Aminiya:
2025-11-08@19:20:34 GMT

Amurka ta roƙi China ta sa baki kada Iran ta rufe mashigar tekun Hormuz

Published: 23rd, June 2025 GMT

Gwamnatin Amurka ta buƙaci ƙasar Sin da ta hana Iran rufe mashigar tekun Hormuz, ɗaya daga cikin muhimman hanyoyin jigilar kayayyaki a duniya.

Sakataren Harkokin Wajen Amurka Marco Rubio ya yi kiran ne bayan da kafar yada labarai ta Iran, Press TV ta ruwaito cewa majalisar dokokin ƙasar ta amince da shirin rufe mashigar.

Duk wani cikas ga samar da man fetur zai yi tasiri mai tsanani ga tattalin arzikin duniya.

Ƙasar Sin ce babbar mai sayen mai daga Iran kuma tana da kyakkyawar alaka da Tehran.

Harin Iran: Amurka ta ɗebo ruwan dafa kanta Koriya ta Arewa za ta taimaka da gyara tashoshin nukiliyan Iran —Masani NAJERIYA A YAU: Matakan daƙile kisan matafiya a hanyoyin Najeriya

Farashin man fetur ya tashi bayan harin da Amurka ta kai kan cibiyoyin nukiliyar Iran, inda farashin man Brent crude ya kai matsayinsa mafi girma cikin watanni biyar.

Matakin rufe mashigar tekun Hormuz wadda kusan kashi 20 cikin ɗari na man fetur da iskar gas na duniya ke bi ta cikinta, zai iya jefa duniya cikin bala’in rashin mai.

Masani kan harkokin kasuwanci Gerrit Heinemann ya shaida wa kafar yaɗa labarai ta Daily Mail ta ƙasar Birtaniya, cewa idan Iran ta zaɓi rufe mashigar, sakamakon zai zama “bala’i.”

Mashigar hanya ce ta kasuwanci mai mahimmanci ga duniya, inda kusan kashi ɗaya cikin biyar na man fetur na duniya ke bi ta mashigar teku. Kazalika adadi mai yawa na iskar Gas Mai Ruwa (LNG), na bi ta mashigar,  wanda hakan ya sa ta zama “mafi muhimmancin mashigar isar da man fetur a duniya.”

Kwamandan Rundunar Juyi Juya Halin Musulunci na Iran kuma ɗan majalisar dokokin ƙasar, Esmail Kosari ya bayyana cewa wannan matakin yana cikin ajandarsu kuma “za a yi shi duk lokacin da ya zama dole.”

A ƙarshen makon jiya Kowsari ya sanar cewa rufe mashigar tekun Hormuz “yana cikin matakan da gwamnatin ƙasar ke duba yiwuwar ɗauka, kuma Iran za ta yanke shawara da ya fi dacewa.”

Press TV ya ruwaito cewa matakin rufe mashigar tekun Hormuz bai kammala ba, har yanzu Majalisar Koli ta Tsaro ta Kasa ta Iran ce ke da hurumin yanke shawara ta ƙarshe kan lamarin.

Amma Kowsari ya bayyana cewa Iran ba ta iyakance iya matakin da za ta ɗauka a kan Isra’ila ba, kuma, “martanin soji wani yanki ne kawai na martaninmu gaba ɗaya.”

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Iran rufe mashigar tekun Hormuz

এছাড়াও পড়ুন:

Barazanar Amurka Na Kawo Wa Nijeriya Hari 

Sai dai, bisa batun gasakiya, karya ce tsagwaronta kan batun kisan kiyashin da ake yamadidin cewa, ana yiwa Kiristoci kisan gilla a Nijeriya.

Bugu da kari, wannan batun ana wani yunkuri ne na son kawo rudadi a kasar nna, musamman duba da cewa, masu son kawo rudadin, a zahiri, sun jahilci irin yanayin sarkakiyar lamarin tsaro na kasar nan.

Wannan Jaridar, ta sha yin tsokaci, kan kalubalen rashin tsaro da ke addabar kasar nan, tare da kuma yawan gabatar da kira ga Gwamnatin kasar da ta tashi tsaye, domin daukar matakan da suka dace, na kare rayuka da dukiyoyin ‘yan Nijeriya.

Batun aikata ta’addanci, yin garkuwa da mutane da kuma aukuwar rikici a tsakanin manoma da makiyaya, matsaloli ne, da ke shafar kowannen dan Nijeriya, wanda kuma Trump da masu ba shi shawara, suka jahilci hakan, musammman duba da cewa, akasarin wadannan matsalalin, na aukuwa Musulmi da Kirista ne.

Wani abin duba wa a nan shi ne, akasarin hare-haren ‘yan ta’addara Boko Hrama na kai wa kan Musulmi da ke Arewacin Nijeriya, wanda Trump, ya kafa hujar da cewa, ana kashe Kiristoci ne, inda kuma hare-haren, suka nuna cewa, anfi hallaka Musulmai, fiye da Kiristoci.

Ayyana matsalar tsaron kasar da Trump ya yin a yi wa Kiristoci kisan kare dangi wani abu ne, da yake da matukar hadari.

Martanin da shugaba Bola Tinubu ya mayarwa da Trump kan wannan ikirarin na sa, abu ne da ya dace, musamman cewar da ya yi a Nijeriya ana bai wa kowanne dan kasar, ‘yancin yin addininsa, ba tare da wata tsangwama ba, musamman kamar yadda kundin tsarin mulkin kasar, ya tanadar.

Bugu da kari, idan har Trump na nuna damuwa kan ikirarinsa na ana yi wa Kiristocin kasar kisan gilla, to su kuma Kiristocin da aka hallak a zirin Gaza biyo bayan hare-haren kasar Isra’ila fa?

Kuma mai ya sa ba zai yi amfani da karfin ikon gwamnatinsa na dakatar da yakar kasar Ukraine, da kasar Rasha ke ci gaba da yi ba, duba da yadda aka kashe dubban Kiristoci a kasar?

Amsar a nan ita ce, Trump ba wai na da nufi bai wa Kiristocin kasar nan kariya bane, wani bakar manufa ce kawai da yake son cimma burinsa.

Tarihi ba zai sanya mu yi saurin manta wa da mamayar da Amurka ta yiwa kasar Afghanistan a 2001 ba don kifar da gwamnatin Taliban wadda ta alakantan, a matsayin ‘yan ta’adda.

A lokacin mamayar, sama da mutane 200,000 ne, suka rasa rayukansu, amma duk da hakan, Taliban ta sake dawo wadda a yanzu, ta ke ci gaba da jan ragamar shugabancin kasar.

Kazalika, Amurka ta mamaye kasar Iraki a 2003, ta cere shugaban sojin kasar kasa marigayi Saddam Hussein, inda sama da mutane 150,000 suka rasa rayukansu sabo da hare-haren Amurka.

Hakazalika, ta kai wata mamayar a kasar Lbiyia ta cere marigayi Gaddafi, wanda har yanzu, kasar ba ta saitu ba, inda kuma burbushin yakin na Lbiya ya haifar da shigar makamai cikin kasar nan da ‘yan Boko Haram da ‘yan bindiga daji da kuma wasu Fulani ke yin amfani da su, wajen kai hare-hare a Nijeriya.

Yin amfani da karin soji da Amurka ta yi barazanar yi kan Nijeriya ba sanya matsalar tsaron kasar nan, ta kau ba, sai dai ma, kara tabarbarar da tsaron kasar.

Idan har da gaske Amurka ta ke yi na taimaka wa Nijeriya ta magance kalubalen rashin tsaronta ba ta hanyar barazana ya kamata ta bullowa kasar ba, kamata ya yi ta taimaka wa Nijeriya da kudade da makamai domin kawo karshen matsalar da kuma yin musayar bayanan sirri.

Amma yi wa Nijeriya wannan barazar, tamkar wani cin fuska ne.

A zahiri barazanar ta Trump, ba wai yana nufin bai wa Kiristocin Nijeriya kariya bane, amma wani salon na ne kawai na son nuna karfin iko da kuma son kawo rabuwar kanuwanan ‘yan Nijeriya.

Ya kamata Trump ya mayar da hankali kan matsalolin da ke ci gaba da addabar kasarsa ne, ba wai yin shiga sharo ba shanu, kan batun da ya shafi Nijeriya ba.

Sai dai, a nan za mu iya cewa, wannan barazar ta sa, dole ne ta zama wata ankawarar ga masu rike da madafun iko a kasar nan, wajen lalubo da mafita kan matsalar tsaro da kasar da kasar ke ci gaba da fuskanta.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Manyan Labarai Gwamnatin Tarayya Ta Amince da Gina Sabbin Gidaje Ga Alƙalai, Da Samar Da Ruwa A  FCT November 6, 2025 Manyan Labarai Amurka Ta Yi Barazanar Ƙwace Kadarorin Ƙungiyoyin Makiyaya A Nijeriya  November 6, 2025 Manyan Labarai Za Mu Ƙara Ƙaimi Wajen Kai Wa ‘Yan Bindiga Hare-Hare Ta Sama – Hafsan Sojin Sama November 6, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Dan Wasan Taekwando Na Kasar Iran Abulfazl Zandi Ya Zamo Shi Ne Na Daya A Duniya
  • Jamhuriyar Musulunci Ta Iran Ta Tabbatar Da Hannun Amurka Wajen Kaddamar Da Yaki Kanta
  • Karuwar Matsalar Jin Kai Mafi Girma A Duniya A Sudan Saboda Ci Gaba Da Masifar Yaki A Kasar
  • Barazanar Amurka Na Kawo Wa Nijeriya Hari 
  • Mun fara tattaunawa da Amurka kan barazanar Trump – Gwamnatin Tarayya
  • Araqchi Ya Ce: Harin Amurka Kan Kasar Venezuela Ya Bayyana Karara Duniya Tana Gani
  • Ƙungiyyar Ƙwallon yashi ta Kada BSC ta fatattaki Kebbi BSC
  • Iran, China da Rasha sun tattauna gabanin taron Kwamitin Gwamnonin IAEA
  • Najeriya ta yi watsi da sanya sunanta cikin jerin kasashen da ake tauye ’yancin addini
  • Gwamnatin Tarayya ta fara shirin sayar da matatun manta ga ’yan kasuwa