Aminiya:
2025-09-24@11:19:54 GMT

’Yan bindiga sun sace babban alƙali a Bayelsa 

Published: 22nd, June 2025 GMT

Wasu mutane da ake zargin masu garkuwa da mutane ne sun sace Alƙalin Babbar Kotun Jihar Bayelsa, Ebiyerin Omukoro.

Lamarin ya faru da misalin ƙarfe 7 na daren ranar Asabar a unguwar Ekeki, kusa da babban titin Melford Okilo a Yenagoa, babban birnin jihar.

Gwamnonin Arewa sun yi Allah-wadai da kisan ’yan ɗaurin aure a Filato HOTUNA: Yadda aka yi jana’izar ’yan ɗaurin auren da aka kashe a Filato

Rahotanni sun bayyana cewa, mutanen sun isa a cikin mota ƙirar Hilux, sanye da baƙaƙen kaya.

Jaridar Aminiya ta ruwaito cewa, maharsn sun kutsa kai gidan cin abincin da alƙalin ke ciki kuma suka tilasta masa shiga motarsu.

Har zuwa yanzu, ba a san inda suka kai shi ba, kuma babu wani saƙo ko buƙatar kuɗin fansa daga masu garkuwar.

Hakazalika ba a san dalilin da ya sa suka sace shi ba.

Wannan ba shi ne karon farko da aka sace mutum a yankin ba, domin an je har gida an sace wani ɗan jarida mai suna Oyins Egrenbido.

Wasu hotuna da bidiyo da suka karaɗe shafukan sada zumunta sun nuna yadda aka kama alƙalin tare da jefa shi cikin motar ƙirar Hilux.

Har yanzu Rundunar ’Yan Sandan Jihar Bayelsa, ba ta fitar da wata sanarwa ba dangane da sace alƙalin.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Bayelsa mahara

এছাড়াও পড়ুন:

An Cafke Wani Magidanci Da Lafin Sojan Gona A Katsina

“A yayin binciken motar, an samu waɗannan abubuwa daga hannun wanda ake zargin: bindiga ta gida guda ɗaya, harsashi guda huɗu, harsashi biyu da aka harba a baya, katin shaida na ƴ an sanda na bogi, da kuma ƙarin lambar rijistar mota ta (Kano FGE 68).”

“Wanda ake zargin yana tsare a hannun jami’an tsaro yayin da ake ci gaba da gudanar da bincike don gano ainihin dalilan mallakar bindiga, katin shaida na bogi, da sauran abubuwan da aka kama daga gare shi.”

“Ƙungiyar jami’an tsaro, bisa ƙarin lura da dabarun tsaron zamani, ta dakatar da wani motar Toyota Corolla, launin toka, mai lambar rijista Lagos GGE 473 BH, wanda wanda ake zargi ya ke tukawa. Bayan an yi masa tambayoyi, bai iya bayar da cikakken bayani kan kansa ko motar ba, lamarin da ya sa aka gudanar da bincike nan take.

“A yayin binciken motar, an samu waɗannan abubuwa daga hannun wanda ake zargin: bindiga ta gida guda ɗaya, harsashi guda huɗu, harsashi biyu da aka harba a baya, katin shaida na ƴ an sanda na bogi, da kuma lambar rijista ta ƙari (Kano FGE 68).”

“Wanda ake zargin yana tsare a hannun jami’an tsaro yayin da ake ci gaba da gudanar da bincike don gano ainihin dalilan mallakar bindiga, katin shaida na bogi, da sauran abubuwan da aka kama daga gare shi.”

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Firaministan Sin Ya Isa New York Don Halartar Babban Taron Mahawara Na MDD Karo Na 80
  • Jihar Kogi Na Cikin Fargaba Yayin Da Kogin Neja Da Benuwe Suka Tumfatsa
  • Yarima Salman ya jagoranci jana’izar babban mai ba da fatawa na Saudiyya
  • ‘Yan Bindiga Sun Sace Ɗan Majalisar Dokokin Jihar Filato
  • NAJERIYA A YAU: Abin Da Doka Ya Ce Kan Kisan Jami’an ‘Yan Sanda
  • Jariri ya mutu a bayan uwarsa yayin tsere wa ’yan bindiga a Neja
  • Ƴan Bindiga Sun Sace Basarake Da Mata 2 A Filato
  • Karin ƙananan hukumomi 2 sun yi sulhu da ’yan bindiga a Katsina
  • Nan Ba Da Jimawa Ba Hauhawar Farashin Kayayyaki Za Ta Zama Tarihi —Fadar Shugaban Ƙasa
  • An Cafke Wani Magidanci Da Lafin Sojan Gona A Katsina