Aminiya:
2025-06-20@19:07:23 GMT

Yin sulhu da ’yan bindiga dabara ce ba gazawa ba — Gwamnatin Sakkwato

Published: 20th, June 2025 GMT

Gwamnatin Jihar Sakkwato ta ce ba gazawa ba ce ta sa ta yanke shawarar tattaunawa da ’yan bindigar da suka yanke hukuncin ajiye makamansu ba.

Ta ce wannan hanya ce mafi kyau da za ta kawo zaman lafiya mai ɗorewa a jihar.

Katolika ta horar da shugabannin al’umma da na addini kan zaman lafiya Kotu ta daure mutumin da yake yada bidiyon tsiraici shekara 76 a kurkuku

Wani mai amfani da kafar sada zumunta, Basharu Altine Guyawa, ya soki wannan mataki na gwamnatin.

Amma Mai Bai Wa Gwamnan Jihar Shawara kan Tsaro, Kanal Ahmed Usman (mai ritaya), ya ce manufar gwamnati ita ce ta kawo zaman lafiya, ba don ta kasa ba.

Ya ce, “Mun san kowa na da ‘yancin faɗin albarkacin bakinsa. Amma dole ne mu fayyace dalilin da ya sa Gwamna Ahmed Aliyu ke amfani da hanyoyi daban-daban wajen magance matsalar rashin tsaro, ciki har da tattaunawa da ‘yan bindigar da suka tuba.”

Ya ƙara da cewa abin mamaki ne yadda Guyawa ke sukar wannan yunƙuri.

Ya ce shi ma ya taɓa buƙatar shirin shiga tsakanin gwamnati da ‘yan bindiga domin yin sulhu.

Kanal Usman ya bayyana cewa gwamnati tana amfani da dukkanin matakai biyu; na ƙarfi da na sulhu.

A cewarsa, mutane da yawa a Rabah, Goronyo, Isa, Sabon Birni da wasu yankuna na ta yin hijira.

Manoma sun bar gonakinsu, amfanin gona ya ragu, kuma kasuwanci ya tsaya cak.

Wannan ya jawo ƙarancin abinci da tsadar rayuwa a faɗin jihar.

“Burinmu shi ne mu dawo da zaman lafiya, mu dawo da mutane gidajensu, sannan a sake farfaɗo da harkokin noma da kasuwanci,” in ji shi.

Ya ce har yanzu gwamnati na aike jami’an tsaro inda ya dace.

Amma waɗanda suka tuba da gaske za a karɓe su bisa kulawa da tsari na gyaran hali.

“Wannan ba gajiyawa ba ce ko jin tsoro, wannan dabara ce ta sulhu domin ɗorewar zaman lafiya.”

Amma ya roƙi masu sukar gwamnati da su yi magana cikin hankali.

“Jihar Sakkwato na buƙatar haɗin kai da mafita, ba rabuwar kai da zargi ba. Gwamna Ahmed Aliyu na aiki tuƙuru don kawo zaman lafiya.”

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Yan Bindiga Gwamnatin Sakkwato martani Tsaro zaman lafiya

এছাড়াও পড়ুন:

Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 24 A Katsina

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ba Tsoro Ne Yasa Muka Amince Da Sulhu Da Ƴan Bindiga Ba – Gwamnatin Sokoto
  • Katolika ta horar da shugabannin al’umma da na addini kan zaman lafiya
  • Ambaliyar Ruwan Mokwa: Masana Sun Shawarci Gwamnati Kan Matakin Kariya A Nan Gaba
  • Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 24 A Katsina
  • Xi Ya Tattauna Da Shugaban Rasha Ta Wayar Tarho
  • Masarautar Gaya Ta Ƙwace Sarautar Wazirin Gaya Da Ta Bai Wa Tsohon Sakataren Gwamnatin Kano
  • Dan Wasan Gaban Chelsea, Murdyk Ka Iya Shafe Shekaru 4 Ba Tare Da Ya Buga Wasa Ba
  • Mun shirya yin sulhu da ’yan bindiga — Gwamnatin Sakkwato
  • Buni ya bai wa manoma 1,000 tallafin aikin gona