Gwamnatin Zamfara Ta Ƙaryata Rahoton Karɓo Lamuni Da Wata Jarida Ta Yaɗa
Published: 25th, June 2025 GMT
Sanarwar ta ƙara da cewa, aikin Sahara ba wai kawai aikin jaridar bogi ba ne; ya samo asali ne zuwa da suna ‘Gonzo’, wanda ke da alaƙa da ƙarairayi wajen bayar da rahoto.
Sanarwar ta ci gaba da cewa: “An ja hankalinmu kan labaran ƙarya da Sahara Reporters ke yaɗawa, shafin da ya shahara wajen yaɗa labaran ƙarya domin tayar da ƙura a intanet.
“A yayin tattaunawa da manema labarai kai tsaye a makon da ya gabata, Gwamna Dauda Lawal ya bayyana ƙudirinsa na ɗaukar nauyin kasafin kuɗi, inda ya tabbatar da cewa bai karbi lamuni na cikin gida ko na ƙasashen waje ba tsawon shekaru biyu da ya yi yana mulki.
“Amma abin ya ba mu mamaki, manyan jami’an yaɗa labaran ƙarya, Sahara Reporters, sun wallafa abin da suka sanya a matsayin wani rahoto na musamman na yadda aka karbi rancen Naira Biliyan 34 a ƙarƙashin kulawar Gwamna Lawal.
“Rahoton na Sahara ya bayyana ƙarara irin gazawar su wajen neman ƙwararan bayanai tare da yin nazari kan takardar kasafin kuɗin jihar Zamfara.
“Rahoton lamuni na naira biliyan 34 da Sahara Reporters ta yaɗa na buƙatar ƙarin haske domin tabbatar da cewa jama’a sun fahimci gaskiyar lamarin.
“An shirya Kasafin Kuɗi na 2023 ne a zamanin gwamnatin Bello Matawalle, wanda a yanzu shi ne Ƙaramin Ministan Tsaro, daga cikin kasafin kuɗin, an ware biliyan 53.2 domin kula da lamuni da gwamnatin jihar ta karbo.
“Duk da cewa ba a samu lamuni a wannan adadi na sama ba, gwamnatin jihar Zamfara ta kashe biliyan 34 wajen biyan kuɗin ruwa na rance daban-daban da gwamnatocin baya suka karba, hakan ya nuna yadda Dauda Lawal ya jajirce wajen rage yawan bashin da ake bin Zamfara da kuma hana karbar ƙarin lamuni.
“Duk dandali da ya ƙuduri aniyar yin aikin jarida na gaskiya zai gudanar da cikakken bincike don tabbatar da hasashensa da kuma tabbatar da sahihancin sa, amma Sahara Reporters ta zabi wata hanya ta daban, ta tsaya kan tsarin aikin jaridar bogi.
“Ya kamata Sahara Reporters ta tambayi tsohon Gwamna Bello Matawalle kan yadda ya yi amfani da lamunin da ya karba a zamaninsa, wanda hakan bai haifar da wani ci gaba ba, rancen da muke biya kenan.
“Gwamna Dauda Lawal bai karbi rance ba tsawon shekaru biyu da ya yi yana Gwamnan jihar Zamfara.
“Muna ƙalubalantar Sahara Reporters da su samar da duk wasu takardun da ke nuna gwamnatin Zamfara mai ci na neman lamuni, ko a cikin gida ko kuma a waje.”
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: Sahara Reporters tabbatar da
এছাড়াও পড়ুন:
Uwargidar Gwamnan Katsina Ta Nemi A Taimaka Wa Mata Wajen Yaƙi Da Ciwon Nono Da Na Mahaifa
A jawabin da Shugaban Jami’ar ABU, Farfesa Adamu Ahmed, ya yi ta bakin mataimakinsa, Farfesa Sanusi Rafindadi, ya yaba da yadda taron ke taimakawa wajen wayar da kai game da wannan cuta mai hatsari.
Ya kuma gode wa Hajiya Fatima bisa amsa gayyatar jagorantar taron.
Shugabar Sashen Kula da Mata, Farfesa Rahanatu Lawal, ta jaddada buƙatar haɗin kan kowa da kowa wajen yaƙi da cutar.
Ta ce mata ba za su iya wannan yaƙi su kaɗai ba, dole ne maza su ba su goyon baya.
Daga cikin waɗanda suka gabatar da jawabi akwai Dakta Aminat Jimoh daga Asibitin Koyarwa na ABU.
Ta buƙaci mata da su riƙa duba kansu akai-akai, musamman idan suna da tarihin ciwon a cikin danginsu.
Ta kuma roƙi Hajiya Fatima ta taimaka wajen sauƙaƙa wahalar samun magani da mata ke fuskanta.
Wata ‘yar kasuwa, Hajiya Rabi Kabiru, ta buƙaci mata da su riƙa dogaro da kansu ta hanyar sana’o’i domin hakan zai taimaka musu wajen kula da lafiyar kansu da ta iyalansu.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp