Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp.

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Fararen hula sun yi garkuwa da sojoji 57 a Columbia

Rundunar Sojin ƙasar Columbia ta tabbatar da cewa fararen hula sun yi garkuwa da dakarunta guda 57.

Janar Federico Alberto Mejía  na Rundunar ya sanar a ranar Lahadi cewa mutane kimanin 200 sun yi garkuwa da sojojin ne bisa umarnin ’yan tawayen FARC da suka addabi ƙasar.

Ta bayyana cewa al’ummar ƙasar suna fuskantar matsin lamba daga ’yan tawayen masu ɗauke da makamai.

Sanarwar ta ƙara da cewa an sace sojoji 31 a ranar Asabar, ragowar kuma ranar Lahadi.

Erik Rodríguez ya bayyana cewa sace sojojin na da alaƙa da kama wani jagoran ’yan tawayen kungiyar EMC da sojojin suka yi.

Ya ce a yayin da suke ƙoƙarin daukar sa a jirgi ne mutanen suka yi musu ƙawanya suka yi awon gaba su a yankin Kudu maso Yammacin Micay Canyon mai tsaunuka.

Ƙungiyar ’yan tawayen FARC ta addabi yankin Kudu maso Yammacin ƙasar, wanda ya yi ƙaurin suna wajen safarar miyagun ƙwayoyi a kusa da Lardin El Plateado.

Yankin ya yi fice wajen sarrafawa da safarar horar iblis, kuma yana cikin yana daga cikin wuraren da suka fi dama da tashin-tsahina a ƙasar ta Columbia.

A baya kungiyar ta kulla yarjejeniyar zaman lafiya da gwamnatin kasar a shekarar 2016.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Al’ummun Afrika Da Sin Ba Za Su Taba Mantawa Da Gudunmuwar Tawagar Jami’an Lafiya Ta Sin Ba
  • Tinubu Ya Haƙura Da Tsayawa Takara A 2027 – Jigo A APC
  • Majalisar Dattawa Na Nazarin Shawarwari 31, Da Ƴancin Ƙananan Hukumomi
  • Likitocin Kasar Sin Sun Gudanar Da Ayyukan Kiwon Lafiya Kyauta Ga Yara A Botswana
  • Tawagar Likitocin Kasar Sin Sun Duba Marayu Marasa Lafiya Fiye Da 200 Kyauta A Zanzibar Ta Tanzaniya
  • Fararen hula sun yi garkuwa da sojoji 57 a Columbia
  • Bio ya maye gurbin Tinubu a matsayin sabon shugaban ECOWAS
  • Gwamnatin Hong Kong Ta Gudanar Da Bikin Cika Shekaru Biyar Da Kafuwar Dokar Tsaron Kasa Ta Yankin
  • Sin Ta Yi Matukar Allah Wadai Da Hare-Haren Da Amurka Ta Kaiwa Iran