Aminiya:
2025-06-22@20:35:27 GMT

’Yan bindiga sun sace babban alƙali a Bayelsa 

Published: 22nd, June 2025 GMT

Wasu mutane da ake zargin masu garkuwa da mutane ne sun sace Alƙalin Babbar Kotun Jihar Bayelsa, Ebiyerin Omukoro.

Lamarin ya faru da misalin ƙarfe 7 na daren ranar Asabar a unguwar Ekeki, kusa da babban titin Melford Okilo a Yenagoa, babban birnin jihar.

Gwamnonin Arewa sun yi Allah-wadai da kisan ’yan ɗaurin aure a Filato HOTUNA: Yadda aka yi jana’izar ’yan ɗaurin auren da aka kashe a Filato

Rahotanni sun bayyana cewa, mutanen sun isa a cikin mota ƙirar Hilux, sanye da baƙaƙen kaya.

Jaridar Aminiya ta ruwaito cewa, maharsn sun kutsa kai gidan cin abincin da alƙalin ke ciki kuma suka tilasta masa shiga motarsu.

Har zuwa yanzu, ba a san inda suka kai shi ba, kuma babu wani saƙo ko buƙatar kuɗin fansa daga masu garkuwar.

Hakazalika ba a san dalilin da ya sa suka sace shi ba.

Wannan ba shi ne karon farko da aka sace mutum a yankin ba, domin an je har gida an sace wani ɗan jarida mai suna Oyins Egrenbido.

Wasu hotuna da bidiyo da suka karaɗe shafukan sada zumunta sun nuna yadda aka kama alƙalin tare da jefa shi cikin motar ƙirar Hilux.

Har yanzu Rundunar ’Yan Sandan Jihar Bayelsa, ba ta fitar da wata sanarwa ba dangane da sace alƙalin.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Bayelsa mahara

এছাড়াও পড়ুন:

Matsalolin Rayuwa: Matasan Suleja Na Buƙatar Ƙarfafa Gwuiwa

A can ne na hadu da wani matashi mai hazaka da kwazo, Faisal Ibrahim Abdullahi, wanda ya shaida min cewa; ya je Jihar Legas ne domin koyon fasahar ‘Epody Resin’, wato kera kayan ado da kayan daki na zamani da ake yi da sinadaran resin. Har yanzu, shi ne kadai daga yankinmu da ya mallaki wannan fasaha. Amma yana da burin koyar da sauran matasa muddin aka tallafa masa.

Na tsaya ina kallon kayan da ya nuna min na daki da ado, wanda na dauka cewa; ana yin su ne daga kasashen waje. Sai na ji cewa, “toh, dama a Suleja ake wannan?” Gaskiya wannan irin kwazo yana da bukatar tallafi, ba yabo kadai ba.

Bayan haka, taron ya kunshi gasa da horo a harkokin kasuwanci ta yanar gizo, inda matasa da dama suka samu kyaututtuka masu daraja daga ciki har da wata budurwa mai suna Blessing Paul da ta lashe kyautar mota da wasu da suka samu kyautar kudi.

Amma abin da ya dada daga min hankali shi ne, yadda galibin matasan da ke cin moriyar wannan dandali ba ’yan asalin Suleja ba ne. Wadanda suka fi mayar da hankali su ne daga wasu jihohi, suna rungumar dama da hannuwa biyu. Amma mu dai har yanzu muna ganin wadannan matasa kamar ‘yan damfara ne.

Wasu daga cikin masu rike da madafun iko ma sun yi watsi da gayyatarsu, idan ban da Mataimakin Shugaban karamar Hukumar Suleja da na Shiroro. Wasu daga cikin manyan sun yi wa su Coach Naseer mumunar fahimta, har suna yi musu kallon ‘Yahoo boys’ ne.

Ina ganin lokaci ya yi da za mu farka daga barci. Wadannan matasa suna kokari ne wajen gyara rayuwarsu ba tare da aikata laifi ba. Wajibi ne shugabanni da masu hannu da shuni da kuma masu zurfin tunani su rungumi irin wannan dandali, domin amfanin kowa da kowa.

Ga wasu daga cikin fa’idojin wannan dandalin talla na yanar gizo (affiliate marketing):

1- karfafa Matasa: Yana koya musu dogaro da kai da kuma dabarun kasuwanci.

2- Rage Aikata Laifuka: Matashin da ke da abin yi ba zai shiga yin shaye-shaye ko damfara ba.

3- Ci Gaban Al’umma: Nasarar mutum daya tana karfafa gwiwar wasu.

4- Samar Da Arziki: Wasu matasan da ke amfani da wannan dandali sun fara daukar ma’aikata, domin hannunsu ya fara maikon shuni.

5- Shiga Duniya: Matasanmu na iya fafatawa da sauran kasashen duniya daga cikin gida.

Don haka, ina kira ga Shuwagabannin Jihar Neja da na Suleja, ’yan kasuwa, manyan malamai da shugabannin gargajiya, da su bayar da goyon baya ga irin wannan yunkuri. Wannan dama ce ta fita daga kangin dogaro da gwamnati da kuma sauya tunanin cewa; dole sai an yi bariki ko kuma damfara kafin a samu kudi.

Haka zalika, kuna iya tallafa wa Faisal; domin ya koyar da matasa. Kuna kuma iya bayar da kayan aiki ko kudin horo. Amma mafi muhimmanci shi ne, ba su karfin gwiwa.

A nan ne, zan yi kira ga adali, manomin Gwamnan Jihar Neja; da ya bude wa wannan matashi kofar masana’antar Ladi Kwali, domin koyar da matasa wannan fasaha.

Yanzu duniya ta koma ta yanar gizo, wanda bai da fasahar zamani; kamar wanda bai iya karatu ba ne. Muna da zabi: mu goyi bayan irin su Coach Naseer da Faisal, ko kuma mu ci gaba da zargin su har su bar mu su tafi su samu nasara a inda ake mutunta fasaha irin tasu.

Daga Suleja nake kawo muku wannan labari mai dadi. Labarin harsashen nasara, ci gaba da inganci da ke kusa da mu, sai dai kash! Yawancinmu, ba ma ganin abin a haka.

Mu tashi tsaye. Mu goyi bayan kwazon matasanmu, kafin lokaci ya kure mana, ko wani ya zo ya amfana da su, mu kuma mu zauna muna ta faman korafi maras amfani.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Mun Gano Wurare 52 Da Ake Aikata Laifuka A Kano – Janar Mai Adda’u
  • Gwamnonin Arewa sun yi Allah-wadai da kisan ’yan ɗaurin aure a Filato
  • Matsalolin Rayuwa: Matasan Suleja Na Buƙatar Ƙarfafa Gwuiwa
  • Babban Al’amari Ne A Samu Ƴar Shekara 6 Ta Haddace Qur’ani A Makarantar Raudatul Jannah – Mai Sikeli
  • Yin sulhu da ’yan bindiga dabara ce ba gazawa ba — Gwamnatin Sakkwato
  • Ba Tsoro Ne Yasa Muka Amince Da Sulhu Da Ƴan Bindiga Ba – Gwamnatin Sokoto
  • Ƴan Bindiga Sun Kai Hari Filato, Mutane 15 Sun Mutu A Bokkos Da Mangu
  • 2027: ‘Sai bayan babban taron APC Tinubu zai bayyana wanda za su yi takara tare’
  • Bikin Ranar Muhalli Ta Duniya: Akwai Babban Aiki A Gaban Nijeriya