Aminiya:
2025-06-24@20:37:35 GMT

Trump ya zargi Isra’ila da Iran da saɓa yarjejeniyar tsagaita wuta

Published: 24th, June 2025 GMT

Shugaban Ƙasar Amurka Donald Trump ya zargi Iran da Isra’ila da saɓa yarjejeniyar tsagaita wuta.

Da yake jawabi kafin tafiyar Babban Taron Ƙungiyar NATO, da zai gudana a birnin Hague, Trump, ya bayyana takaicinsa bisa yadda kasashen biyu game da saɓa yarjejeniyar, sa’o’i kaɗan bayan sun amince da ita.

Tun da farko sai da ya buƙaci Isra’ila ta janye shirinta na kai wa Iran hari.

A safiyar Litinin bayan sanarwar Trump cewa ɓangarorin sun amince su tsagaita wuta ne, Ministan Tsaron Isra’ila ya yi barazanar kai wa Iran hari mai tsanani bayan zargin ta da harbo wa ƙasarsa rokoki.

Iran ta musanta zargin tare da cewa Isra’ila za ta yaba wa aya zaƙi idan kuskura ta kawo mata hari.

Daga bisani Trump ya ce wa Isra’ilar, “Kada ki kai harin bom a Iran, yin kika babban saɓawa ne. Ki umarci matuƙa jiragenkinki su koma gida.”

Buƙatar tasa bayan fara tsagaita wuta da Iran ta yi, na da alaƙa da sabon tayar da jijiyoyin wuts tsakanin Iran da Isra’ila.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Iran Isra ila yarjejeniyar tsagaita wuta

এছাড়াও পড়ুন:

Yakin Iran Da Isra’ila Ya Haifar Da Tashin Farashin Litar Man Fetur A Nijeriya

Rikicin Isra’ila da Iran ya kara dagula tabarbarewar harkokin man fetur da iskar gas a cikin fargabar barkewar rikicin Gabas ta Tsakiya wacce ta kasance jigo wajen hada-hadar man fetur da iskar gas.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Trump ya soki Iran da Isra’ila kan saɓa wa yarjejeniyar tsagaita wuta
  • Harin asibiti ya kashe mutum 40 a Sudan — WHO
  • Mun amince da tsagaita wuta da Iran —Isra’ila
  • Iran da Isra’ila sun amince da tsagaita wuta —Trump
  • Iran Da Isra’ila Sun Amince Su Tsagaita Wuta – Trump
  • Trump ta ce Iran da Isra’ila sun amince da tsagaita wuta bayan harin Iran kan sansanonin Amurka
  • Yakin Iran Da Isra’ila Ya Haifar Da Tashin Farashin Litar Man Fetur A Nijeriya
  • Koriya ta Arewa za ta taimaka wa Iran gyara tashoshin nukiliyan da Amurka ta kai hari —Masani
  • Za mu ci gaba da yi wa Isra’ila luguden wuta — Shugaban Iran