HausaTv:
2025-05-01@03:59:12 GMT

Kasashen Turai sun goyi bayan shirin Larabawa na sake gina Gaza

Published: 9th, March 2025 GMT

Manyan kasashen Turai, da suka hada da Burtaniya, Faransa, Jamus, da Italiya, sun goyi bayan shawarar Masar na sake gina Gaza a matsayin mai adawa da shirin “riviera” na shugaban Amurka Donald Trump wanda ke ba da shawarar korar Falasdinawa da karfi daga yankin.

Duk da goyon bayansu da kuma wanke ayyukan kisan kare dangi da Isra’ila ke yi a zirin Gaza tun farkon yakin a watan Oktoban 2023, ministocin harkokin wajen Birtaniya, Faransa, Jamus, da Italiya sun sanar a cikin wata sanarwa a ranar Asabar cewa sun amince da shirin Masar wanda zai inganta “mummunan yanayin rayuwa da Falasdinawa suke ciki a Gaza.

Sanarwar ta kara da cewa, “Shirin ya nuna wata hanya ta sake gina Gaza idan aka aiwatar da hakan cikin gaggawa.

A ranar Asabar ne kungiyar hadin kan kasashen musulmi ta OIC mai mambobi 57 ta amince da shawarar kungiyar hadin kan kasashen Larabawa a hukumance kan sake gina Gaza a wani taron gaggawa da ta gudanar a kasar Saudiyya.

OIC ta bukaci “kasashen duniya da cibiyoyin bayar da kudade na kasa da kasa da na shiyya-shiyya da su gaggauta ba da tallafin da ya dace ga shirin.”

Wani cikakken daftarin shirin sake gina Gaza da Masar ta gabatar ya hada da ware dala biliyan 53 don sake gina gina yankin, da kuma batun kafa kwamitin gudanarwa domin tafiyar da yankin zirin Gaza.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Iran Da Iraki Sun Ce An Kammala Shimfida Layin Dogo Daga Shalamcheh Zuwa Basra

A wani taro wanda ya hada ministan riko na tattalin arziki da kudade na JMI da kuma mai bawa firai ministan kasar Iraki shawara, bangarorin biyu sun tabbatar da cewa an kammala aikin shimfida layin dogo tsakanin garin Shalamcheh na kasar Iran da kuma birnin Basra a kasar Iraki.

Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya nakalto jami’an gwamnatocin kasashen biyu na fadar haka, sun kuma jaddada muhimmancin layin dogon da kuma samar da kasuwar babu kudaden fito a kan iyakokin kasashen biyu.

Labarin ya kara da cewa harkokin kasuwanci tsakanin kasashen biyu ya zuwa yanzu ya kai dalar Amurka biliyon $11a ko wace shekara kuma anan saran nan gaba zai iyakaruwa zuwa dalar Amurka biliyon $25.

Rahmatollah Akrami, ministan riko na tattalin arziki da kudade na JMI, da kuma Hazem Majid Naji Al-Khalidi mai bawa firai ministan kasar Iraki shawara sun jaddada muhimmancin kammala layin dogo tsakanin kasashen biyu, da kuma kasuwar ba kudaden fito tsakanin kasashen biyu. Da kuma fatan zasu yi kokarin amfanar juna gwagwadon abinda zasu iya.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Araghchi : Za’ayi Tattaunawar Iran da Amurka ta gaba a Rome bayan taron E3
  • Iran ta sha alwashin ci gaba da aiwatar da manufofinta na raya dangantakarta da Nijar
  • Yadda ’yan Tifa da baƙin direbobi ke haddasa haɗari a Abuja
  • Iran Da Iraki Sun Ce An Kammala Shimfida Layin Dogo Daga Shalamcheh Zuwa Basra
  • Saudiya Ta Yi Allawadai Da Kissan Kiyashin Da HKI Take Yi A Gaza A Gaban Kutun ICJ
  •  Falasdinawa 40 Sun Yi Shahada A Cikin Sa’oi 24 A Gaza
  • Xi Jinping Ya Ziyarci Sabon Bankin Raya Kasashen BRICS
  • Karin Wata Kasa Da Bai San Ta Ba A Doron Duniya
  • Shugaban Kasar Yana Maraba Da Masu Zuba Hannun Jari A Kasarsa Daga Kasashen Waje
  • Majalisar Dinkin Duniya Ta Jaddada Wajabcin Komawa Kan Shirin Tsagaita Bude Wuta A Gaza