Tottenham Da West Ham Sun Nuna Sha’awar Daukar Dan Wasan Nijeriya Raphael Onyedika
Published: 21st, June 2025 GMT
Manyan kungiyoyin kwallon kafa a Turai Tottenham Hotspur da West Ham United na fafatawa wajen ganin sun dauki tauraron dan wasan Nijeriya dake buga kwallo a Club Brugge, Raphael Onyedika, ana alakanta Onyedika da barin kungiyar Club Brugge sakamakon rawar gani da ya taka a bana.
Dan wasan na Nijeriya ya samu dimbin masu sha’awar raba shi da Brugge saboda bajintar da ya nuna a gasar cin kofin zakarun nahiyar Turai ta bara, a cewar Transferfeed, kungiyoyin biyu na son siyan dan wasan tsakiyar a wannan bazarar, West Ham na son ya maye gurbin Tomas Soucek dan kasar Czech, wanda ke kan hanyarsa ta barin kungiyar.
A daya bangaren kuma kungiyar Tottenham na son kara yawan yan wasanta na tsakiya bayan ta kare a mataki na 16 a gasar Firimiya a kakar wasan da ta gabata, hakazalika babbar kungiyar kwallon kafa ta AC Milan ta nuna sha’awarta ta sayen dan wasan mai shekaru 24, kadan ya rage Onyedika ya bar Brugge zuwa kungiyar Galatasaray ta Turkiyya a bazarar da ta gabata amma kuma sai ya ci gaba da zama a kungiyar.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
Ministan Harkokin Wajen Iran ya isa taron Kungiyar OIC a Turkiyya
Wakilin ƙasar Iran ya isa birnin Santanbul na ƙasar Turkiyya domin halartar taron Ƙungiyar Haɗin kan Kasashen Musulmi (OIC) a ranar Asabar.
Kamfanin dillancin labarai na Tasnim ya ruwaito cewa, a yayin taron Ministan Harkokin Wajen Iran, Abbas Araghchi, zai gana da jami’an diflomasiyya na ƙasashen Larabawa don tattauna batun rikicin da ke ƙara ƙamari tsakanin ƙasarsa da Isra’ila.
Kimanin jami’an diflomasiyya 40 ne ake sa ran za su halarci taron a daidai lokacin da Isra’ila da Iran ke ci gaba da musayar hare-haren makamai masu linzami.
“Ministan harkokin wajen ya isa Istanbul a safiyar yau domin halartar taron ministocin harkokin wajen kungiyar hadin kan Musulunci,” in ji Tasnim.
Yadda Iran ta lalata cibiyar kimiyya mafi muhimmanci a Isra’ila Najeriya ta tura sojoji domin samar da zaman lafiya a GambiaWannan ziyarar ta zo ne bayan da Ministan ya gana da takwarorinsa daga Biritaniya, Faransa, da Jamus a Geneva a ranar Juma’a.
A cewar kamfanin dillancin labaran, “A wannan taron, bisa shawarar Iran, za a tattauna batun harin da gwamnatin Isra’ila ta kai wa kasarmu musamman,” in ji Araghchi.
Isra’ila ta fara farmakinta ne a safiyar 13 ga watan Yuni, tana mai cewa Iran tana dab da ƙera makaman nukiliya.
Wannan ya haifar da martani nan take daga Tehran, a rikici mafi mubi da aka taɓa fuskanta tsakanin kasashen biyu masu zaman doya da manja.
Tun da farko a ranar Juma’a, Araghchi ya bayyana cewa Iran a shirye take ta “sake duba harkokin diflomasiyya” idan har “aka dakatar da hare-haren Isra’ila.”
Ana sa ran ministocin ƙasashen Larabawa za su fitar da sanarwa bayan ganawarsu, in ji kamfanin dillancin labarai na ƙasar Turkiyya Anadolu.