Aminiya:
2025-08-06@04:43:09 GMT

Uba Sani ya yi jajen ’yan ɗaurin aure 12 da aka kashe a Filato

Published: 21st, June 2025 GMT

Gwamnan Jihar Kaduna, Malam Uba Sani, ya aike da saƙon ta’aziyyarsa ga iyalan matafiyan da aka kashe a garin Mangu na Jihar Filato, yayin da suke kan hanyarsu ta zuwa ɗaurin aure.

A yayin isar da saƙon a ƙauyen DanBami da ke Anguwar Rimi, a Ƙaramar Hukumar Kudan, Gwamnan ya roƙi Allah Ya gafarta wa mamatan tare da addu’a ga waɗanda suka ji rauni.

An kashe uban ango da ɗan uwansa a harin Filato Ɗan ƙunar baƙin wake ya kashe mutum 10 da bam a Borno

Gwamnan, wanda Kwamishinan ’Yan Sandan Jihar Kaduna, CP Rabi’u Muhammad, ya wakilta, ya ce gwamnati na ƙoƙarin gano waɗanda suka aikata wannan mummunan aiki.

Ya tabbatar da cewa ana ci gaba da tuntuɓar Gwamnan Jihar Filato domin ɗaukar matakan da suka dace.

An tabbatar da cewa mutum 11 daga cikin 31 da ke cikin mota sun rasu, yayin da suke kan hanyarsu ta zuwa bikin ɗaurin auren wani ɗan uwansu a Mangu.

Mutum na 12 shi ne direban motar wanda ɗan asalin garin Basawa ne.

Gwamna Uba Sani, ya ce an kama wasu mutane da ake zargi da hannu a lamarin, kuma gwamnati ba za ta yi ƙasa a gwiwa ba wajen ganin an hukunta waɗanda suka aikata wannan aika-aika.

Ya kuma roƙi al’umma, musamman matasa, da su guji ɗaukar hukunci a hannunsu, domin gwamnati na aiki kafaɗa da kafaɗa da Jihar Filato domin tabbatar da adalci.

“Na jajanta wa iyalan mamatan bisa wannan babban rashi. Ina roƙon ku da ku ɗauki wannan a matsayin ƙaddara. Mutuwa abu ne da babu makawa, kuma kowa zai fuskance ta a lokacin da Allah Ya rubuta masa,” in ji Gwamnan.

A nasa ɓangaren, Sarkin Zazzau, Malam Ahmed Nuhu Bamalli, wanda Hakimin Basawa, Haruna Abubakar, ya wakilta, ya roƙi Allah Ya jiƙan mamatan tare da bai wa iyalansu haƙuri da juriya.

Malam Musa Ibrahim, da ya yi magana a madadin iyalan mamatan da al’ummar DanBami, ya ce sun rungumi ƙaddara bisa wannan al’amari.

Sai dai ya roƙi Gwamnan da ya tallafa wa iyalan ta hanyar biyansu diyya domin rage musu raɗaɗin rashin da suka yi.

Ya ce dukkanin mamatan ‘yan garin ne kuma ‘yan uwan juna ne, direban motar ne kawai daga garin Basawa.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Ɗaurin Aure Gwamnan Kaduna hari Zariya

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnan Yobe ya naɗa Gadaka a matsayin sabon Sarkin Gudi

Gwamnan Jihar Yobe, Mai Mala Buni, ya amince da naɗa Hon. Ismaila Ahmed Gadaka a matsayin sabon Sarkin Gudi, bayan rasuwar Alhaji Isa Bunuwa Madugu Ibn Kaji.

Sabon Sarkin na Gudi, Ismaila Ahmed Gadaka, ya shahara da ƙwarewa a fannoni da dama.

Sojoji sun ceto malamin Jami’a da aka sace a Taraba Ma’aikatan jinya sun dakatar da yajin aiki a faɗin Najeriya

Ya taɓa zama ɗan majalisar wakilai mai wakiltar Fika/Fune daga 2011 zuwa 2019, kuma kafin nan ya yi aiki a matsayin Kwamishina a Jihar Yobe daga 2007 zuwa 2010.

Gadaka, ƙwararren ma’aikacin banki ne, inda ya yi aiki da bankuna irin su UBA da Standard Trust Bank, inda ya kai matsayin Manajan Kasuwanci.

Kafin naɗa shi Sarki, ya riƙe sarautar Yariman Gudi, a masarautar.

Yanzu haka, yana shugabantar hukumar gudanarwar Kwalejin Ilimi ta Tarayya da ke Yawuri, a Jihar Kebbi, da kuma Kwamitin Kula da Ayyukan Gwamnatin a Ƙananan hukumomin Jihar Yobe tun daga 2024.

Gwamna Buni, ya bayyana cewa yana da tabbacin sabon Sarkin zai kula da martabar masarautar Gudi, ya kuma tabbatar da zaman lafiya da haɗin kan al’umma.

Ya kuma aike da saƙon ta’aziyyarsa ga masarautar Gudi da iyalan marigayi Sarkin, tare da taya sabon Sarkin murna bisa wannan sarauta da ya samu.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gobara ta cinye gidan hakimi a Bauchi
  • Sanata Buba ya ƙaddamar da allurar rigakafin dabbobi kyauta
  • Mu daina zagin malaman addini idan muna son zaman lafiya — Uba Sani
  • Wasu Kungiyoyi Sun Yi Kira Ga Dan Majalisa Aminu Sani Jaji Ya Fito Takarar Gwamnan Zamfara 
  • Gwamnan Jihar Kwara Ya Hori Sabbin Matasa Masu Yiwa Kasa Hidima Akan Kishin Kasa
  • Gwamnatin Sakkwato Za Ta Kashe fiye da Naira Miliyan 200 Wajen Gyara Tashar Talabijin Ta Kasa NTA
  • Gwamnan Kano Ya Kaddamar da Shirin Dashen Bishiyoyi
  • Shirin kashe N712bn kan gyaran filin jirgin Legas ya tayar da ƙura
  • Gwamnan Yobe ya naɗa Gadaka a matsayin sabon Sarkin Gudi
  • Hanyoyin Da Za A Bi A Rage Yawan Zawarawa