Barau ya nesanta kansa daga masu nema masa kujerar mataimakin Tinubu a 2027
Published: 25th, June 2025 GMT
Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Barau I. Jibrin, ya nesanta kansa daga wata kungiya da take fafutukar ganin Shugaban Kasa Bola Tinubu ya dauke shi a matsayin mataimakinsa a 2027.
Mai magana da yawun Sanatan, Isma’il Mudashir ne ya bayyana hakan a cikin wata sanarwa ranar Talata, inda ya ce a maimakon haka, kamata ya yi kungiyar ta fi mayar da hankali wajen mara wa Tinubu baya ya samu nasarar yunkurinsa na bunkasa Najeriya.
A kwanan nan ne dai wata kungiya mai suna Zauren Matasan APC na Arewacin Najeriya (NNPYA) ta ayyana goyon bayanta ga Tinubu ya dauki Sanatan a matsayin wanda za su yi takara tare.
Gwamnatin Nijeriya ta yi wa Amurka martani kan barazanar tsaro a Abuja Mali ta ƙulla yarjejeniyar nukiliya da RashaHakan dai ya biyo bayan jita-jitar da ake ta yadawa a ’yan kwanakin nan cewa ba lallai ne Tinubun ya sake yin takara tare da Kashim Shettima a matsayin mataimakinsa a 2027 din ba.
A cewar Sanata Barau, “An jawo hankalina kan wasu rubuc-rubuce a shafukan sada zumunta da ma wasu jaridu na wasu kungiyoyi, cikinsu har da NNPYA, inda suke kiran jagoranmu, Shugaba Bola Tinubu, da ya dauke ni a matsayin mataimaki a 2027. Wannan ba da yawuna ba ne kuma ba shi ne abu mafi muhimmanci ba a yanzu.
“Ina kira ga NNPYA da ma sauran kungiyoyin da ke wannan fafutukar da su daina daga yanzu, sannan su mayar da hankalinsu wajen goyon bayan yunkurin Shugaba Tinubu na magance matsalolin da ke addabar kasarmu.
“Kamata ya yi mu hada karfi da karfe wajen goyon bayan Tinubu har ya samu ya kai Najeriya tudun mun tsira.
“Yanzu ba lokaci ne da za mu rika wannan kiraye-kirayen ba, lokaci ne na tabbatar da cewa Tinubu ya samu nasarar sauke nauyin da ke wuyansa.
“Ya damu kwarai da gaske wajen ganin Najeriya ta samu ci gaba. Saboda haka nake kira da kowa ya goya masa baya kan kudurorinsa da tuni aka fara ganin amfaninsu a kasa,” in ji Sanata Barau.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Barau
এছাড়াও পড়ুন:
Shugaban Najeriya Bola Tinubu Ya yi Alwashin Kawo Karshen Ta’addanci A Kasar
Shugaban Najeriya Bola Tinubu ya ce gwamnatinsa na tattaunawa da sauran ƙasashen duniya “ta hanyar difilomasiyya” game da matsalolin tsaron da ƙasar ke fuskanta a yanzu.
Kalaman shugaban na zuwa ne bayan da Shugaban Amurka Donald Trump ke barazanar kutsawa Najeriyar domin kai wa ‘yan bindiga hare-hare bayan ya zargin gwamnatin Tinubu da ƙyale su suna “yi wa Kiristoci kisan gilla”
Da yake magana yayin zaman majalisar ministocinsa a jiya Alhamis, Tinubu ya tabbatar wa ‘yan Najeriya cewa gwamnatinsa za ta kawo karshen”ta’addanci”.
“Duk da kalubalen irin na siyasa da fargabar da mutanenmu ke ciki, muna ci gaba da tattaunawa da kawayenmu, muna tattaunawa a difilomasiyyance,”
“Ina tabbatar muku cewa za mu kawo karshen ta’addanci. Abin da muka saka a gaba shi ne cigaba da ayyuka ido bude bisa manufarmu ta Sabunta Fata [Renewed Hope] domin gina Najeriya mai yalwa.”
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Araqchi Ya Ce: Harin Amurka Kan Kasar Venezuela Ya Bayyana Karara Duniya Tana Gani November 6, 2025 Qalibaf: Iran Da Pakistan Zasu Aiwatar Dukkan Yarjejeniyar Da Suka Cimma A Tsakaninsu November 6, 2025 Kwamitin Tsaro Ya Ce: Amurka Ta Bukaci Duba Kudurin Neman Kafa Rundunar Kasa Da Kasa A Gaza November 6, 2025 Sojojin Mamayar Isra’ila Sun Kashe Mutum Guda Tare Da Jikkata Wasu Uku A Kudancin Lebanon November 6, 2025 Sayyid Muqtada al-Sadr Ya Fadakar Da Magoya Bayansa Kwanaki Kafin Zabe A Iraki November 6, 2025 Araghchi : Yakin kwanaki 12 ya bamu babban darasi November 6, 2025 Putin : zamu dauki mataki idan Amurka ta koma gwajin makaman nukiliya November 6, 2025 Iran, China da Rasha sun tattauna gabanin taron Gwamnonin IAEA November 6, 2025 Shugabannin Iran Da Faransa Sun Yi Wata Tattaunawa Ta Wayar Tarho November 6, 2025 Najeriya Ta Sake Yin Watsi Da Zargin Take Hakkin Kiristoci A Kasar November 6, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci