Aminiya:
2025-09-20@08:12:53 GMT

Uba Sani ya yi jajen ’yan ɗaurin aure 12 da aka kashe a Filato

Published: 21st, June 2025 GMT

Gwamnan Jihar Kaduna, Malam Uba Sani, ya aike da saƙon ta’aziyyarsa ga iyalan matafiyan da aka kashe a garin Mangu na Jihar Filato, yayin da suke kan hanyarsu ta zuwa ɗaurin aure.

A yayin isar da saƙon a ƙauyen DanBami da ke Anguwar Rimi, a Ƙaramar Hukumar Kudan, Gwamnan ya roƙi Allah Ya gafarta wa mamatan tare da addu’a ga waɗanda suka ji rauni.

An kashe uban ango da ɗan uwansa a harin Filato Ɗan ƙunar baƙin wake ya kashe mutum 10 da bam a Borno

Gwamnan, wanda Kwamishinan ’Yan Sandan Jihar Kaduna, CP Rabi’u Muhammad, ya wakilta, ya ce gwamnati na ƙoƙarin gano waɗanda suka aikata wannan mummunan aiki.

Ya tabbatar da cewa ana ci gaba da tuntuɓar Gwamnan Jihar Filato domin ɗaukar matakan da suka dace.

An tabbatar da cewa mutum 11 daga cikin 31 da ke cikin mota sun rasu, yayin da suke kan hanyarsu ta zuwa bikin ɗaurin auren wani ɗan uwansu a Mangu.

Mutum na 12 shi ne direban motar wanda ɗan asalin garin Basawa ne.

Gwamna Uba Sani, ya ce an kama wasu mutane da ake zargi da hannu a lamarin, kuma gwamnati ba za ta yi ƙasa a gwiwa ba wajen ganin an hukunta waɗanda suka aikata wannan aika-aika.

Ya kuma roƙi al’umma, musamman matasa, da su guji ɗaukar hukunci a hannunsu, domin gwamnati na aiki kafaɗa da kafaɗa da Jihar Filato domin tabbatar da adalci.

“Na jajanta wa iyalan mamatan bisa wannan babban rashi. Ina roƙon ku da ku ɗauki wannan a matsayin ƙaddara. Mutuwa abu ne da babu makawa, kuma kowa zai fuskance ta a lokacin da Allah Ya rubuta masa,” in ji Gwamnan.

A nasa ɓangaren, Sarkin Zazzau, Malam Ahmed Nuhu Bamalli, wanda Hakimin Basawa, Haruna Abubakar, ya wakilta, ya roƙi Allah Ya jiƙan mamatan tare da bai wa iyalansu haƙuri da juriya.

Malam Musa Ibrahim, da ya yi magana a madadin iyalan mamatan da al’ummar DanBami, ya ce sun rungumi ƙaddara bisa wannan al’amari.

Sai dai ya roƙi Gwamnan da ya tallafa wa iyalan ta hanyar biyansu diyya domin rage musu raɗaɗin rashin da suka yi.

Ya ce dukkanin mamatan ‘yan garin ne kuma ‘yan uwan juna ne, direban motar ne kawai daga garin Basawa.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Ɗaurin Aure Gwamnan Kaduna hari Zariya

এছাড়াও পড়ুন:

Fubara ya sauka a filin jirgin saman Fatakwal

Gwamnan Jihar Ribas, Siminalayi Fubara, ya dawo bayan shafe tsawon lokaci baya jihar biyo bayan sanya dokar ta-ɓaci da  Shugaba Tinubu ya yi.

A ranar Laraba ne Shugaba Tinubu ya janye dokar ta-ɓaci, wadda tsohon Hafsan sojan ruwa, Vice Admiral Ibok-Ekwe Ibas (rtd), ya jagoranta.

’Yan bindiga sun kai hari sakatariyar ’yan jarida ta jihar Yobe An dakatar da shugabannin sakandare 6 a Sakkwato kan zargin cin amanar aiki

Magoya bayan gwamnan sun taru a gidan gwamnatin jihar da ke Fatakwal domin tarbarsa bayan dakatar da shi na tsawon watanni shida, amma daga baya suka watse bayan shafe lokaci suna jira ba tare da ganinsa ba.

Da safiyar ranar Juma’a, magoya bayan suka koma Filin Jirgin Sama na Fatakwal.

Jirgin da ya ɗauko gwamnan ya sauka a filin da misalin ƙarfe 12 na rana.

Ya gaisa da magoya bayansa a filin jirgin kafin daga bisani ya shiga mota tare da ayarinsa suka tafi.

Babu tabbacin cewar ko gidan gwamnati ya nufa kai-tsaye domin ci gaba da gudanar da harkokin mulki.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Tinubu Ya Ziyarci Iyalan Buhari A Jihar Kaduna
  • Fubara ya sauka a filin jirgin saman Fatakwal
  • Mutum 1,666 ne suka kashe kansu a Legas cikin shekaru biyar – ’Yan sanda
  • Akasarin masu kai mana hare-hare daga jihohin da suka kewaye mu suke – Gwamnatin Filato
  • Yadda jariri ya rasu a bayan mahaifiyarsa yayin tsere wa harin ’yan bindiga a Neja
  • Mataimakin Gwamnan Zamfara Ya Jajantawa Al’ummar Gumi
  • Gobara ta kashe manyan jami’an hukumar FIRS 4 a Legas
  • Gwamnati ta ƙaddamar da jiragen ruwa na zamani 20 a Sakkwato
  • Al’ajabi: Yadda Aka Shirya Bikin Haihuwar ‘Ya’yan Awaki Biyar A Garin Dakasoye
  • Gwamna Namadi Ya Taya Malaman Makarantu Da Suka Yi Fice A Jihar Murna