Aminiya:
2025-08-10@09:32:00 GMT

Barau ya nesanta kansa daga masu nema masa kujerar mataimakin Tinubu a 2027

Published: 25th, June 2025 GMT

Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Barau I. Jibrin, ya nesanta kansa daga wata kungiya da take fafutukar ganin Shugaban Kasa Bola Tinubu ya dauke shi a matsayin mataimakinsa a 2027.

Mai magana da yawun Sanatan, Isma’il Mudashir ne ya bayyana hakan a cikin wata sanarwa ranar Talata, inda ya ce a maimakon haka, kamata ya yi kungiyar ta fi mayar da hankali wajen mara wa Tinubu baya ya samu nasarar yunkurinsa na bunkasa Najeriya.

A kwanan nan ne dai wata kungiya mai suna Zauren Matasan APC na Arewacin Najeriya (NNPYA) ta ayyana goyon bayanta ga Tinubu ya dauki Sanatan a matsayin wanda za su yi takara tare.

Gwamnatin Nijeriya ta yi wa Amurka martani kan barazanar tsaro a Abuja Mali ta ƙulla yarjejeniyar nukiliya da Rasha

Hakan dai ya biyo bayan jita-jitar da ake ta yadawa a ’yan kwanakin nan cewa ba lallai ne Tinubun ya sake yin takara tare da Kashim Shettima a matsayin mataimakinsa a 2027 din ba.

A cewar Sanata Barau, “An jawo hankalina kan wasu rubuc-rubuce a shafukan sada zumunta da ma wasu jaridu na wasu kungiyoyi, cikinsu har da NNPYA, inda suke kiran jagoranmu, Shugaba Bola Tinubu, da ya dauke ni a matsayin mataimaki a 2027. Wannan ba da yawuna ba ne kuma ba shi ne abu mafi muhimmanci ba a yanzu.

“Ina kira ga NNPYA da ma sauran kungiyoyin da ke wannan fafutukar da su daina daga yanzu, sannan su mayar da hankalinsu wajen goyon bayan yunkurin Shugaba Tinubu na magance matsalolin da ke addabar kasarmu.

“Kamata ya yi mu hada karfi da karfe wajen goyon bayan Tinubu har ya samu ya kai Najeriya tudun mun tsira.

“Yanzu ba lokaci ne da za mu rika wannan kiraye-kirayen ba, lokaci ne na tabbatar da cewa Tinubu ya samu nasarar sauke nauyin da ke wuyansa.

“Ya damu kwarai da gaske wajen ganin Najeriya ta samu ci gaba. Saboda haka nake kira da kowa ya goya masa baya kan kudurorinsa da tuni aka fara ganin amfaninsu a kasa,” in ji Sanata Barau.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Barau

এছাড়াও পড়ুন:

Tinubu zai kashe tiriliyan 1.5 wajen gina layin dogo na zamani a birnin Kano

Shugaban Kwamitin Kasafin Kudi na Majalisar Wakilai, Abubakar Kabir Abubakar, ya ce Gwamnatin Tarayya za ta kashe Naira tiriliyan daya da rabi don gina layin dogo na zamani domin saukaka harkar sufuri a cikin birnin Kano.

Ya bayyana hakan ne lokacin da yake amsa tambayoyin manema labarai a Kano, inda ya ce aikin zai saukaka wa mazauna birnin wahalar da suke sha a harkar sufuri.

Zamfarawa sun yi zanga-zanga kan hare-haren ’yan bindiga Abba ya yi alhinin hadiminsa da ’yan daba suka kashe a Kano

Ya ce, “Wannan aikin na gina layin dogo na zamani ya kai Dalar Amurka biliyan daya, kwatankwacin Naira tiriliyan daya da rabi.

“Ga wadanda suke tafiye-tafiye zuwa kasashen waje, musamman kasashen Turai da nahiyar Asiya, sun san akwai irin wadannan ayyukan kuma suna da muhimmanci. Aikin zai kara habaka tattalin arzikin jihar idan aka kammala shi.”

Dan majalisar ya kuma ce sabanin yadda ake yadawa, Shugaban Kasa Bola Tinubu, ya bullo da muhimman ayyukan raya kasa a bangarorin lafiya da aikin gona da ilimi da kuma tsaro a Arewacin Najeriya.

“Abin mamaki ne idan na ji wasu mutane na cewa Shugaba Tinubu bai damu da Arewa ba. Ni ne shugaban kwamitin kasafin kudi, kuma na san me ya yi wa Arewa.

“Ya kamata mu ajiye son rai a gefe guda mu fada wa kanmu gaskiya a kan Shugaba Tinubu. Ya bijiro da ayyuka da dama a Arewa da ya kamata a yaba masa,” in ji Abubakar Bichi.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Cacar Baki Ta Ɓarke Tsakanin el-Rufai Da APC Kan Tazarcen Tinubu A 2027
  • An Naɗa Farfesa Adamu Muƙamin Mataimakin Shugaban Jami’ar Yakubu Gowon, Abuja
  • PDP ta gargaɗi ’ya’yanta kan goyon bayan Tinubu a zaɓen 2027
  • Tinubu zai kashe tiriliyan 1.5 wajen gina layin dogo na zamani a birnin Kano
  • NAJERIYA A YAU: Shekara nawa shugabanni ke bukata don cika alkawuran zabe?
  • Tsoffin Kansilolin APC Sun Yi Zanga-zangar Nesanta Kansu Da Maganganun Abdullahi Abbas 
  • Abba ya yi alhinin hadiminsa da ’yan daba suka kashe a Kano
  • NAHCON ta ƙayyade N8.5m kafin alƙalami na kujerar Hajjin 2026
  • Ranar Cutar Daji Ta 2025: Akwai Matakan Kariya Daga Kamuwa Da Cutar Kansa -Masana
  • Tinubu Ya Nada Sabon Shugaban Hukumar Kula Da Wutar Lantarki Ta Kasa