Aminiya:
2025-08-04@23:46:39 GMT

Jami’an tsaro sun ƙwato makamai da kama mutane 398 a Kaduna

Published: 20th, June 2025 GMT

Tawagar jami’an tsaron  haɗin gwaiwa ta musamman da Gwamnan Jihar Kaduna, Uba Sani ya kafa domin yaƙi da ayyukan ’yan daba da sace-sacen waya a jihar, ta samu nasarar ƙwato makamai tare da cafke mutane 398 da ake zargi a wurare daban-daban.

Wata sanarwa da jami’in hulɗa da jama’a na rundunar ’yan sanda (PPRO), DSP Hassan Mansir ne ya fitar, na bayyana cewa, an kai samamen ne  cikin gaggawa tare da wasu sahihan bayanan sirri.

Wani ya kashe mahaifiyarsa mai shekara 71 a Akwa Ibom Yin sulhu da ’yan bindiga dabara ce ba gazawa ba — Gwamnatin Sakkwato

Samamen ya sanya wasu da dama daga cikin masu aikata laifuka tserewa daga Jihar Kaduna saboda fargabar kama su.

Sanarwar ta kuma bayyana cewa, a cikin kwanaki tara na farko da rundunar take gudanar ayyukanta, ta kama wani mutum mai suna Mathew Adamu, wanda ya shahara wajen aikata ta’addancin cikin al’umma.

Sanarwar ta ce, rundunar ta ƙunshi rundunar ’yan sandan Najeriya ne a matsayin hukumar da ke jagorantar hukumar, tare da sojoji da Jami’an tsaron farin kaya DSS da Sibil defens da jami’an shige da fice na Najeriya da hukumar gyaran hali da hukumar hana sha da fataucin miyagun ƙwayoyi (NDLEA) da hukumar kiyaye haɗurra ta ƙasa (FRSC) da Hukumar Kwastam ta Najeriya, ciki har da hukumar ’yan banga ta Jihar Kaduna (KADVIS).

DSP Hassan ya bayyana cewa, an samu wata ƙaramar bindiga ƙirar gida daga hannun wani mutum mai suna Adamu Umar, wani fitaccen mai sayar da miyagun ƙwayoyi, wanda za a miƙa ƙararsa ga Hukumar NDLEA mai yaƙi da miyagun ƙwayoyi a Najeriya domin ci gaba da bincike da gurfanar da shi.

 

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Kwastam

এছাড়াও পড়ুন:

Kasar Iran Ko Da Zata Sake Tattaunawa Da Amurka Zata Kasance Dauke Da Makamai Cikin Shirin

Mashawarcin Ma’aikatar Harkokin Wajen Iran ya bayyana cewa: Za su koma shawarwari da Amurka ne yayin da suke dauke da makamai a hannu

Mai baiwa ministan harkokin wajen Iran shawara Sa’ed Khatibzadeh, ya jaddada cewa: Iran ba za ta sake amincewa da Amurka kan duk wata tattaunawa da za ta iya yi ba, yana mai cewa makomar yankin ba kamar yadda Amurka da Isra’ila suke zato ba.

A ziyararsa ta farko da ya kai kasar China bayan hare-haren da Amurka da yahudawan sahayoniyya suka kai kan kasar Iran a baya-bayan nan, Khatibzadeh ya yi wata fitacciyar hira da gidan talabijin na Phoenix, inda ya tattauna muhimman batutuwa da suka hada da ci gaban Shirin makamashin nukiliyar Iran, dangantakar shiyya da kasa da kasa, da makomar shawarwari, da dambaruwar yankin, da kuma yiwuwar barkewar wani babban rikici.

Khatibzadeh ya yi ishara da manufofin gwamnatocin Amurka da yahudawan sahayoniyya yana mai cewa: A kodayaushe ana samun karuwar tashin hankali, musamman ma a yayin da bangaren da ke adawa da gwamnatin Amurka da yahudawan sahayoniyya suke, Iran a kodayaushe tana neman zaman lafiya kuma ba ta kaddamar da wani yaki ba tsawon karnonin da suka gabata.

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Rahotonni Sun Bayyana Cewa; Agajin Jin kai Da Ake Wurga Ta Sama A Gaza Tamkar Digon Ruwa Ne August 4, 2025 Wa’adin Da Shugaban Amurka Ya Gindaya Na Kawo Karshen Yaki A Ukraine Ya Karato Ba Tare Da Alamun Karewarsa Ba August 4, 2025 Sojojin Somaliya Sun halaka Mayakan Kungiyar Al-Shabab Fiye Da Hamsin A Kudu Maso Yammacin Mogadishu August 4, 2025 Pakisatan: Iran Ce Madogara Ga Al-ummar Musulmi August 4, 2025 Wakilin Hukumar FAO A Iran Yace Sauyin Yanayi Ya shafi Dukkan Yankin August 4, 2025 Malamai A Najeriya Suna Goyon Bayan Iran A Yadda Take Fuskantar HKI August 4, 2025 Shugaban Kasar Lebanon Ya Yi Alkawalin Adalci Ga Wadanda Feshewar Beirut Ta Shafa August 4, 2025 Iran Ta Ce Ba Wani Ma’aikacin Hukumar IAEA A Kasar A Halin Yanzu August 4, 2025 Pezeshkian ya yaba da irin goyon bayan da Pakistan ta baiwa Iran a lokacin yaki August 4, 2025 Bloomberg: FBI ta cire sunan Trump daga Fayilolin badakalar Epstein August 4, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kasar Iran Ko Da Zata Sake Tattaunawa Da Amurka Zata Kasance Dauke Da Makamai Cikin Shirin
  • Rundunar PLA Ta Yi Sintiri A Yankin Tekun Kudancin Sin Cikin Shirin Ko Ta-Kwana
  • Makon Kiwon Lafiyar Uwa da Ɗa ya Samu Gagarumar Nasara a Karamar Hukumar Gwarzo
  • Iran Ta Ce Ba Wani Ma’aikacin Hukumar IAEA A Kasar A Halin Yanzu
  • Gwamnan Neja Ya Bada Umarnin Sake Bude Jami’ar Ibrahim Badamasi Babangida, Lapai.
  • An kama dilallan ƙwaya 28 a cikin barikin sojoji a Kaduna
  • Sojoji sun ceto malamin Jami’a da aka sace a Taraba
  • An Sake Kashe Wata Ɗalibar Jami’ar Ondo
  • Jami’ar Umaru Yar’adua ta kori ɗalibai 57 kan satar jarabawa
  • Ƴansanda Sun Ƙwato Mota Da Aka Sace, Gami Da Cafke Dillalan Ƙwayoyi A Jigawa