine-gine, yana mai cewa “jarida tana da alhakin duba gwamnati, amma kuma tana da haƙƙin yabawa idan ana yin daidai.”
ShareTweetSendShare MASU ALAKA