‘Harin da Iran ta kai wa sansanin sojin Amurka keta haddin Qatar ne’
Published: 24th, June 2025 GMT
Gwamnatin Qatar ta yi Allah-wadai da harin da Iran ta kai kan sansanin sojin saman Amurka da ke yankin al-Udeid na kasar.
Kakakin ma’aikatar harkokin wajen ƙasar, Majed al-Ansari, ya wallafa a shafinsa na X cewa: “Mun ɗauki wannan a matsayin keta haddin Qatar da sararin samaniyarta da dokokin duniya da kuma yarjejeniyar Majalisar Dinkin Duniya.
Ya ce na’urorin kakkaɓo makamai na ƙasar sun “samu nasarar daƙile hare-haren na makamai masu linzami” kuma tuni aka janye dakarun Amurka daga sansanin tun kafin harin.
Ya ƙara da cewa “an ɗauki duka matakan da suka dace wajen tabbatar da tsaron lafiyar dakarun a sansanin, ciki har da sojojin Qatar, da dakarun ƙawance da sauransu.
“Mun tabbatar da cewa babu wanda ya rasa rai ko jikkata a harin.”
Kakakin ya ce Qatar na da damar mayar da martani “domin rama daidai da abin da aka yi mata.”
উৎস: Aminiya
এছাড়াও পড়ুন:
Amurka za ta gamu da fushinmu kan shigar wa Isra’ila yaƙinta da Iran — Houthi
’Yan tawayen Houthi na Yemen sun yi barazanar cewa Amurka za ta gamu da fushinsu muddin ta kai wa Iran hari a rikicin da ya ɓarke tsakaninta da Isra’ila.
’Yan tawayen sun ce za su kai wa jiragen ruwan Amurka hare-hare a Tekun Bahar Rum, idan har Washington ta yi kuskuren shiga yaƙin da Isra’ila ta ƙaddamar wa Iran, duk kuwa da yarjejeniya tsagaita wuta da aka cimma a baya-bayan nan.
Mahaifin Rahama Sadau ya rasu Za mu sake gina kasuwar waya ta Farm Center — AbbaA cikin wani faifan bidiyo, kakakin ’yan tawayen Houthi Yahya Saree ya bayyana cewa, muddin Amurka ta kai wa Iran hari ko kuma ta shiga cikin wannan rikici, mayankansu za su ƙaddamar da farmaki kan muradun Amurkar da suka haɗa da jiragen yaƙi da kuma jiragen dakon kaya da ke zirga-zirga a Tekun Bahar Rum.
Wannan barazana ta ’yan tawayen Houthi na zuwa ne a daidai lokacin da shugaban Amurka Donad Trump ya saka wa’adin makonni biyu domin yanke shawara a game da yiwuwar shiga rikicin da ya ɓarke tsakanin Isra’ila da Iran inda aka shiga mako na biyu suna yi wa juna ruwan bama-bamai.
Sai dai kuma tuni Amurkan ta ƙaddamar da hare-hare kan wasu cibiyoyin nukiliyar Iran kamar yadda Shugaba Donald Trump ya bayyana a daren Asabar wayewar gari Lahadi.