Jakadan Sin Dake Amurka Ya Yi Jawabi A Gun Liyafar Da Kwamitin Kasa Mai Lura Da Kasuwancin Amurka Da Sin Ya Shirya
Published: 20th, June 2025 GMT
Kwamitin kasa mai lura da kasuwancin Amurka da Sin ko USCBC, ya gudanar da liyafar murna ta shekarar 2025, a ranar Laraba 18 ga wata a birnin Washington na Amurka, liyafar da jakadan kasar Sin a Amurka Xie Feng ya halarta tare da gabatar da jawabi.
Cikin jawabin nasa jakada Xie ya ce cimma moriya da nasara tare, muhimman ginshikai ne na ci gaba mai dorewa na hadin-gwiwar Sin da Amurka ta fuskar raya tattalin arziki da kasuwanci, inda dukkan bangarorin biyu gami da duniya ke cin gajiya.
Jakadan ya kara da cewa, dangantakar Sin da Amurka na cikin wani muhimmin lokaci, kana, neman hada kai don cimma moriya tare, ko kuma nuna wa juna kiyayya, hanyoyi ne mabambanta dake gabansu. Don haka ya dace kasashen biyu su tsaya bisa jagorancin shugabanninsu kan manyan tsare-tsare, da aiwatar da muhimman ra’ayoyi iri daya da suka cimma a zahiri. Har kullum kasar Sin na nuna sahihanci amma mai kunshe da sharadi, wato kiyaye cikakken yankin kasa, gami da muradun neman ci gaba, tamkar jan layi ne da ba za a iya tsallakewa ba, yayin da girmama juna, da kiyaye zaman lafiya da samun moriya tare cikin hadin-gwiwa, suka zamo babbar ka’ida da dole a mutunta ta. (Murtala Zhang)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
Mun shirya yin sulhu da ’yan bindiga — Gwamnatin Sakkwato
Gwamnatin Jihar Sakkwato, ta bayyana cewa ta shirya zama da ’yan bindiga domin tattaunawa idan har suna da niyyar ajiye makamansu su rungumi zaman lafiya.
Wannan bayani ya fito ne daga Hadimi na Musamman kan Harkokin Tsaro na Gwamna Ahmed Aliyu, Kanal Ahmed Usman (mai ritaya).
Sojoji sun raunata shugaban ISWAP na Najeriya, Albarnawi Litar fetur za ta iya komawa N1,000 a Najeriya saboda yakin Isra’ila-Iran – MasanaHadimin ya ce gwamnatin jihar na son tattaunawa don samar da zaman lafiya fiye da ci gaba da tafka yaƙi.
Gwamnatin ta ce a tarihi, an fi samu damar warware rikice-rikice da dama ta hanyar yin sulhu, ba ta hanyar amfani da ƙarfi kaɗai ba.
Saboda haka, jihar za ta iya tattaunawa da duk ’yan bindigar da suka yi niyyar miƙa wuya su dawo cikin al’umma lafiya.
Haka kuma, gwamnatin jihar ta nuna godiya ga Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu, shugabannin rundunonin tsaro, da dukkanin jami’an tsaro da ke aiki wajen kare rayuka da dukiyoyin jama’a.
“Muna godiya matuƙa da sadaukarwarsu. Allah Ya jikan jarumanmu da suka rasu, ya bai wa iyalansu haƙuri,” in ji sanarwar.
Gwamnatin ta yaba da shirin da Gwamnatin Tarayya ke yi na tura masu gadi daji domin inganta tsaro.
Amma ta jaddada cewa dole ne a tabbatar da sahihanci da amincewar al’umma wajen ɗaukar aikin.
Ta kuma ce dole ne a sanya masu gadin daji su yi aiki ne ƙarƙashin kulawar hukumomin tsaro domin hana aikata ba daidai ba.
Sanarwar ta ƙara da cewa dole ne a tabbatar da kyakkyawar sadarwa tsakanin masu gadin daji da al’umma.
Ta ce wannan zai taimaka wajen samar da amana da goyon baya daga mutanen da ake son karewa.
Hakazalika, Gwamnatin ta jaddada cewa tana da cikakken ƙudiri wajen samar da zaman lafiya da tsaro ga kowa.
Ta ce ba za ta tsaya ko ta yi ƙasa a guiwa ba wajen tabbatar da tsaro da kwanciyar hankali a faɗin jihar.
Wannan mataki yana nuna cewa gwamnat8i na son yin haɗin gwiwa da al’umma domin samar da dawwamammen zaman lafiya.