Atiku Da Wasu Sun Kafa Sabuwar Jam’iyya, Sun Nemi INEC Ta Musu Rajista
Published: 21st, June 2025 GMT
A cikin takardar, ƙungiyar ta bayyana cewa ta yanke shawarar kafa sabuwar jam’iyya maimakon haɗaka da wasu.
Sun bayyana cewa sun zaɓi suna All Democratic Alliance (ADA) kuma taken jam’iyyar shi ne “Justice for All” wato “Adalci ga Kowa.”
Sun kuma haɗa da adireshin babban ofishin jam’iyyar a cikin takardar.
Sun gabatar da wasu muhimman takardu da suka haɗa da tambarin jam’iyya, tsarin kundin mulki, tutar jam’iyyar, da manufofinta.
Tambarin jam’iyyar ya ƙunshi kayan hatsi irin su masara da launuka masu ma’ana.
Kundin tsarin mulki kuma ya ƙunshi manufofi, tsari da dokokin jam’iyyar, bisa ga tsarin dokokin Najeriya da ƙa’idar dimokuraɗiyya ta duniya.
Takardar ta ƙare da girmamawa, inda ta ke roƙon INEC da ta ɗauki mataki na gaba wajen kammala rijistar jam’iyyar.
Sauran manyan ‘yan siyasa da ke cikin wannan haɗaka sun haɗa da Tsohon Gwamnan Jihar Ribas, Rotimi Amaechi, Tsohon Shugaban Majalisar Dattawa David Mark, da Dakta Umar Ardo, wanda ya kafa ƙungiyar League of Northern Democrats.
A baya, ƙungiyar ta yi la’akari da shiga wata jam’iyya, kamar African Democratic Congress (ADC) da Social Democratic Party (SDP).
Sai dai daga sun fasa bayan sun lura da rikice-rikicen cikin gida da shari’o’i da waɗannan jam’iyyu ke fuskanta.
Saboda haka, suka zaɓi kafa sabuwar jam’iyya da za su fara daga tushe tare da daidaita tsakanin mambobinta.
Yanzu suna jiran matakin da INEC za ta ɗauka yayin da suke shirin tunkarar zaɓen 2027.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: Adawa Haɗaka Manyan Yan Siyasa Sabuwar Jam iyya
এছাড়াও পড়ুন:
Tsohon Shugaban Amurka Joe Biden Ya Caccaki Trump Kan Rusa Kundin Tsarin Mulkin Kasar
Tsohon shugaban Amurka Joe Biden ya yi dirar mikiya da ba a taba ganin irinsa ba kan gwamnatin Trump!
Tsohon shugaban kasar Amurka Joe Biden ya yi gargadin cewa: Amurka na fuskantar “kwanaki masu duhu” a karkashin gwamnatin shugaba Donald Trump, yana mai zargin bangaren zartarwa da “rusa kundin tsarin mulkin kasar,” tare da dorawa Majalisa da Kotun Koli wani bangare na alhakinsu.
Biden ya bayyana hakan ne a wani jawabi da ya gabatar a birnin Chicago a wajen taron shekara-shekara na kungiyar lauyoyi ta kasa, inda ya yi jawabi ga lauyoyi da alkalai na Amurka baki daya.
Biden ya jaddada cewa; Gwamnatin Trump tana yin hakan, sau da yawa tare da taimakon Majalisa da ke zaune a gefe, da kuma ba da ikon kotun koli a ƙasar. “Allah ne ya san irin hukunce-hukuncen da mahukuntan Amurka suke zartarwa bisa radin kansu.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka IRGC Tace Bata Amince Da Kasashen Biyu A Kan Kasar Falasdinu Ba August 3, 2025 Iran Da Japan Suna Iya Jagorantar Duniya Don Rabata Da Makamai Kare Dangi August 3, 2025 Kungiyar Hamas Ta Bayyana Cewa Ba za ta Ajiye Makamanta ba Sai Bayan samar Da Kasar falasdinu August 3, 2025 Kungiyar Hamas Ta Wallafa Hotunan bidiyo Na Fursinan HKI tsare A Gaza August 3, 2025 Sojojin HKI, Daga Jiya Zuwa Yau lahadi Kadai Sun Kashe Falasdinawa 62 August 3, 2025 Pezeskkian Ya Ce: Suna Fatan Musayar Kasuwancin Tsakanin Iran Da Pakistan Ta Haura Dala Biliyan 10 August 2, 2025 Araqchi: Abokantaka Da Ke Tsakanin Iran Da Pakistan Wata babbar Jari Ce Nan Gaba August 2, 2025 Jaridar Isra’ila Ta Ce: Gwamnatin Mamayar Isra’ila Ta Sha Kashi A Yakin Gaza August 2, 2025 Dakarun Yemen Sun Kai Hari Kan Filin Jirgin Lod Da Ke Haramtacciyar Kasar Isra’ila August 2, 2025 Rahoton Majalisar Dinkin Duniya Ya Yi Gargadi Kan Barazanar Kungiyoyin ‘Yan Ta’adda A Afirka August 2, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci