2. Haɗin kai da shugabanni daga ko’ina

3. Rashin ta’asar da ya yi wa kowa

Bayannan ƙuri’un INEC na 2023 daga jihohin Arewa maso Gabas sun nuna cewa Atiku Abubakar ya samu ƙuri’u fiye da Tinubu a dukkan jihohin yankin.

Ƙungiyar ta kammala da cewa: “Lokaci ya yi da Shugaba Tinubu ya kamata ya yi la’akari da wannan batu yayin shirye-shiryen zaɓen 2027.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Barau

এছাড়াও পড়ুন:

Mulkin Tinubu ya fi na Buhari muni — Maina Waziri

Tsohon Ministan Harkokin ’Yan Sanda, Adamu Maina Waziri, ya caccaki Shugaba Bola Ahmed Tinubu da cewa gwamnatinsa ta kere ta tsohon shugaban ƙasa Muhammadu Buhari ta fuskar muni, wanda a yanzu ƙasar tana cikin mummunan bala’i. 

Waziri, wanda jigo ne a jam’iyyar ADC (African Democratic Congress), ya bayyana haka ne a yayin wata tattaunawa da aka yi da shi a gidan talabijin na Trust TV.

’Yan gida ɗaya sun kitsa garkuwar ƙarya domin karɓar N5m a wurin mahaifinsu Sojoji sun hallaka ’yan ta’adda 17 a Borno da Adamawa

“Babu ta inda gwamnatin Tinubu ba ta gaza ba. Ta gaza a dukkan fannoni, kama daga kan tsaro, tattalin arziki, yaƙi da cin hanci saboda komai ya tabarbare. Nijeriya ta koma baya sosai a ƙarƙashin mulkinsa,” in ji shi.

Duk da ya amince an tafka kura-kurai a gwamnatin Buhari, Waziri ya ce a ganinsa Tinubu ya yi wa tsohon shugaban ƙasar fintinkau ta fuskar gazawa.

Tsohon Ministan ya bayyana cewa mulkin shugaba Tinubu ya jefa ’yan Nijeriya cikin ƙuncin rayuwa, musamman tun bayan janye tallafin mai da sauye-sauyen tattalin arziki, wanda ya janyo hauhawar farashin kaya da ƙarancin abinci.

Ya kuma soki yadda wasu ’yan siyasa ke nuna goyon baya ga gwamnatin Tinubu saboda saboda son zuciya da wani ra’ayi na ƙashin kai, yana mai cewa “wadannan mutanen su kansu suna cikin tsaka mai wuya, amma sai su riƙa yabon gwamnati saboda siyasa.”

Ya ce yana mamakin irin waɗannan mutane musamman waɗanda yankunansu ke fama da hare-haren ’yan bindiga da rashin tsaro za su riƙa fitowa a kafafen watsa labarai suna goyon bayan gwamnati, lamarin da ya bayyana a matsayin mai ɗaure kai.

“Ina mamakin yadda wasu mutane waɗanda ƙananan hukumominsu ke ƙarƙashin ikon ’yan bindiga za su iya fitowa a talabijin na ƙasa su na yabon wannan gwamnati,” in ji shi.

Waziri ya ƙara da cewa, a yanzu Nijeriya na buƙatar shugabanci nagari, wanda babu makirci da ruɗu a cikinsa, saboda haka babu wata gwamnati da ta rasa ƙima irin wannan da za ta nemi wa’adi na biyu.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Barcelona Ta Tube Ter Stergen Daga Mukaminsa Na Kaftin Din Kungiyar 
  • Amurka Ta Fara Girbar Sakamakon Kare-Karen Haraji
  • Sulhu Da ‘Yan Bindiga A Jihohin Makwabta, Ya Kara Ta’azzarar Rashin Tsaro A Neja – Bago
  • Jama’a Suke Tona Asirin Gurɓattun Jami’anmu – Kwamishinan ‘Yansandan Kano
  • Yawancin ‘Yan Siyasar Nijeriya Ba Su Da Tarbiyya – Sarki Sanusi II
  • Tinubu Ya Taya Nafisa, Rukayya, Hadiza Murnar Samun Nasarar Zama Gwanaye A Gasar Turanci Ta Duniya
  • Remi Tinubu Ta Bai Wa Waɗanda Ambaliya Ta Shafa A Neja Tallafin N1bn
  • Kasar Sin Ta Sanar Da Matakan Fara Bayar Da Ilimin Kafin Firamare Kyauta
  • Mulkin Tinubu ya fi na Buhari muni — Maina Waziri
  • Remi Tinubu Ta Bada Gudunmawar Naira Biliyan 1 Ga Wadanda Ambaliyar Ruwan Neja Ta Shafa