Aminiya:
2025-08-08@16:44:23 GMT

Iran da Isra’ila sun amince da tsagaita wuta —Trump

Published: 24th, June 2025 GMT

Shugaban Ƙasar Amurka Donald Trump ya ce an ƙulla yarjejeniyar tsagaita wuta gaba daya a yaƙin da ya ɓarke tsakanin Iran da Isra’ila.

Kafar yaɗa labarai ta the Guardian ta ƙasar Birtaniya ta ruwaito cewa Trump ya sanar da haka ne a shafinsa na sadar da zamunta, ’yan sa’o’i bayan hare-haren ramuwar gayya da Iran ta kai a sansanin sojin Amurka da ke ƙasar Qatar da Iran bayan hare-haren da Amirkan ta kai wa Iran.

Ya sanar cewa cikin awa shida na farko Iran za ta fara dakatar da kai hare-hare, daga bisani Isra’ila ta dakatar, wanda hakan zai kawo ƙarshen yaƙin ɗungurungum.

Sanarwar tasa na zuwa ne bayan tsohon Fira Ministan Rasha, babbar ƙawar Iran, Dimitry Medvedev na cewa ƙasashe masu ƙarfin makaman nukiliya na yi wa Iran tayin makaman nasu a yayin da yaƙin ke ƙara ƙamari.

Babu dalilin kai wa Iran farmaki — Putin Akwai ƙasashen da ke shirin bai wa Iran makaman nukiliya — Rasha

Kazalika akwai yiwuwar babbar abokiyar gaban Amurka, wato Koriya ta Kudu na shirin taimaka wa Iran gyara tashoshin nukiliyan da hare-haren Amurka da Isra’ila suka shafa, da kuma gina sababbin masana’antun ƙera makamai masu linzami masu gudun walƙilya.

Hakan na zuwa ne kuma bayan Majalisar Dokokin Iran ta amince da ƙudirin rufe mashigar tekun Hormuz, matakin da Amurka ta buƙaci China ta sa baki Iran ɗin ta janye.

A gefe guda kuma Iran ta ci gaba da ruwan rokoki a kan Isara’ila, wadda ta fara kai wa cibiyoyin nukiliyar da na harkokin soji da fararen hula hari a ranar 13 ga watan nan na Yuni.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: hare hare Iran Isra ila nukiliya

এছাড়াও পড়ুন:

Araqchi: Ba a kayyade wani lokacin shiga wata sabuwar tattaunawa da Amurka ba

Ministan harkokin wajen kasar Iran Abbas Araghchi ya bayyana bukatar samar da wata sabuwar hanyar yin mu’amala da hukumar kula da makamashin nukiliya ta kasa da kasa IAEA, inda ya bayyana cewa, ba a kayyade lokacin shiga wasu shawarwari da Amurka ba, ya kuma tabo batun muhimmancin dangantakar dake tsakanin Iran da kasashen Rasha, Sin da Masar.

A cikin wata sanarwa da ya aikewa gidan talabijin na Iran , Araqchi ya jaddada bukatar samar da sabon tsarin hadin gwiwa tare da hukumar kula da makamashin nukiliya ta kasa da kasa, yana mai nuni da cewa, abubuwan da suka faru wanda ya kai  ga kaiwa kasar Iran hari bisa fakewa da rahotannin siyasa na  huumar IAEA, yasa dole ne Iran ta sake sabon salon a mu’amala ada wannan  hukuma.

Araghchi ya bayyana cewa, Tehran ta gayyaci mataimakin babban daraktan hukumar ta IAEA domin tattaunawa kan sabon tsarin dangantakarsu, yana mai jaddada cewa ziyarar ko alama ba za ta hada da duba cibiyoyin nukiliyar Iran ba, yana mai ishara da cewa Iran ba za ta mika kai bori ya hau ba.

Dangane da batun komawa kan teburin tattaunawa da Amurka  kuwa, Araghchi ya bayyana cewa, hakan ya dogara ne da muradu da maslaha ta kasar Iran, yana mai jaddada cewa, tattaunawar wani makami ne kawai na kiyaye muradun al’ummar Iran wajen mu’amala da Amurka.

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Ghana: Ministocin tsaro da muhalli sun rasa rayukansu a hatsarin jirgi mai saukar ungulu August 7, 2025 Jamus: Shahararrun mutane fiye da 160 da ‘yan jarida sun bukaci a daina baiwa Israila makamai August 7, 2025 Gaza: Fararen hula 22 sun yi shahada a hare-haren Isra’ila a daren jiya August 7, 2025 Pezeshkian Ya Jaddada Wajabcin Haduwar Kasashen Musulmi Wajen Hana Laifukan Yaki A Gaza August 6, 2025 Araqchi Ya Taya Larijani Murnar Zama Sakataren Majalisar Kolin Tsaron Kasar Iran August 6, 2025 Japan: An Fara Juyayin Cikar Shekaru 80 Da Harin Amurka Na Makamin Nukiliya A Hiroshima August 6, 2025 Sudan: Dakarun RSF Sun Kashe Fararen Hula 14 Tare Da Jikkata Wasu Na Daban August 6, 2025 IRGC: Bayan yakin Kwanaki 12 Yanayi Ya Sauya Zuwa Ga Amfani Ga Iran August 6, 2025 ‘Yansanda A Iran Suna Amfani Da Kayakin Tsaro Na Zamani A Lokacin 40 August 6, 2025 Iran tana Goyon Bayan Zaman Lafiya Tsakanun Kasashen Yankin August 6, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Axios: Majalisar ministocin Isra’ila ta amince da sabon shiri na mamaye birnin Gaza
  • Zamfarawa sun yi zanga-zanga kan hare-haren ’yan bindiga
  • Hare-Haren Sojojin Mamayar Isra’ila Kan Gaza Sun Janyo Shahadan Falasdinawa Masu Yawa
  • Human Rights Watch Ta Ce: Sojojin Mamayar Isra’ila Sun Rusa Makarantu Fiye Da 500 A Gaza
  • Yadda sabbin takunkuman Trump za su shafi tattalin arziƙin duniya
  • Araqchi: Ba a kayyade wani lokacin shiga wata sabuwar tattaunawa da Amurka ba
  • Gaza: Fararen hula 22 sun yi shahada a hare-haren Isra’ila a daren jiya
  • Sin Ya Yi Kira Ga Isra’ila Da Ta Dakatar Da Aiwatar Da Mataki Mai Hadari A Zirin Gaza
  • IRGC: Bayan yakin Kwanaki 12 Yanayi Ya Sauya Zuwa Ga Amfani Ga Iran
  • Hare-haren Boko Haram Da ‘Yan Bindiga Ya Ragu A Cikin Shekaru Biyu – Ribadu