Aminiya:
2025-06-21@16:43:38 GMT

Bam ya kashe mutum 5, 15 sun jikkata a Kano

Published: 21st, June 2025 GMT

Aƙalla mutum biyar ne aka tabbatar da rasuwarsu, yayin da wasu 15 suka jikkata sakamakon fashewar wani bam a Jihar Kano.

Aminiya ta gano yadda fashewar bam ɗin ya haddasa firgici a yankin da lamarin ya faru, inda jami’an tsaro da na agajin gaggawa suka garzaya wajen don kai ɗauki.

An yi wa ma’aikatan ƙananan hukumomin Gombe ƙarin albashin N5,000 Mahara sun kashe ’yan ɗaurin aure 12 daga Zariya a Filato

Kwamishinan ‘yan sandan Jihar Kano, Ibrahim Adamu Bakori, ya ce fashewar na iya kasancewa bam ɗin da sojoji suke yin jigilar ne wanda aka yi sakaci ya fashe.

“Na samu kiran gaggawa cewa wani abu mai tayar da hankali ya faru. Da na isa wajen, sai na ga abin kamar bama-baman sojoji ne suka fashe.

“Mutane 15 sun jikkata, kuma abin takaici, guda biyar sun rasu,” in ji shi.

Ya ƙara da cewa an garzaya da waɗanda suka jikkata zuwa asibitocin da ke kusa yankin domin samun kulawa ta gaggawa.

Ya ce binciken farko ya nuna cewa wata babbar mota ce ɗauke da kayan fashewar, wadda ta ke kan hanyar zuwa Jihar Yobe.

Har yanzu jami’an tsaro ba su tabbatar da ko motar sojoji ce ke ɗauke da kayan fashewar ba.

Rundunar na ci gaba da da bincike domin gano musabbabin faruwar lamarin da kuma abin da ya haddasa fashewar abun.

“Za mu samu cikakken bayani bayan kammala bincike,” in ji Kwamishinan.

Ya kuma roƙi jama’a da su kwantar da hankalinsu.

 

Ga hotunan yadda jami’an tsaro ke bincike kan lamarin:

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Yan Sanda fashewa

এছাড়াও পড়ুন:

Najeriya ta tura sojoji domin samar da zaman lafiya a Gambia

Najeriya ta tura sojojinta 197 domin zuwa aikin tabbatar da tsaro da wanzar da zaman lafiya a kasar Gambia.

Dakarun na Najeriya waɗanda tuni suka kammala samun horo, za sai yi aikin wanzar da zaman lafiya a Gambia be a ƙarƙashin rundunar Ƙungiyar Tattalin Arzikin Yammacin Afirka (ECOWAS) da sunan (ECOMIG).

Shugaban Ayyuka na Rundunar Sojin Ƙasa ta Najeriya, Manjo-Janar Uwem Bassey, ya buƙaci sojojin da su kasance masu nuna nuna ƙwarewa da jarumta a yayin gudanar da ayyukansu a ƙasar Gambia.

Ya yi wannan kira ne a jawabinsa a wurin bikin yaye sojojin a Barikin Sojoji na Jaji da ke Jihar Kaduna, kafin tafiyarsu.

Yadda Iran ta lalata cibiyar kimiyya mafi muhimmanci a Isra’ila An sallami ƙarin ma’aikata 639 a tashar Muryar Amurka

Manjo-Janar Bassey ya buƙaci sojojin da su guji nuna son kai, su mutunta hakkokin ɗan Adam da kuma dokoki da al’adun al’ummar Gambia.

Ya gargaɗe su game da cin zarafi musamman na jinsi, tare da cewa duk sojan aka samu da laifi zai gamu da tsauraran matakan ladabtarwa.

Bassey ya bayyana cewa Najeriya tana da dogon tarihi na bayar da gudummawa ga ayyukan wanzar da zaman lafiya na ƙasar da ƙasa, inda sojojinta ke samun karɓuwa a duniya saboda jaruntakarsu, da ƙwarewarsu.

Sojojin Najeriya sun taka muhimmiyar rawa wajen dawo da zaman lafiya a rikice-rikicen da aka samu a faɗin Afirka da ma duniya, ciki har da Lebanon da Yugoslavia da Laberiya, Saliyo, da Sudan, inda suka ci gaba da samun yabo saboda jaruntakarsu da ƙwarewarsu.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ɗan ƙunar baƙin wake ya kashe mutum 10 da bam a Borno
  • Bom ya kashe mutum 5 a Kano — ’Yan sanda
  • Mahara sun kashe ’yan ɗaurin aure 12 daga Zariya a Filato
  • Najeriya ta tura sojoji domin samar da zaman lafiya a Gambia
  • Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (6)
  • Rikicin Filato: An sake kashe mutum 17 a Mangu da Bokkos
  • Sojoji Sun Daƙile Harin Ƴan Ta’adda, Sun Kashe 8 A Katsina
  • Gwamnonin APC Sun Nemi Tinubu Ya Ƙirkiri ‘Yansandan Jihohi Don Yaƙar Matsalar Tsaro
  • An ɗaure mutum 7 kan yi wa ɗan sanda rauni a Kano