Aminiya:
2025-06-22@00:10:07 GMT

Uba Sani ya yi jajen ’yan ɗaurin aure 12 da aka kashe a Filato

Published: 21st, June 2025 GMT

Gwamnan Jihar Kaduna, Malam Uba Sani, ya aike da saƙon ta’aziyyarsa ga iyalan matafiyan da aka kashe a garin Mangu na Jihar Filato, yayin da suke kan hanyarsu ta zuwa ɗaurin aure.

A yayin isar da saƙon a ƙauyen DanBami da ke Anguwar Rimi, a Ƙaramar Hukumar Kudan, Gwamnan ya roƙi Allah Ya gafarta wa mamatan tare da addu’a ga waɗanda suka ji rauni.

An kashe uban ango da ɗan uwansa a harin Filato Ɗan ƙunar baƙin wake ya kashe mutum 10 da bam a Borno

Gwamnan, wanda Kwamishinan ’Yan Sandan Jihar Kaduna, CP Rabi’u Muhammad, ya wakilta, ya ce gwamnati na ƙoƙarin gano waɗanda suka aikata wannan mummunan aiki.

Ya tabbatar da cewa ana ci gaba da tuntuɓar Gwamnan Jihar Filato domin ɗaukar matakan da suka dace.

An tabbatar da cewa mutum 11 daga cikin 31 da ke cikin mota sun rasu, yayin da suke kan hanyarsu ta zuwa bikin ɗaurin auren wani ɗan uwansu a Mangu.

Mutum na 12 shi ne direban motar wanda ɗan asalin garin Basawa ne.

Gwamna Uba Sani, ya ce an kama wasu mutane da ake zargi da hannu a lamarin, kuma gwamnati ba za ta yi ƙasa a gwiwa ba wajen ganin an hukunta waɗanda suka aikata wannan aika-aika.

Ya kuma roƙi al’umma, musamman matasa, da su guji ɗaukar hukunci a hannunsu, domin gwamnati na aiki kafaɗa da kafaɗa da Jihar Filato domin tabbatar da adalci.

“Na jajanta wa iyalan mamatan bisa wannan babban rashi. Ina roƙon ku da ku ɗauki wannan a matsayin ƙaddara. Mutuwa abu ne da babu makawa, kuma kowa zai fuskance ta a lokacin da Allah Ya rubuta masa,” in ji Gwamnan.

A nasa ɓangaren, Sarkin Zazzau, Malam Ahmed Nuhu Bamalli, wanda Hakimin Basawa, Haruna Abubakar, ya wakilta, ya roƙi Allah Ya jiƙan mamatan tare da bai wa iyalansu haƙuri da juriya.

Malam Musa Ibrahim, da ya yi magana a madadin iyalan mamatan da al’ummar DanBami, ya ce sun rungumi ƙaddara bisa wannan al’amari.

Sai dai ya roƙi Gwamnan da ya tallafa wa iyalan ta hanyar biyansu diyya domin rage musu raɗaɗin rashin da suka yi.

Ya ce dukkanin mamatan ‘yan garin ne kuma ‘yan uwan juna ne, direban motar ne kawai daga garin Basawa.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Ɗaurin Aure Gwamnan Kaduna hari Zariya

এছাড়াও পড়ুন:

Ƴan Ta’adda Sun Kashe Matafiya 12 A Filato 

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An kashe uban ango da ɗan uwansa a harin Filato
  • Ɗan ƙunar baƙin wake ya kashe mutum 10 da bam a Borno
  • Ƴan Ta’adda Sun Kashe Matafiya 12 A Filato 
  • Mahara sun kashe ’yan ɗaurin aure 12 daga Zariya a Filato
  • Hajjin Bana: Jihohi 11 Sun Kashe Naira Biliyan 6.2 Kan Mahajjata
  • Wani ya kashe mahaifiyarsa mai shekara 71 a Akwa Ibom
  • Rikicin Filato: An sake kashe mutum 17 a Mangu da Bokkos
  • Indomie Arewa Ta Ƙaddamar da AI Career Generator Domin Ranar Yara
  • Yadda manoma suka yi addu’ar roƙon ruwa a Zamfara