Aminiya:
2025-11-09@02:30:07 GMT

An tura ’yan China 6 kurkuku kan laifin ta’addanci a Nijeriya

Published: 24th, June 2025 GMT

Wata Babbar Kotun Tarayya da ke zamanta a Jihar Legas ta yi wa wasun ‘yan China shida ɗaurin shekara ɗaya bayan ta same su da laifin ta’addanci da zamba ta intanet.

Sanarwar da hukumar yaƙi da masu yi wa tattalin arziƙin Nijeriya ta’annati (EFCC) ta fitar ta ce kotun da ke unguwar Ikoyi ta Jihar Legas ce ta ɗaure mutanen ne bayan ta same su da laifi.

Sarkin Musulmi ya ba da umarnin fara duban watan Muharram Harin asibiti ya kashe mutum 40 a Sudan — WHO

“Masu laifin sun hada da : JIA You (da aka fi sani da A. You) da Wang Zheng Feng ( da aka fi sani da Feng) da Liu San Hua da Chen Wen Yuan da Liu BeiIxingda Wen Zong Xu (da aka fi sani Li Long),” in ji sanarwar.

EFCC ta ce masu laifin suna cikin mutum 792 da ake zargi da hannu a damfara ta hanyar kirifto waɗanda aka kama ranar 19 ga watan Disamba shekarar 2024 a Legas a wani samame da hukumar ta ƙaddamar mai taken “Eagle Flush Operation.”

Bayan an kama su ne aka gurfanar da su a gaban kotu kan zargin aikata ta’addanci da kuma aikata zamba ta intanet.

Sanarwar ta ambato tuhumar da aka yi wa masu laifin na shiga manhajar komfuta da gangan domin lalata tattalin arziki da zamantakewar al’ummar Nijeriya, wanda hakan ya nuna cewa ya aikata laifi da ya saɓa wa dokar hana laifukan intanet ta 2015 da kuma dokar hana ta’addanci ta 2022.

Daga farko dai waɗanda ake zargin sun musanta zargin da aka karanta musu daga takardar tuhumar.

Sai dai kuma a zaman kotun na ranar 23 ga watan Yuni sun sauya matsayarsu zuwa amsa laifi, kuma nan take lauyoyin gwamnati suka nemi kotu ta same su da laifi tare da hukunta su.

“Saboda haka, kotun ta same su da laifi tare da yi wa kowanne daga waɗanda ake tuhumar ɗaurin shekara ɗai-ɗai daga ranar 10 ga watan Disamba na shekarar 2025, da kuma cin kowanne daga cikinsu tarar naira miliyan ɗaya-ɗaya,” in ji sanarwar.

Alƙalin ya kuma ba da umarni ga shugaban hukumar kula da shige da fice ta Nijeriya ya tabbatar cewa an mayar da ’yan China ƙasar da suka fito cikin kwanani bakwai da zarar sun kammala wa’adin gidan yari.

Kazalika, kotun ta ba da umarnin cewa a sallamar da wayoyi da kamfutoci da kuma na’uororin samar da intanet da aka ƙwace daga masu laifin wa Gwamnatin Tarayyar Nijeriya.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: yan China

এছাড়াও পড়ুন:

Xi Jinping Ya Taya Paul Biya Murnar Tazarce a Kamaru

Yau 7 ga watan Nuwamba, Shugaban kasar Sin Xi Jinping ya taya Paul Biya murnar yin tazarce a wani sabon wa’adin shugabancin kasar Kamaru.

Shugaba Xi ya ce, kasar Sin da Kamaru suna da daddadiyar alaka mai kyau. A cikin ‘yan shekarun nan, amincewar siyasa tsakanin kasashen biyu ta kara zurfafawa, kuma an samu nasarori masu yawa a fannoni daban-daban na hadin gwiwa, tare da mara wa juna goyon baya a kan batutuwan da suka shafi muradunsu da kuma batutuwa masu muhimmanci.

A shekara mai zuwa ce za a cika shekaru 55 da kulla alakar diflomasiyya tsakanin kasar Sin da Kamaru, matakin da ya samar musu da sabbin damammaki na ci gaban huldarsu. Xi yana dora muhimmanci sosai kan ci gaban dangantakar Sin da Kamaru, kuma yana fatan hadin gwiwa da shugaba Paul Biya, don aiwatar da sakamakon taron kolin dandalin tattaunawar hadin gwiwa tsakanin Sin da Afirka da aka gudanar a birnin Beijing a bara, ta yadda za a inganta cikakkiyar alaka ta hadin gwiwa tsakanin kasashen biyu bisa manyan tsare-tsare masu zurfi, da kyautata rayuwar al’ummomin kasashen biyu. (Amina Xu)

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Labarai An Gano Gawar Wata Tsohuwa Mai Shekaru 96 Bayan Faɗawa Shadda A Kano November 7, 2025 Manyan Labarai Batun Kawo Harin Soja: ‘Yan Nijeriya Sun Yi Watsi Da Barazanar Trump November 7, 2025 Manyan Labarai Barazanar Amurka Na Kawo Wa Nijeriya Hari  November 7, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kasashen Afirka Bakwai Da Sojojin Amurka Suka Shiga
  • Kamfanoni Masu Jarin Waje Na Samun Kwarin Gwiwa Daga CIIE
  • Matsalar Tsaro: Mun samu gagarumin ci gaba a shekaru biyu – Tinubu
  • Matsalar Tsaro: Mun sami gagarumin ci gaba a shekaru biyu – Tinubu
  •  Tanzania: An Tuhumi Mutane Da Dama Da Laifin Cin Amanar Kasa Bayan Rikicin Zabe
  • Jerin Gwarazan Taurarinmu!
  • An Kaddamar Da Taron Kolin Wuzhen Na Ayyuka Masu Nasaba Da Yanar Gizo
  • Xi Jinping Ya Taya Paul Biya Murnar Tazarce a Kamaru
  • Barazanar Amurka Na Kawo Wa Nijeriya Hari 
  • Iran, China da Rasha sun tattauna gabanin taron Kwamitin Gwamnonin IAEA