Gwamnonin Arewa sun yi Allah-wadai da kisan ’yan ɗaurin aure a Filato
Published: 22nd, June 2025 GMT
Shugaban Ƙungiyar Gwamnonin Arewa kuma Gwamnan Jihar Gombe, Muhammadu Inuwa Yahaya, ya nuna baƙin cikinsa kan kisan wasu matafiya daga Jihar Kaduna da aka yi a Ƙaramar Hukumar Mangu ta Jihar Filato.
Matafiyan sun fito ne daga Zariya suna kan hanyarsu ta zuwa ɗaurin aure, yayin da wasu ɓata-gari suka farmake su.
Gwamnan ya ce wannan kisa abin takaici ne kuma rashin imani ne da ya saɓa wa doka.
Ya buƙaci a yi adalci cikin gaggawa.
Haka kuma ya miƙa ta’aziyyarsa ga Gwamnatin Jihar Kaduna, iyalan mamatan, da sauran waɗanda abin ya shafa.
A cewar sanarwar da Daraktan Yaɗa Labaran Gwamnatin Jihar Gombe, Isma’ila Uba Misilli, ya fitar, Gwamna Yahaya ya yaba wa gwamnati da ‘yan sanda a Jihar Filato bisa kamo wasu da ake zargi da hannu a kisan.
Gwamnan ya buƙaci a yi bincike na gaskiya, a gurfanar da waɗanda ke da hannu domin a hukunta su, sannan a hana irin hakan faruwa a gaba.
Haka kuma, ya roƙi al’ummar Filato da Kaduna da sauran maƙwabta da su zauna lafiya, su guji ɗaukar fansa.
Ya ce Gwamnonin Arewa za su ci gaba da haɗa kai domin tabbatar da zaman lafiya da tsaro a yankin.
“Ina tabbatar muku cewa kare rayuka da dukiyoyin al’umma shi ne babban burinmu. Za mu yi aiki tare har sai an kawo ƙarshen wannan matsala,” in ji Gwamnan.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Yan Ɗaurin Aure Gwamnonin Arewa
এছাড়াও পড়ুন:
Hukumar Kwastam Ta Kama Tankar Mai Dauke Da Buhunan Shinkafa A Kaduna
Kwanturola na shiyyar, Kwanturola AM Alkali, ya yaba wa jami’an bisa yadda suka nuna kwarewa a yayin gudanar da aikinsu.
Kwanturolan ya kuma yabawa muhimmiyar rawar da jama’a ke takawa, inda ya yi kira ga ‘yan Nijeriya da su marawa hukumar kwastam baya a yakin da take yi da zagon kasa ga tattalin arziki.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp