Amurka ta roƙi China ta sa baki kada Iran ta rufe mashigar tekun Hormuz
Published: 23rd, June 2025 GMT
Gwamnatin Amurka ta buƙaci ƙasar Sin da ta hana Iran rufe mashigar tekun Hormuz, ɗaya daga cikin muhimman hanyoyin jigilar kayayyaki a duniya.
Sakataren Harkokin Wajen Amurka Marco Rubio ya yi kiran ne bayan da kafar yada labarai ta Iran, Press TV ta ruwaito cewa majalisar dokokin ƙasar ta amince da shirin rufe mashigar.
Duk wani cikas ga samar da man fetur zai yi tasiri mai tsanani ga tattalin arzikin duniya.
Ƙasar Sin ce babbar mai sayen mai daga Iran kuma tana da kyakkyawar alaka da Tehran.
Harin Iran: Amurka ta ɗebo ruwan dafa kanta Koriya ta Arewa za ta taimaka da gyara tashoshin nukiliyan Iran —Masani NAJERIYA A YAU: Matakan daƙile kisan matafiya a hanyoyin NajeriyaFarashin man fetur ya tashi bayan harin da Amurka ta kai kan cibiyoyin nukiliyar Iran, inda farashin man Brent crude ya kai matsayinsa mafi girma cikin watanni biyar.
Matakin rufe mashigar tekun Hormuz wadda kusan kashi 20 cikin ɗari na man fetur da iskar gas na duniya ke bi ta cikinta, zai iya jefa duniya cikin bala’in rashin mai.
Masani kan harkokin kasuwanci Gerrit Heinemann ya shaida wa kafar yaɗa labarai ta Daily Mail ta ƙasar Birtaniya, cewa idan Iran ta zaɓi rufe mashigar, sakamakon zai zama “bala’i.”
Mashigar hanya ce ta kasuwanci mai mahimmanci ga duniya, inda kusan kashi ɗaya cikin biyar na man fetur na duniya ke bi ta mashigar teku. Kazalika adadi mai yawa na iskar Gas Mai Ruwa (LNG), na bi ta mashigar, wanda hakan ya sa ta zama “mafi muhimmancin mashigar isar da man fetur a duniya.”
Kwamandan Rundunar Juyi Juya Halin Musulunci na Iran kuma ɗan majalisar dokokin ƙasar, Esmail Kosari ya bayyana cewa wannan matakin yana cikin ajandarsu kuma “za a yi shi duk lokacin da ya zama dole.”
A ƙarshen makon jiya Kowsari ya sanar cewa rufe mashigar tekun Hormuz “yana cikin matakan da gwamnatin ƙasar ke duba yiwuwar ɗauka, kuma Iran za ta yanke shawara da ya fi dacewa.”
Press TV ya ruwaito cewa matakin rufe mashigar tekun Hormuz bai kammala ba, har yanzu Majalisar Koli ta Tsaro ta Kasa ta Iran ce ke da hurumin yanke shawara ta ƙarshe kan lamarin.
Amma Kowsari ya bayyana cewa Iran ba ta iyakance iya matakin da za ta ɗauka a kan Isra’ila ba, kuma, “martanin soji wani yanki ne kawai na martaninmu gaba ɗaya.”
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Iran rufe mashigar tekun Hormuz
এছাড়াও পড়ুন:
Kasar Masar Tana Ta Zama Mai Shiga Tsakanin Iran Da IAEA Da Kuma Amurka
Ministan Harkokin wajen Masar Badr Abdelatty ya fara ayyukan diblomasiyya inda ya fara tattaunawa da Ministan harkokin wajen kasar Iran Abbas Araghchi dangane da farfado da tattaunawa kan shirin Iran na makamashin Nukliya tare da shugaban hukumar, IAEA Rafael Grossi, da kum wakilin Amurka na musamman a gabas ta tsakiya Steve Witkoff,. Amma a yanzun ba tare da barazana ko kuma kaiwa hare-hare ba.
Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya bayyana cewa wadannan bangarori biyu suna son Iran ta sake bada wata dama, don tattauna batun shiruin makamashin nukliya na kasar da kuma dangane da tashe tashen hankula a yankin yammacin Asia.
A dai dai lokacinda al-amura suke ci gaba da tarbarbarewa a yankin kasar masar ta sanya kanta a matsayin mai shiga tsakanin Iran da wadannan kasashen yamma.
Ministan harkokin wajen Iran yace a halin yannzu kuma bama dogaro da maganar Amurka don a sanda suka kaimana hare-hare bas u gaya mana ba.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Araqchi: Ba a kayyade wani lokacin shiga wata sabuwar tattaunawa da Amurka ba August 7, 2025 Ghana: Ministocin tsaro da muhalli sun rasa rayukansu a hatsarin jirgi mai saukar ungulu August 7, 2025 Jamus: Shahararrun mutane da ‘yan jarida sun bukaci a daina baiwa Israila makamai August 7, 2025 Gaza: Fararen hula 22 sun yi shahada a hare-haren Isra’ila a daren jiya August 7, 2025 Pezeshkian Ya Jaddada Wajabcin Haduwar Kasashen Musulmi Wajen Hana Laifukan Yaki A Gaza August 6, 2025 Araqchi Ya Taya Larijani Murnar Zama Sakataren Majalisar Kolin Tsaron Kasar Iran August 6, 2025 Japan: An Fara Juyayin Cikar Shekaru 80 Da Harin Amurka Na Makamin Nukiliya A Hiroshima August 6, 2025 Sudan: Dakarun RSF Sun Kashe Fararen Hula 14 Tare Da Jikkata Wasu Na Daban August 6, 2025 IRGC: Bayan yakin Kwanaki 12 Yanayi Ya Sauya Zuwa Ga Amfani Ga Iran August 6, 2025 ‘Yansanda A Iran Suna Amfani Da Kayakin Tsaro Na Zamani A Lokacin 40 August 6, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci