Leadership News Hausa:
2025-11-08@20:36:57 GMT

Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (6)

Published: 20th, June 2025 GMT

Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (6)

Kazalika, dalibai su kasance suna iya yin bayani a kan abin da suka fahimta na abin da aka koya musu, sannan su rika bayar da shawarwari, su kasance za su iya yin wani abu ta kirkira, su yi mu’amala da wasu ba tare da wata matsala ba, su ba da hadin kai, su kasance suna iya yin abin da ake so su yi.

Idan har aka samu damar magance wadannan matsaloli da aka ambata a sama tare kuma da tabbatar hanyoyin da ake bi koyarwa, ta haka za a iya samun gyaran da ake bukata.

 

Bankin duniya a shekarar (2019) ya ce, ana fara samun sauyi ne daga Malaman makaranta; wadanda suka san abin da suke yi da kuma irin salon da ake amfani da shi wajen koyarwa. Bugu da kari kuma, ya kamata masana ilimi su yi amfani da irin ci gaban da fasaha ta kawo a wannan fanni na koyarwa.

Wasu Abubuwa Da Suka Shafi Ilimi A Duniya 

Kashi 88 na yara mata da kuma kashi 91 na yara maza, suna da ilimin Firamare, sai dai kuma mata da dama na samun ilimi mai zurfi fiye da maza, (World Economic Forum, 2019). 

A shekarar 2020, yawancin wadanda suka kammala karatun Firamare a fadin duniya baki-daya, kashi  90.14 cikin 100 ne, (UNESCO, 2021e). 

A cikin shekarar, an samu raguwar wadanda suka kammala karatun Sakandaren da kashi 77 cikin 100, (UNESCO, 2021d).

Haka nan ma, wadanda suka yi makarantar yaki da jahilci ‘yan shekara 15 da wadanda suka haura haka, kashi 86 ne cikin 100, (UNESCO, 2021c).

Wadanda suka yi yaki da jahilci ‘yan shekara 15 da wadanda suka haura haka, sun zarce kashi 83.3 cikin 100, yayin da su kuma maza suka kasance kashi 90 cikin 100, (UNESCO, 2021a; UNESCO, 2021b).

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: wadanda suka

এছাড়াও পড়ুন:

Zaben Kananan Hukumomi A Neja Ya Bar Baya Da Kura

“A yayin da ake tarwatsa masu kai harin, DPO na Sassan A da B sun tura ma’aikatansu suka harba hayaki mai sa hawaye, amma wasu motoci cikin motar gwamnan sun lalace,” in ji Abiodun.

Ya bayyana cewa mutane uku na farko da ake zargi sune Ali Mohammed da Adamu Hussain, dukkansu daga yankin Nasarafu, Bida, da Isah Umaru na yankin Darachita, Bida. Ya kara da cewa an kama Nagenu, mai shekaru 39, daga yankin Bello Masaba, daga baya dangane da wannan lamari, sannan ya ambaci wasu biyu, Salihu Mohammed da Abdulrahman Baba, yayin tambayoyi.

“Dukkan wadanda ake zargi suna karkashin bincike kuma suna taimaka wa ‘yansanda wajen gano wasu. Ana ci gaba da kokarin kama karin mutane da ake zargi,” in ji Abiodun.

Lauyan Nagenu, Barrister Ibrahim Wali, ya kuma tabbatar da kama abokin aikinsa ga *Daily Trust*, yana cewa ana tsare da shi a Ofishin Rundunar ‘Yan Sanda na Yanki a Bida. Ya bayyana cewa kama shi na da alaka da bidiyon da ya bazu, kuma ana daukar matakan shari’a don samun ‘yancinsa.

Kokarin tuntubar jami’an NNPP bai samu nasara ba. Kiran da aka yi ga shugaban jam’iyyar na jihar, Danladi Umar Abdulhamid, bai yi nasara ba, kuma bai amsa sakonnin da aka tura masa ba.

Gwamnatin Neja ta yi alkawarin gurfanar da masu laifi a gaban shari’a

Babban Mataimakin Musamman ga Gwamna kan Tattara Matasa, Hamza Bida, ya yi alkawarin cewa gwamnatin jihar za ta tabbatar an hukunta wadanda suka yi wannan hari.

Yayin da yake magana da Daza TB, wata kafar yada labar ta Hausa, ya ce wannan lamari ba shi da alaka da zaben kananan hukumomi.

“Ban ji dadi da abin da wadannan yara suka yi a Bida ba. Abin da ya faru shi ne, a rana daya kafin zaben, mutane sun taru a gidan gwamna kuma ya yi musu alkawarin ba su kudi a ranar Lahadi. Daga baya daren nan, an kafa wani kwamitin, ciki har da dan majalisar wakilai na Bida/Gbako/Katcha, don tabbatar da cewa kudin ya isa ga kowa,” in ji Bida.

Ya kara da cewa wasu matasa, wadanda ba su gamsu da tsarin ba, suka rikide zuwa tashin hankali. “Wadanda suka yi wannan aikatawa yara ne da iyayensu suka rasa ikon kula da su, amma za mu koya musu darasi,” in ji shi.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Labarai Gwamnatin Zamfara Ta Ɗauki Malaman Makaranta 500 Aiki November 7, 2025 Labarai Majalisar Wakilai Ta Yi Tir Da Harin Da Aka Kai Wa Tawagar Ɗan Majalisar Neja November 7, 2025 Manyan Labarai Hajjin 2026: NAHCON Ta Kammala Tantance Masaukai Da Ɗakunan Dafa Abincin Alhazai A Madinah November 7, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kasashen Afirka Bakwai Da Sojojin Amurka Suka Shiga
  • Kamfanoni Masu Jarin Waje Na Samun Kwarin Gwiwa Daga CIIE
  • Lalacewar Tarbiyar Dalibai Mata A Makarantun Islamiyya Da Na Boko
  • NELFUND Ta Ce Dalibai Miliyan Daya Ne Suka Nemi Tallafin Kudin Karatu
  • Matsalar Tsaro: Yadda Dabarun Uba Sani Suka Mayar Da Tsoro Zuwa Kyakkyawar Fata A Jihar Kaduna
  • Abin Da APC Za Ta Yi Da Rinjayen Kashi Biyu Bisa Uku A Majalisar Tarayya
  • Yadda PDP Ta Yi Asarar Kudancin Kaduna
  • Zaben Kananan Hukumomi A Neja Ya Bar Baya Da Kura
  • Yadda Duniya Ta Fara Wayewa Tun Daga Zamanin Annabi Nuhu (AS) Har Manzon Allah (SAW) Ya Zo Ya Cika Komai (2)
  • Mao Ning: Harka Da Kasar Sin Mabudi Ne Na Samun Damammaki