Aminiya:
2025-06-24@12:20:44 GMT

Iran da Isra’ila sun amince da tsagaita wuta —Trump

Published: 24th, June 2025 GMT

Shugaban Ƙasar Amurka Donald Trump ya ce an ƙulla yarjejeniyar tsagaita wuta gaba daya a yaƙin da ya ɓarke tsakanin Iran da Isra’ila.

Kafar yaɗa labarai ta the Guardian ta ƙasar Birtaniya ta ruwaito cewa Trump ya sanar da haka ne a shafinsa na sadar da zamunta, ’yan sa’o’i bayan hare-haren ramuwar gayya da Iran ta kai a sansanin sojin Amurka da ke ƙasar Qatar da Iran bayan hare-haren da Amirkan ta kai wa Iran.

Ya sanar cewa cikin awa shida na farko Iran za ta fara dakatar da kai hare-hare, daga bisani Isra’ila ta dakatar, wanda hakan zai kawo ƙarshen yaƙin ɗungurungum.

Sanarwar tasa na zuwa ne bayan tsohon Fira Ministan Rasha, babbar ƙawar Iran, Dimitry Medvedev na cewa ƙasashe masu ƙarfin makaman nukiliya na yi wa Iran tayin makaman nasu a yayin da yaƙin ke ƙara ƙamari.

Babu dalilin kai wa Iran farmaki — Putin Akwai ƙasashen da ke shirin bai wa Iran makaman nukiliya — Rasha

Kazalika akwai yiwuwar babbar abokiyar gaban Amurka, wato Koriya ta Kudu na shirin taimaka wa Iran gyara tashoshin nukiliyan da hare-haren Amurka da Isra’ila suka shafa, da kuma gina sababbin masana’antun ƙera makamai masu linzami masu gudun walƙilya.

Hakan na zuwa ne kuma bayan Majalisar Dokokin Iran ta amince da ƙudirin rufe mashigar tekun Hormuz, matakin da Amurka ta buƙaci China ta sa baki Iran ɗin ta janye.

A gefe guda kuma Iran ta ci gaba da ruwan rokoki a kan Isara’ila, wadda ta fara kai wa cibiyoyin nukiliyar da na harkokin soji da fararen hula hari a ranar 13 ga watan nan na Yuni.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: hare hare Iran Isra ila nukiliya

এছাড়াও পড়ুন:

Za mu ci gaba da yi wa Isra’ila luguden wuta — Shugaban Iran

Shugaban Ƙasar Iran, Masoud Pezeshkian, ya bayyana cewa ƙasarsa za ta ci gaba da mayar da martani kan hare-haren da Isra’ila ke kai mata.

Ya bayyana haka ne a lokacin da yake magana da shugaban Faransa, Emmanuel Macron, ta wayar tarho.

Uba Sani ya yi jajen ’yan ɗaurin aure 12 da aka kashe a Filato Ɗan ƙunar baƙin wake ya kashe mutum 10 da bam a Borno

Shugaba Pezeshkian ya ce Iran tana da niyyar yin haɗin gwiwa da sauran ƙasashe don amfani da makamashin nukiliya ta hanyar da ba ta da alaƙa da yaƙi, amma hakan ba yana nufin za su dakatar da inganta shirye-shiryensu na nukiliya gaba ɗaya ba.

Ya ƙara da cewa hare-haren da Isra’ila ke kai wa ƙasarsa ba za su wuce haka nan ba, domin kuwa Iran za ta riƙa mayar da martani mai zafi.

A ranar Asabar, rundunar sojin Iran ta yi gargaɗi cewa za ta kai wa Isra’ila ta hark ta jiragen ruwa.

A cewar wani kakakin rundunar sojin Iran da ya bayyana a wani bidiyo, duk ƙasar da ta tura makamai zuwa Isra’ila, kamar ta shiga yaƙi da Iran ce kai-tsaye, kuma Iran ba za ta yi ƙasa a gwiwa ba wajen kare kanta ba.

A ranar Juma’ar da ta gabata, Iran ta harba makamai masu linzami da jiragen yaƙi marasa matuƙa zuwa Isra’ila, lamarin da ya jikkata mutane aƙalla 19 a birnin Haifa da ke Arewacin Isra’ila, kamar yadda wani asibiti a yankin ya tabbatar.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Trump ya zargi Isra’ila da Iran da saɓa yarjejeniyar tsagaita wuta
  • Mun amince da tsagaita wuta da Iran —Isra’ila
  • Iran Da Isra’ila Sun Amince Su Tsagaita Wuta – Trump
  • Trump ta ce Iran da Isra’ila sun amince da tsagaita wuta bayan harin Iran kan sansanonin Amurka
  • Koriya ta Arewa za ta taimaka wa Iran gyara tashoshin nukiliyan da Amurka ta kai hari —Masani
  • Sin Ta Yi Matukar Allah Wadai Da Hare-Haren Da Amurka Ta Kaiwa Iran
  • Me Zai Faru Idan Iran Ta Datse Mashigar Hormuz Sanadiyar Hare-Haren Isra’ila?
  • Amurka ta ƙaddamar da hare-hare kan Iran
  • Za mu ci gaba da yi wa Isra’ila luguden wuta — Shugaban Iran