Dole a ɗauki mataki kan waɗanda suka kashe ’yan ɗaurin aure a Filato — Uba Sani
Published: 22nd, June 2025 GMT
Gwamnan Kaduna, Uba Sani ya buƙaci a ɗauki mataki kan kisan wasu ’yan jiharsa mutum 12 a Ƙaramar Hukumar Mangu ta Jihar Filato a hanyarsu ta zuwa ɗaurin auren ɗan uwansu.
Aminiya ta ruwaito cewa an kashe mutum 12 yayin da wasu 11 suka jikkata daga cikin mutum 31 da suka taso daga garin Basawa da ke Ƙaramar Hukumar Zaria a Jihar Kaduna cikin motar bas mallakin Jami’ar ABU Zaria, kafin su faɗa hannun maharan.
Gwamna Uba Sani ya nuna kaɗuwarsa matuka kan lamarin a cikin wata sanarwa da ya fitar, inda ya umarci jami’an tsaro da su gaggauta kama waɗanda suka aikata laifin da kuma hukunta su.
Ya sha alwashin cewa gwamnatin jihar ba za ta gajiya ba har sai ta ga an gurfanar da maharan.
“Lokaci ya yi da za mu kawo karshen irin waɗannan abubuwa na kashe mutanen da ba su yi laifin komai ba, musamman yayin tafiya tsakanin jihohi.
“Babu wata hujja ta far wa kowane ɗan Nijeriya a kowane ɓangare na ƙasar. Ya kamata mu dakatar da wannan ɗanyen aiki,” in ji gwamnan.
Ya kuma jajanta wa iyalan waɗanda lamarin ya shafa, inda ya yi kira ga al’ummar jihar da su kwantar da hankali domin ana ƙoƙarin ganin an hukunta masu laifin.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Ɗaurin Aure Jihar Filato Jihar Kaduna
এছাড়াও পড়ুন:
An rufe masana’antu 1,724 bisa rashin bin dokokin aiki a Guinea
Gwamnatin ƙasar Guinea ta rufe wasu sassan kamfanoni guda 1,724 sakamakon kama su da laifin ƙin bin dokokin hukuma, yayin da aka janye kayayyakin da suke sarrafawa daga kasuwa.
Sanarwar na zuwa ne ƙarƙashin ma’aikatar kasuwanci a ƙasar, tana mai cewa an ɗauki matakin ne don kare lafiyar masu sayen kayayyakin da kuma tabbatar da kare muhalli, da kuma tilasta musu biyayya ga dokokin tafiyar da kamfanoni.
Ma’aikatar kasuwanci ta ƙasar ta ce ba shakka wannan mataki zai zama tamkar hannunka mai sanda ga sauran kamfanoni da ke tafiyar da ayyukansu ba dai-dai ba.
Da yake magana shugaban ƙungiyar masu sayen kayayyaki na ƙasar, Ousmane Keita, ya ce tun shekaru sama da uku suke ta wannan kiraye-kiraye, amma ba a sami damar daukar mataki ba sai yanzu.
NAJERIYA A YAU: Yadda tsadar taki ke hana noman masara da shinkafa An wajabta wa ɗaliban firamare mallakar lambar NIN a BauchiA cewar sa ba shakka wannan matakin zai sassauta yadda kamfanonin ke wasa da aikinsu da kuma jefa rayukan jama’a cikin hadari.
Bayanai sun ce a yanzu gwamnati zata mayar da hankali wajen sayawa kamfanonin da ke sarrafa ruwan sha idanun ganin muhimmancinsa ga lafiyar dan Adam.