Dole a ɗauki mataki kan waɗanda suka kashe ’yan ɗaurin aure a Filato — Uba Sani
Published: 22nd, June 2025 GMT
Gwamnan Kaduna, Uba Sani ya buƙaci a ɗauki mataki kan kisan wasu ’yan jiharsa mutum 12 a Ƙaramar Hukumar Mangu ta Jihar Filato a hanyarsu ta zuwa ɗaurin auren ɗan uwansu.
Aminiya ta ruwaito cewa an kashe mutum 12 yayin da wasu 11 suka jikkata daga cikin mutum 31 da suka taso daga garin Basawa da ke Ƙaramar Hukumar Zaria a Jihar Kaduna cikin motar bas mallakin Jami’ar ABU Zaria, kafin su faɗa hannun maharan.
Gwamna Uba Sani ya nuna kaɗuwarsa matuka kan lamarin a cikin wata sanarwa da ya fitar, inda ya umarci jami’an tsaro da su gaggauta kama waɗanda suka aikata laifin da kuma hukunta su.
Ya sha alwashin cewa gwamnatin jihar ba za ta gajiya ba har sai ta ga an gurfanar da maharan.
“Lokaci ya yi da za mu kawo karshen irin waɗannan abubuwa na kashe mutanen da ba su yi laifin komai ba, musamman yayin tafiya tsakanin jihohi.
“Babu wata hujja ta far wa kowane ɗan Nijeriya a kowane ɓangare na ƙasar. Ya kamata mu dakatar da wannan ɗanyen aiki,” in ji gwamnan.
Ya kuma jajanta wa iyalan waɗanda lamarin ya shafa, inda ya yi kira ga al’ummar jihar da su kwantar da hankali domin ana ƙoƙarin ganin an hukunta masu laifin.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Ɗaurin Aure Jihar Filato Jihar Kaduna
এছাড়াও পড়ুন:
Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar
“Sauran motocin da ke cikin ayarin, ciki har da wacce ke ɗauke da shugaban majalisar, da ƙyar suka iya tsayawa wanda tsakaninsu mitoci kaɗan ne daga wurin da haɗarin ya afku,” in ji wani ganau.
Majiyoyin tsaro sun tabbatar da cewa, an garzaya da jami’an ‘yansandan da suka samu raunuka zuwa babban asibitin Gumel a sume amma daga baya sun farfaɗo.
Da yake magana kan lamarin, mataimakin shugaban majalisar, Aqeel Akilu, ya yi godiya ga Ubangiji cewa, ba a rasa rayuka ba.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp