Aminiya:
2025-06-22@11:09:49 GMT

Za mu sake gina kasuwar waya ta Farm Center — Abba

Published: 22nd, June 2025 GMT

Gwamnan Kano Kano, Abba Kabir Yusuf, ya yi alƙawarin sake gina kasuwar waya ta Farm Center da ta yi gobara a kwanakin baya.

Hakan na kunshe cikin wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Sunusi Bature Dawakin Tofa ya fitar a ranar Asabar.

Amurka ta ƙaddamar da hare-hare kan Iran Za mu ci gaba da yi wa Isra’ila luguden wuta — Shugaban Iran

Sanarwar ta ce bayan ziyarar gani da ido da gwamnan ya yi a ranar Juma’a, ya ɗauki matakin sake gina kasuwar tare da sabunta ta da zamanantar da ita, aikin da da ya ce “gwamnan zai kashe naira biliyan 2.

“Wannan yunƙuri ba kawai saboda gobarar ba ce, za mu yi amfani da wannan damar ne domin inganta tattalin arzikin jihar, da samar da ayyukan yi,” kamar yadda sanarwar ta bayyana.

Sanarwar ta ƙara da cewa gwamnatin jihar za ta saya ƙarin fili domin faɗaɗa kasuwar, inda za ta samu damar gina abubuwan da ake buƙata a kasuwa na zamani, ciki har da gina sashen masu kashe gobara domin jiran kar-ta-kwana.

“Ba kasuwa kawai za mu gina ba, cibiyar kasuwanci za mu gina domin jawo ’yan kasuwa daga ƙasashen duniya,”in ji shi.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Farm Center Gobara Jihar Kano

এছাড়াও পড়ুন:

Amurka za ta gamu da fushinmu kan shigar wa Isra’ila yaƙinta da Iran — Houthi

’Yan tawayen Houthi na Yemen sun yi barazanar cewa Amurka za ta gamu da fushinsu muddin ta kai wa Iran hari a rikicin da ya ɓarke tsakaninta da Isra’ila.

’Yan tawayen sun ce za su kai wa jiragen ruwan Amurka hare-hare a Tekun Bahar Rum, idan har Washington ta yi kuskuren shiga yaƙin da Isra’ila ta ƙaddamar wa Iran, duk kuwa da yarjejeniya tsagaita wuta da aka cimma a baya-bayan nan.

Mahaifin Rahama Sadau ya rasu Za mu sake gina kasuwar waya ta Farm Center — Abba

A cikin wani faifan bidiyo, kakakin ’yan tawayen Houthi Yahya Saree ya bayyana cewa, muddin Amurka ta kai wa Iran hari ko kuma ta shiga cikin wannan rikici, mayankansu za su ƙaddamar da farmaki kan muradun Amurkar da suka haɗa da jiragen yaƙi da kuma jiragen dakon kaya da ke zirga-zirga a Tekun Bahar Rum.

Wannan barazana ta ’yan tawayen Houthi na zuwa ne a daidai lokacin da shugaban Amurka Donad Trump ya saka wa’adin makonni biyu domin yanke shawara a game da yiwuwar shiga rikicin da ya ɓarke tsakanin Isra’ila da Iran inda aka shiga mako na biyu suna yi wa juna ruwan bama-bamai.

Sai dai kuma tuni Amurkan ta ƙaddamar da hare-hare kan wasu cibiyoyin nukiliyar Iran kamar yadda Shugaba Donald Trump ya bayyana a daren Asabar wayewar gari Lahadi.

 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Amurka za ta gamu da fushinmu kan shigar wa Isra’ila yaƙinta da Iran — Houthi
  • Hikimar Yunƙurin Sake Farfaɗo Da Noman Filanten A Jihar Nasarawa
  • Kiran Gwamnatin Tarayya Ga ‘Yan Jarida: Ku Zama Jigo Wajen Gina Dimokuraɗiyyar Nijeriya
  • Amurka ta ƙaddamar da hare-hare kan Iran
  • Uba Sani ya yi jajen ’yan ɗaurin aure 12 da aka kashe a Filato
  • Rikicin Filato: An sake kashe mutum 17 a Mangu da Bokkos
  • An Nemi A Kafa Dokar Ta-ɓaci Kan Masu Ƙwacen Waya
  • Indomie Arewa Ta Ƙaddamar da AI Career Generator Domin Ranar Yara
  • Ba zai yiwu mu bar Khamenei a raye ba — Isra’ila