An kashe uban ango da ɗan uwansa a harin Filato
Published: 21st, June 2025 GMT
Mahaifin ango da ƙanin ango na daga cikin mutanen da aka kashe lokacin da wasu suka kai musu hari a Jihar Filato.
Rahotanni sun nuna cewa mutum 31 ne ke cikin wata babbar mota mai ɗaukar fasinja 18 daga Jami’ar Ahmadu Bello Zariya (ABU), yayin da aka kai musu hari.
Ɗan ƙunar baƙin wake ya kashe mutum 10 da bam a Borno An yi wa ma’aikatan ƙananan hukumomin Gombe ƙarin albashin N5,000Mutanen sun fito ne daga unguwar Basawa da ke Ƙaramar Hukumar Zariya a Jihar Kaduna, yayin da suke kan hanyarsu ta zuwa garin Pau da ke Jihar Filato domin ɗaurin aure.
Mutum 12 sun rasu a sakamakon harin, yayin da 19 suka jikkata kuma ana kula da su a Asibitin Gwamnati na Mangu.
Ɗaya daga cikin waɗanda suka tsira, Ibrahim Umar, ya ce: “Mahaifi da ƙanin ango duk sun rasu a harin.
“Angon daga Zariya yake, amma yana aiki a matsayin malami a wata makaranta a yankin. A nan ne ya haɗu da matar da zai aura.
“Muna ɗauke da goro da sauran kayayyakin da ake kai wa wajen aure. Mun shaida wa waɗanda suka tare mu cewa ba ‘yan yankin ba ne, kuma mu ba ma faɗa, sai dai ba su saurare mu ba,” in ji shi.
Ya yaba da yadda sojojin da ke kusa da wajen suka kai musu ɗauki.
“Sojojin sun taimaka mana sosai. Da ba su zo ba, da abin ya fi haka muni,” in ji shi.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Ɗan Uwan Ango Ɗaurin Aure hari Matafiya
এছাড়াও পড়ুন:
Sojoji Sun Daƙile Harin Ƴan Ta’adda, Sun Kashe 8 A Katsina
“Wannan nasarar ta nuna mahimmancin ci gaba da lura da kuma haɗin gwuiwa tsakanin Sojoji da jami’an tsaro. Ya zama dole kowa ya taka rawarsa wajen tabbatar da zaman lafiya a jihar Katsina,”
In ji kakakin birgediyar
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp