Harin Amurka A Wurare 3 Na Nukiliyar Iran: Babu Wani Lahani A Harin Bama-baman – Iran
Published: 22nd, June 2025 GMT
Trump ya ce hare-haren da Amurka ta kai kan cibiyoyin nukiliyar Iran guda uku, lallai zai kara rura wutar rikici a ci gaba da yakin da ake yi tsakanin Iran da Isra’ila.
Sai dai ministan harkokin wajen Iran Seyed Abbas Araghchi ya yi Allah wadai da harin da Amurka ta kai da cewa “abin takaici ne” sannan ya ce Iran ta tanadi “dukkan zabin kare ‘yancinta”, yana mai jaddada cewa Amurka za ta fuskanci “tsauraran sakamako”.
Araghchi ya kara da cewa, Amurka ta keta kundin tsarin mulkin Majalisar Dinkin Duniya a matsayinta na mamba a kwamitin sulhu na Majalisar Dinkin Duniya.
Bugu da kari, wani dan Majalisar kasar Iran, ya kara da cewa, “babu wani mummunan lahani a wuraren, kuma dama tun kafin harin, an riga an kwashe duk wasu abubuwa masu muhimmanci na tashoshin nukiliyar”.
Tun da farko, Tehran ta yi gargadin cewa za ta kai hari kan muradun Amurka a yankin Gabas ta Tsakiya domin daukar fansa kan duk wani hari da Amurka ta kai, kuma ya zuwa yanzu ta harba makamai masu linzami kan Isra’ila, inda aka ji karar fashewar wasu abubuwa a birnin Kudus.
A halin da ake ciki, kawunan ‘yan majalisar dokokin Amurka ya rabu dangane da shigar kasar, inda ‘yan jam’iyyar Republican suka yabawa Trump, yayin da ‘yan jam’iyyar Democrat suka yi gargadin cewa an jefa Amurka cikin wani yakin da ba nata ba.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
HKI Ta Kai Hare-Hare Kan Wurare Har 5 A Kudancin Kasar Lebanon
HKI ta kai hare-hare kan wurare 5 a kudancin kasar Lebanon a jiya Alhamis.
Tashar talabijin Al-mayadeen ta kasar Lebanon ta bayyana cewa kafin hare-haren yahudawan sun bada sanarwan cewa zasu kai hare-hare kan warare uku a gudancin kasar ta Lebanon a jiya Alhamis kuma sune Meis al-Jabal, Debbine, da kuma Kafar Tebnit.
Mai aikawa tashar talabijin ta kasar Lebanon rahoto daga kudancin kasar ta bayyana, amma a lokacinda ta fara kai hare-hare jiragen yakin da ake sarrafawa daga nesa, suka fara shawagi a kan wadan nan wurare, suna ayyukan leken asiri. Sannan bayana wani lokacin makaman Drones suka ketasararin samaniya kasar Lebanon suka kai hare-hare har guda biyu a kan garin Meisal-Jabal, inda ya jiyamutum guda rauni.
Yar rahoton Al-mayadden a kudancin Lebanon ta bayyana cewa bayan haka jiragen ‘Drones’ su sake shigowa kudancin kasar suka kai hare-hare a wannan karon kan gidajen mutane a Kafar Tebnit da lardin Nabatieh. Sun kumakaihare-hare kan garin Debbine a can kuryar kudancin kasar.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Majiyoyin Diblomasiyya Sun Ce Washington Zata Jagoranci Turawa A Tattaunawa Da Iran September 19, 2025 Iran Ta Bukaci Kwamitin Tsaro Na MDD Ta Zabi Diblomasiyya Kan Fito Na Fito September 19, 2025 Yahudawa Suna Ci Gaba Da Yin Hijira Zuwa Wajen HKI September 18, 2025 ‘Yan Gwgawarmaya Sun Kashe Sojojin HKi 4 A Gaza September 18, 2025 An Halaka Sojojin HKI Biyu Ta Hanyar Sukarsu Da Wuka A Kusa Da Iyakar Jordan September 18, 2025 Husi: Kai Wa Kasar Katar Hari Gargadi Ne Ga Al’ummar Musulmi September 18, 2025 Shugaban Kasar Iran Ya bayyana Yadda Hadin Gwiwa Tsakanin Iran Da Rasha Ya Kawo Ci Gaba Tsakaninsu September 18, 2025 Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Ce: Iran Ta Sauke Hakkin Da Ya Hau Kanta Sauran Bangaren Turai September 18, 2025 Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Iran Ya Ce: Masu Goyon Bayan Isra’ila Suna Da Hannu A Laifukanta September 18, 2025 Sojojin Mamayar Isra’ila Sun Cika Kwanaki 713 Suna Kisan Kiyashi A Zirin Gaza September 18, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci