Aminiya:
2025-09-24@12:49:06 GMT

Za mu sake gina kasuwar waya ta Farm Center — Abba

Published: 22nd, June 2025 GMT

Gwamnan Kano Kano, Abba Kabir Yusuf, ya yi alƙawarin sake gina kasuwar waya ta Farm Center da ta yi gobara a kwanakin baya.

Hakan na kunshe cikin wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Sunusi Bature Dawakin Tofa ya fitar a ranar Asabar.

Amurka ta ƙaddamar da hare-hare kan Iran Za mu ci gaba da yi wa Isra’ila luguden wuta — Shugaban Iran

Sanarwar ta ce bayan ziyarar gani da ido da gwamnan ya yi a ranar Juma’a, ya ɗauki matakin sake gina kasuwar tare da sabunta ta da zamanantar da ita, aikin da da ya ce “gwamnan zai kashe naira biliyan 2.

“Wannan yunƙuri ba kawai saboda gobarar ba ce, za mu yi amfani da wannan damar ne domin inganta tattalin arzikin jihar, da samar da ayyukan yi,” kamar yadda sanarwar ta bayyana.

Sanarwar ta ƙara da cewa gwamnatin jihar za ta saya ƙarin fili domin faɗaɗa kasuwar, inda za ta samu damar gina abubuwan da ake buƙata a kasuwa na zamani, ciki har da gina sashen masu kashe gobara domin jiran kar-ta-kwana.

“Ba kasuwa kawai za mu gina ba, cibiyar kasuwanci za mu gina domin jawo ’yan kasuwa daga ƙasashen duniya,”in ji shi.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Farm Center Gobara Jihar Kano

এছাড়াও পড়ুন:

Bayan Sulhu  Da Ƴan Bindiga, An Saki Mutane 70 Da Aka Yi Garkuwa Da Su A Katsina

Mutune 70 da aka yi garkuwa da su sun samu ƴanci a Jihar Katsina, bayan yarjejeniyar sulhu da aka ƙulla da fitaccen shugaban ƴan bindiga, Isiya Kwashen Garwa. A wani faifan bidiyo da ya bayyana, Garwa ya saki mutane 40 a ƙaramar hukumar Faskari, kwanaki biyu bayan ya fara sakin wasu 30, wanda hakan ya kai adadin zuwa 70 gaba ɗaya.

Rahotanni daga mazauna yankin sun ce sakin na baya-bayan nan ya biyo bayan tattaunawa tsakanin shugabannin al’umma da sansanin Garwa, a wani mataki da ake ganin zai rage tashin hankali da hare-hare a yankin. Duk da haka, Garwa ya nuna rashin jin daɗi kan abin da ya kira sumamen Sojoji a unguwar Ruwan Godiya a lokacin Sallar Juma’a, inda ya yi zargin cewa wasu Hausawa da Fulani sun samu raunuka. Ya gargaɗi cewa irin waɗannan hare-hare na iya rusa sulhun da aka ƙulla.

Abubuwan Da Ba A Faɗa Ba Game Sulhu Da Ƴan Bindiga A Katsina An Cafke Wani Magidanci Da Lafin Sojan Gona A Katsina

Hukumomin jihar ba su fitar da wata sanarwa ba kan sumamen da ake zargin ba, sai dai majiyoyin tsaro sun ce an kai hare-haren ne kan maboyar ƴan ta’adda tare da nufin kare rayukan jama’a. Mutanen da aka sako, galibinsu manoma ne da aka sace daga ƙauyukan karkara a Faskari, suna cikin kulawar likitoci da kuma binciken tsaro kafin a mayar da su wurin iyalansu.

Gwamnatin jihar ta ce tattaunawa tana daga cikin dabarun tsaro da ake amfani da su, amma ta jaddada cewa dole ne ƴan bindiga su miƙa makamansu gaba ɗaya tare da fuskantar hukunci kan laifuffukan da suka aikata.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sojoji Sun Kashe ‘Yan Ta’adda, Sun Kama Masu Laifi
  • Xi Ya Bukaci Hada Karfi Da Karfe Wajen Gina Yankin Xinjiang Ya Zama Mafi Kyau
  • An kama ɗan sandan bogi a Kano
  • Sojoji Sun Daƙile Hare-haren ISWAP, Sun Bai Wa Magidanta 10,000 Kariya A Borno
  • Iran Da Rasha Zasu Rattaba Hannun Kan Batun Gina Wasu Tashoshin Nukiliya.
  • Taron Canada: Haɗin Gwiwa Afirka Ke Buƙata Ba Agaji Ba – Gwamnan Zamfara 
  • Bayan Sulhu  Da Ƴan Bindiga, An Saki Mutane 70 Da Aka Yi Garkuwa Da Su A Katsina
  • Iran Da Pakistan Sun Sake Tsara Dangantakarsu Ta Tattalin Arziki
  • Gwamnan Gombe ya bai wa maharba kyautar motoci da babura don bunƙasa tsaro
  • ’Yan sanda sun kama mutane 5 kan zargin satar abincin yara a Borno