Aminiya:
2025-08-05@02:39:18 GMT

Yin sulhu da ’yan bindiga dabara ce ba gazawa ba — Gwamnatin Sakkwato

Published: 20th, June 2025 GMT

Gwamnatin Jihar Sakkwato ta ce ba gazawa ba ce ta sa ta yanke shawarar tattaunawa da ’yan bindigar da suka yanke hukuncin ajiye makamansu ba.

Ta ce wannan hanya ce mafi kyau da za ta kawo zaman lafiya mai ɗorewa a jihar.

Katolika ta horar da shugabannin al’umma da na addini kan zaman lafiya Kotu ta daure mutumin da yake yada bidiyon tsiraici shekara 76 a kurkuku

Wani mai amfani da kafar sada zumunta, Basharu Altine Guyawa, ya soki wannan mataki na gwamnatin.

Amma Mai Bai Wa Gwamnan Jihar Shawara kan Tsaro, Kanal Ahmed Usman (mai ritaya), ya ce manufar gwamnati ita ce ta kawo zaman lafiya, ba don ta kasa ba.

Ya ce, “Mun san kowa na da ‘yancin faɗin albarkacin bakinsa. Amma dole ne mu fayyace dalilin da ya sa Gwamna Ahmed Aliyu ke amfani da hanyoyi daban-daban wajen magance matsalar rashin tsaro, ciki har da tattaunawa da ‘yan bindigar da suka tuba.”

Ya ƙara da cewa abin mamaki ne yadda Guyawa ke sukar wannan yunƙuri.

Ya ce shi ma ya taɓa buƙatar shirin shiga tsakanin gwamnati da ‘yan bindiga domin yin sulhu.

Kanal Usman ya bayyana cewa gwamnati tana amfani da dukkanin matakai biyu; na ƙarfi da na sulhu.

A cewarsa, mutane da yawa a Rabah, Goronyo, Isa, Sabon Birni da wasu yankuna na ta yin hijira.

Manoma sun bar gonakinsu, amfanin gona ya ragu, kuma kasuwanci ya tsaya cak.

Wannan ya jawo ƙarancin abinci da tsadar rayuwa a faɗin jihar.

“Burinmu shi ne mu dawo da zaman lafiya, mu dawo da mutane gidajensu, sannan a sake farfaɗo da harkokin noma da kasuwanci,” in ji shi.

Ya ce har yanzu gwamnati na aike jami’an tsaro inda ya dace.

Amma waɗanda suka tuba da gaske za a karɓe su bisa kulawa da tsari na gyaran hali.

“Wannan ba gajiyawa ba ce ko jin tsoro, wannan dabara ce ta sulhu domin ɗorewar zaman lafiya.”

Amma ya roƙi masu sukar gwamnati da su yi magana cikin hankali.

“Jihar Sakkwato na buƙatar haɗin kai da mafita, ba rabuwar kai da zargi ba. Gwamna Ahmed Aliyu na aiki tuƙuru don kawo zaman lafiya.”

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Yan Bindiga Gwamnatin Sakkwato martani Tsaro zaman lafiya

এছাড়াও পড়ুন:

Sauyin Yanayi: Gwamnatin Kano ta ƙaddamar da shirin dashen bishiya miliyan 5

Gwamnan Jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, ya ƙaddamar da babban shirin dashen bishiyoyi miliyan biyar a shekarar 2025.

An fara dashen ne yankin Yanbawa da ke Ƙaramar Hukumar Makoda.

Sake zaɓen Tinubu zai lalata makomar Najeriya — El-Rufai  Gwamnan Yobe ya naɗa Gadaka a matsayin sabon Sarkin Gudi

Gwamnan ya ce wannan shiri na nufin yaƙi da sauyin yanayi, farfaɗo da ƙasar da ta lalace, da kuma kare muhalli.

Ya ce an fara dashen bishiyoyin a wannan fili tun shekarar 1972, amma aka bari ya lalace.

Yanzu gwamnatinsa ta gyara shi don ya taimaka wajen shawo kan matsalolin fari da sauyin yanayi.

Ya ƙara da cewa wannan shiri yana daga cikin ayyukan muhalli da gwamnatinsa ta aiwatar cikin shekara guda.

Ayyukan sun haɗa da gyaran gonakin dasa itatuwa a Garun Malam da Garko, waɗanda yanzu suke samar da dubban ƙananan itatuwa da ake rabawa a Kananan Hukumomin 44 na jihar.

Ya ce tuni aka farfaɗo da sama da hekta 200,000 na ƙasa da ta lalace.

Hakazalika, ya ce an samar da wata gona mai hekta 100 domin koya wa manoma dabarun noman itatuwa da kayan gona.

Gwamnan, ya bayyana cewa suna haɗin gwiwa da Ƙungiyar Abinci da Aikin Gona ta Majalisar Ɗinkin Duniya (FAO), don koyar da yadda ake amfani da ƙasa yadda ya kamata da kula da muhalli.

