A cikin takardar, ƙungiyar ta bayyana cewa ta yanke shawarar kafa sabuwar jam’iyya maimakon haɗaka da wasu.

Sun bayyana cewa sun zaɓi suna All Democratic Alliance (ADA) kuma taken jam’iyyar shi ne “Justice for All” wato “Adalci ga Kowa.”

Sun kuma haɗa da adireshin babban ofishin jam’iyyar a cikin takardar.

Sun gabatar da wasu muhimman takardu da suka haɗa da tambarin jam’iyya, tsarin kundin mulki, tutar jam’iyyar, da manufofinta.

Tambarin jam’iyyar ya ƙunshi kayan hatsi irin su masara da launuka masu ma’ana.

Kundin tsarin mulki kuma ya ƙunshi manufofi, tsari da dokokin jam’iyyar, bisa ga tsarin dokokin Najeriya da ƙa’idar dimokuraɗiyya ta duniya.

Takardar ta ƙare da girmamawa, inda ta ke roƙon INEC da ta ɗauki mataki na gaba wajen kammala rijistar jam’iyyar.

Sauran manyan ‘yan siyasa da ke cikin wannan haɗaka sun haɗa da Tsohon Gwamnan Jihar Ribas, Rotimi Amaechi, Tsohon Shugaban Majalisar Dattawa David Mark, da Dakta Umar Ardo, wanda ya kafa ƙungiyar League of Northern Democrats.

A baya, ƙungiyar ta yi la’akari da shiga wata jam’iyya, kamar African Democratic Congress (ADC) da Social Democratic Party (SDP).

Sai dai daga sun fasa bayan sun lura da rikice-rikicen cikin gida da shari’o’i da waɗannan jam’iyyu ke fuskanta.

Saboda haka, suka zaɓi kafa sabuwar jam’iyya da za su fara daga tushe tare da daidaita tsakanin mambobinta.

Yanzu suna jiran matakin da INEC za ta ɗauka yayin da suke shirin tunkarar zaɓen 2027.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Adawa Haɗaka Manyan Yan Siyasa Sabuwar Jam iyya

এছাড়াও পড়ুন:

An Kashe Wasu ‘Yan Bindiga 12, An Kwato Makamai A Katsina

Da take aiwatar da rahotannin sirri cikin gaggawa, rundunar hadin gwiwa da ta kunshi jami’an ‘yansandan Nijeriya, Sojoji, jami’an kula da jama’a na jihar, da ’yan banga na yankin sun bi sawun barayin da suka tsere zuwa Dutsen Falale da ke yankin Kurfi-Safana inda aka yi musayar wuta mai tsanani, wanda ya yi sanadin mutuwar ‘yan bindigar 12.

 

Sai dai kuma, yayin da yake yabawa wannan bajinta da jajircewa da jami’an tsaron suka yi, Dakta Mua’zu ya bayyana matukar alhininsa game da rasuwar wani dan banga mai suna Alhaji Danmalam wanda ya rasa ransa a fafatawar.

 

Bugu da kari, soja guda ya samu raunuka kuma a halin yanzu yana samun kulawa a Asibiti.

 

Alhaji Danmalam ya rasu ne sakamakon harbin bindiga a cibiyar kiwon lafiya ta matakin farko da ke Charanchi.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • 2027: Manyan ’Yan adawa na neman rajistar sabuwar jam’iyya
  • Zamfara Ta Zama Jiha Ta Farko Da Ta Ƙaddamar da Tsarin Ilimin Fasahar Zamani
  • An Kafa Fiye Da Kamfanonin Waje 24,000 A Sin Cikin Watanni 5 Na Farkon Bana
  • An Nemi A Kafa Dokar Ta-ɓaci Kan Masu Ƙwacen Waya
  • Tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa, Namadi Sambo Ya Karyata Sauya Sheƙa Zuwa APC
  • Ba Atiku kaɗai ba ne matsalar PDP — Gwamna Lawal
  • An ɗaure mutum 7 kan yi wa ɗan sanda rauni a Kano
  • Motoci Masu Aiki Da Lantarki Kirar Sin Sun Samar Da Sabuwar Hanyar Sufuri Ga Al’Ummun Kasashen Shiyyar Tsakiyar Asiya
  • An Kashe Wasu ‘Yan Bindiga 12, An Kwato Makamai A Katsina