Aminiya:
2025-09-24@11:17:40 GMT

Fararen hula sun yi garkuwa da sojoji 57 a Columbia

Published: 23rd, June 2025 GMT

Rundunar Sojin ƙasar Columbia ta tabbatar da cewa fararen hula sun yi garkuwa da dakarunta guda 57.

Janar Federico Alberto Mejía  na Rundunar ya sanar a ranar Lahadi cewa mutane kimanin 200 sun yi garkuwa da sojojin ne bisa umarnin ’yan tawayen FARC da suka addabi ƙasar.

Ta bayyana cewa al’ummar ƙasar suna fuskantar matsin lamba daga ’yan tawayen masu ɗauke da makamai.

Sanarwar ta ƙara da cewa an sace sojoji 31 a ranar Asabar, ragowar kuma ranar Lahadi.

Erik Rodríguez ya bayyana cewa sace sojojin na da alaƙa da kama wani jagoran ’yan tawayen kungiyar EMC da sojojin suka yi.

Ya ce a yayin da suke ƙoƙarin daukar sa a jirgi ne mutanen suka yi musu ƙawanya suka yi awon gaba su a yankin Kudu maso Yammacin Micay Canyon mai tsaunuka.

Ƙungiyar ’yan tawayen FARC ta addabi yankin Kudu maso Yammacin ƙasar, wanda ya yi ƙaurin suna wajen safarar miyagun ƙwayoyi a kusa da Lardin El Plateado.

Yankin ya yi fice wajen sarrafawa da safarar horar iblis, kuma yana cikin yana daga cikin wuraren da suka fi dama da tashin-tsahina a ƙasar ta Columbia.

A baya kungiyar ta kulla yarjejeniyar zaman lafiya da gwamnatin kasar a shekarar 2016.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: yan tawayen

এছাড়াও পড়ুন:

Xi Jinping Zai Halarci Bikin Murnar Cika Shekaru 70 Da Kafuwar Yankin Xinjiang Na Uygur Mai Cin Gashin Kansa

A ranar Alhamis 25 ga watan nan, shugaban kasar Sin Xi Jinping zai halarci wani babban taro a birnin Urumqi, babban birnin yankin Xinjiang na Uygur mai cin gashin kansa, domin murnar cika shekaru 70 da kafuwar yankin.

An shirya fara bikin da shugaba Xi zai halarta da karfe 10:30 na safiyar Alhamis, kuma babban rukunin gidajen rediyo da talabijin na kasar Sin (CMG) da dandalin shafin intanet na kamfanin dillancin labarai na kasar Sin (Xinhuanet) za su watsa shi kai-tsaye. (Abdulrazaq Yahuza Jere)

 

 

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An Yanke Wa Sojojin Da Suka Sayar Wa ‘Yan Ta’adda Makamai Hukuncin Ɗaurin Rai-da-rai A Borno
  • An yi wa sojoji ɗaurin rai da rai kan sayar wa ’yan ta’adda makamai a Borno
  • Xi Jinping Zai Halarci Bikin Murnar Cika Shekaru 70 Da Kafuwar Yankin Xinjiang Na Uygur Mai Cin Gashin Kansa
  • Sojoji Sun Daƙile Hare-haren ISWAP, Sun Bai Wa Magidanta 10,000 Kariya A Borno
  • An yi garkuwa da ɗan Majalisar Dokokin Jihar Filato
  • Sojojin Mamayar Isra’ila Sun Aiwatar Da Kisan Gilla Kan Fararen Hula 5 A Kudancin Kasar Lebanon
  • Shettima ya tafi New York don halartar taron Majalisar Ɗinkin Duniya
  • Shettima ya bar Abuja don halartar taron majalisar ɗinkin duniya a New York
  • Ko Ka San Dalilin Da Zai Bai Wa Nijeriya Damar Zuwa Gasar Cin Kofin Duniya?
  • Birtaniya za ta amince da ƙasar Falasɗinu