Ya ce sun kuma fara shirye-shiryen ilmantar da makarantu da al’umma game da sauyin yanayi da muhimmancin kula da muhalli.

Don ɗorewar wannan shiri, gwamnan ya ce an kafa dokar sauyin yanayi da tsarin aiki a Jihar Kano, wanda ya sanya mata hannu.

Haka kuma an kafa ɗakin gwajin gurɓacewar iska da ruwa a Jami’ar Northwest don binciken muhalli.

Ya ce yanzu haka suna fitar da rahotannin lafiyar iska da ruwa a kowane mako daga sabon ɗakin binciken.

Wannan ya nuna cewa gwamnatin tana amfani da kimiyya da bayanai wajen yaƙi da sauyin yanayi.

Gwamnatin ta sake ɗaukar masu tsaron daji, tare da biyansu albashi, sannan ta ɗauki sabbin ma’aikata don kare dazuka a faɗin jihar.

“Dukkanin itacen da muka dasa dole ne ya girma,” in ji gwamnan.

“Shi ya sa muke gina ƙwararrun cibiyoyi da tsarin lura da yadda shirin ke tafiya.”

Za a raba itatuwan a makarantu, wuraren ibada, gonaki, gidaje, wuraren jama’a, da kuma gefen tituna a cikin gari da karkara.

Gwamnan, ya umarci shugabannin Ƙananan Hukumomi 44 su ɗauki shirin da muhimmanci, su tabbatar da gaskiya wajen raba itatuwan.

“Yanzu ne lokacin da ya dace mu dakatar da yaɗuwar hamada, mu yaƙi sauyin yanayi, da hana zaizayar ƙasa.

“Mu daina sare itatuwa ba tare da tunani ba. Kowa ya dasa, ya kula, kuma ya kare itatuwa don kare ƙasarmu da makomar ’ya’yanmu,” in ji shi.

Ya kuma yi kira ga shugabannin gargajiya, matasa, ƙungiyoyi, makarantu da kasuwanni su haɗa kai wajen samar da kyakkyawan muhalli a Kano.

“A yau ne muka ɗauki alhakin gyara ƙasarmu. Allah Ya taimake mu a wannan aikin alheri,” a cewarsa.

Kwamishinan Muhalli da Sauyin Yanayi, Muhammad Dahiru Hashim, ya ce wannan shiri na dasa itatuwa ya nuna irin jajircewar Gwamnan wajen kare muhalli.

Ya bayyana cewa shekara guda da ta wuce, suka fara shirin dasa itatuwa miliyan uku.

Wannan sabon shirin ya ƙara faɗaɗa, kuma an yi amfani da itatuwan da aka noma a cikin jihar.

Ya ce an sake farfaɗo da gonakin gwamnati da ke Gwale da Gwarzo, waɗanda yanzu ke samar da itatuwa don ɗorewar wannan shiri.

Ya ƙara da cewa tun da farko Gwamna Abba, ya nuna irin ƙwarewarsa wajen kare muhalli.

Aikin farko da ya halarta bayan ya hau mulki shi ne bikin Ranar Muhalli ta Duniya ta 2023, wanda ya nuna wa jama’a cewa gwamnatinsa na ɗaukar sauyin yanayi da muhimmanci.

“Jihar Kano ba kawai tana dasa itatuwa ba ne. Muna gyara muhalli, muna tsaftace iska, kuma muna dakatar da yaɗuwar hamada.

“Wannan shiri yana nuna sauyi, da kuma makomarmu,” in ji shi.

Ya kuma yaba wa ma’aikatan ma’aikatar muhalli, shugabannin gargajiya, saboda irin goyon bayan da suka bayar don nasarar wannan shiri.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Mu daina zagin malaman addini idan muna son zaman lafiya — Uba Sani
  • Gwamna Buni Ya Bukaci Sabon Sarkin Gudi Ya Jagoranci Zaman Lafiya, Hadin Kai, Da Ci Gaban Kasa
  • ‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutane Da Dama A Kauyukan Zamfara
  • Gwamnatin Sakkwato Za Ta Kashe fiye da Naira Miliyan 200 Wajen Gyara Tashar Talabijin Ta Kasa NTA
  • Wani Dan Siyasa Ya Shirya Addu’o’i Na Musamman Domin Samun Zaman Lafiya A Zamfara
  • Kano Za Ta Mayar Da Gidan Yarin Kurmawa Zuwa Gidan Tarihi – Gwamnati
  • Sauyin Yanayi: Gwamnatin Kano ta ƙaddamar da shirin dashen bishiya miliyan 5
  • Ma’aikatan Jinya Sun Janye Yajin Aiki Bayan Gwamnatin Tarayya Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu 
  • Jihar Sakkwato ta ciyo bashin N70.4bn domin inganta kiwon lafiya
  • Jihar Sakkwato ta ciyo bashin N70.4bn N70.4bn domin inganta kiwon lafiya