Kasashen Turai sun goyi bayan shirin Larabawa na sake gina Gaza
Published: 9th, March 2025 GMT
Manyan kasashen Turai, da suka hada da Burtaniya, Faransa, Jamus, da Italiya, sun goyi bayan shawarar Masar na sake gina Gaza a matsayin mai adawa da shirin “riviera” na shugaban Amurka Donald Trump wanda ke ba da shawarar korar Falasdinawa da karfi daga yankin.
Duk da goyon bayansu da kuma wanke ayyukan kisan kare dangi da Isra’ila ke yi a zirin Gaza tun farkon yakin a watan Oktoban 2023, ministocin harkokin wajen Birtaniya, Faransa, Jamus, da Italiya sun sanar a cikin wata sanarwa a ranar Asabar cewa sun amince da shirin Masar wanda zai inganta “mummunan yanayin rayuwa da Falasdinawa suke ciki a Gaza.
Sanarwar ta kara da cewa, “Shirin ya nuna wata hanya ta sake gina Gaza idan aka aiwatar da hakan cikin gaggawa.
A ranar Asabar ne kungiyar hadin kan kasashen musulmi ta OIC mai mambobi 57 ta amince da shawarar kungiyar hadin kan kasashen Larabawa a hukumance kan sake gina Gaza a wani taron gaggawa da ta gudanar a kasar Saudiyya.
OIC ta bukaci “kasashen duniya da cibiyoyin bayar da kudade na kasa da kasa da na shiyya-shiyya da su gaggauta ba da tallafin da ya dace ga shirin.”
Wani cikakken daftarin shirin sake gina Gaza da Masar ta gabatar ya hada da ware dala biliyan 53 don sake gina gina yankin, da kuma batun kafa kwamitin gudanarwa domin tafiyar da yankin zirin Gaza.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Iran Da Kasashen Afrika Sun Daura Dammarar Karfafa Alakar Kimiyya Tsakaninsu
A cikin wani taron hadin guiwa da aka yi takanin iran da sauran jakadun kasashen afrika guda 19 da sauran jami’an kasar iran, sun jadadda game da muhimmancin yin aiki tare a bangaren ilimi, bincike da kuma kiwon lafiya, da kuma yadda zaa kara karfafa alaka tsakanin Iran da kuma nahiyar Afrika.
Taron ya nuna irin ci gaban da aka samu daga yin aiki tare na lokaci bayan lokaci zuwa hadin guiwa da iran ta hanyar ilimi da kiwon lafiya, da kuma yin aiki tare a bangaren kimiya da nahiyar Afrika, wannan abin da aka kirkiro zai tunkari barazanar da ake fuskanta na yaduwar cututtuka, karancin magani da kuma ayyukan lafiya a yankunan karkara a Afrika.
Jami’ar llimin likitanci ta birnin Tehran ta ce ba wai kawai ta dauki kanta a matsayin jigo a bangaren ilimi ba ne, har ma a matsayin wata madogara wajen ayyukan kiwon lafiya na kasa, wanda zai iya jurewa takunkumi, ta hanyar bude dakunan gwaje-gwaje, cibiyoyin bincike da kuma shirye shiryen ilimi ga abokan hulda a Afrika,
Iran tana son gina gada mai tsawo ta yin hadin guiwar kimiyya da nahiyar Afrika.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Ecowas Ta Tura Sojoji Zuwa Jamhuriyar Benin Don Dakile Juyin Mulki December 8, 2025 IRGC: Makaman Iran Sun Fada Kan Matatan Man Haifa Har Sau Biyu A Yakin Kwanaki 12 December 8, 2025 Najeriya: Gwamnatin Tarayya Ta Bada Sanarwan Kubutar Da Yan Makaranta 100 Da Aka Sace December 8, 2025 Iraki Ta Musanta Cewa Ta Tushe Asusun Hizbullah Da Ansarallah December 8, 2025 Sabon Fada Ya Barke A Tsakanin Thailand Da Cambodia December 8, 2025 Iran Ta Yi Allawadai Da Kisan Fararen Hula A Kasar Sudan December 8, 2025 Macron Na Faransa Ya Yi Wa Najeriya Alkawalin Taimakawa Akan Matsalolin Tsaro December 8, 2025 Rasha Ta Yi Maraba Da Cire Sunanta A Matsayin ” Barazanar Da Amurka Teke Fuskanta December 8, 2025 Majid Majidi Na Iran Ya Sami Kyauyar Girmamawa Daga Cibiyar Fina-finai Na “Eurasia Dake Kasar Rasha December 8, 2025 Benin : Har yanzu Shugaba Patrice Talon ne a kan mulkin_fadar shugaban kasa December 7, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci