Rahotanni sun bayyana cewa, kasashen Rasha, da Sin da Pakistan, sun gabatar da wani daftarin kudurin kwamitin sulhun MDD, kan halin da ake ciki a Iran. Game da hakan, kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin Guo Jiakun, ya shaidawa nuni taron manema labarai da aka saba yi a yau Litinin cewa, harin da Amurka ta kai kan wuraren da kasar Iran ta girke na’urorin nukiliya ya saba wa manufar tsarin dokokin MDD, tare da kara ta’azzara tashin hankali a yankin gabas ta tsakiya, don haka, dole ne kwamitin sulhun ya dauki mataki kan batun.

Kakakin ya kara da cewa, kasar Sin na sa ran mambobin kwamitin za su goyi bayan daftarin kudurin, tare da sa kaimin kwamitin ya taka muhimmiyar rawa wajen tabbatar da zaman lafiya, da tsaron kasa da kasa.

‘Yan Bindiga Sun Sace Dukkan Fasinjojin Motar Bas A Jihar Benuwe Yanzu-yanzu: Zanga-zanga Ta Ɓarke A Jami’ar Neja Bayan Kashe Ɗalibi

Dangane da goyon bayan da majalisar dokokin Iran ta nuna game da rufe mashigin tekun Hormuz, mashigin tekun Farisa, da yankin ruwan da ke kewaye da shi muhimmiyar hanyar cinikayyar kayayyaki da makamashi ce ta kasa da kasa. Kuma kasar Sin ta yi kira ga kasashen duniya da su kara kokarin sa kaimi ga kwantar da kurar rikici, don magance karin tasiri da tashin hankalin da ake fuskanta a shiyyar ka iya haifarwa ga gaban tattalin arzikin duniya.

Baya ga haka kuma, kakakin ya bayyana cewa, ‘yan kasar Sin 3,125 sun riga sun fice daga kasar Iran lami lafiya, kuma ofishin jakadancin kasar Sin dake Isra’ila, ya taimaka wa ‘yan kasar Sin sama da 500 barin Isra’ila yadda ya kamata, kana ya taimaka wa wasu ‘yan kasar Birtaniya, da Indiya, da Poland wajen barin kasar lami lafiya. (Mai fassara Bilkisu Xin)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Kasar Sin Za Ta Shirya Taron Mata Na Duniya A Beijing Yayin Cika Shekaru 30 Da Taron Mata Na 1995

Mai magana da yawun ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin Guo Jiakun ya bayyana a yau Litinin 22 ga wata cewa, nan ba da jimawa ba kasar Sin za ta gudanar da taron mata na duniya a birnin Beijing a daidai lokacin da ake cika shekaru 30 da gudanar da babban taron mata na duniya a shekarar 1995. Ya ce, kasar ta Sin tana son yin aiki kafada da kafada da dukkan kasashen duniya don kara hanzarta aiwatar da sabon tsarin ciyar da mata gaba a dukkan fannoni, da kuma rubuta wani sabon babi na raya al’amuran mata a duniya.

Guo ya ce, ta fuskar abin da aka sa gaba a duniya, akwai sauran shekaru biyar kafin a cimma muradun samar da ci gaba mai dorewa na shekarar 2030. Batun ciyar da mata gaba a duniya yana fuskantar dimbin kalubale masu tsanani yayin da kuma a lokaci guda hakan ke kawo damammaki masu yawa. A fannin inganta daidaito tsakanin jinsi da ci gaban mata a dukkan fannoni, kasar Sin ba mai neman tabbatar da hakan ne kawai ba, har ma ta kasance mai yi a aikace.

Guo ya kuma bayyana cewa, tun bayan babban taron wakilan jam’iyyar Kwaminis ta kasar Sin karo na 18, harkokin mata na kasar Sin sun samu bunkasa, da samun nasarori masu dimbin tarihi, da yin gyare-gyare a dukkan fannoni. Hanyar ci gaban mata a karkashin tsarin gurguzu mai kunshe da sigogin kasar Sin ta nuna matukar samun kuzari da fa’ida ta musamman. (Abdulrazaq Yahuza Jere)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Larijani: Iran na kare tsaron kasa da azama
  • Xi Ya Bukaci Hada Karfi Da Karfe Wajen Gina Yankin Xinjiang Ya Zama Mafi Kyau
  • Firaministan Sin Ya Isa New York Don Halartar Babban Taron Mahawara Na MDD Karo Na 80
  • CBN ya rage kuɗin ruwa zuwa kashi 27 cikin 100
  • Sin Tana Maraba Da Kwararru Daga Bangarori Daban Daban Na Kasa Da Kasa Su Zo Kasar
  • Kasar Sin Na Matukar Goyon Bayan Tabbatar Da Adalci Ga Falasdinawa Wajen Maido Da Hakkinsu Na Kasa
  • Da Ɗumi-ɗumi: Gwamnan Ribas, Fubara Ya Ziyarci Tinubu A Fadar Gwamnati A Abuja
  • Kasar Sin Za Ta Shirya Taron Mata Na Duniya A Beijing Yayin Cika Shekaru 30 Da Taron Mata Na 1995
  • Xi Jinping Ya Mika Gaisuwar “Bikin Girbi Na Manoman Kasar Sin” Na Takwas
  • Jagoran Juyin Juya Halin Musulunci Ya Jinjinawa Tawagar Kokawar Greco-Roma Ta Iran Murnar Lashe Gasar Cin Kofin Duniya