Aminiya:
2025-09-24@09:55:55 GMT

Bio ya maye gurbin Tinubu a matsayin sabon shugaban ECOWAS

Published: 23rd, June 2025 GMT

Shugaban Ƙasar Saliyo, Julius Maada Bio, ya zama sabon shugaban Ƙungiyar Raya Tattalin Arziƙin Ƙasashen Yammacin Afirka (ECOWAS), inda ya karɓi ragamar shugabancin daga Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu.

An sanar da hakan ne a taron shugabannin ECOWAS karo na 67 da aka gudanar a Abuja.

An kashe matar aure, manomi ya jikkata a wani sabon hari a Kaduna ’Yan bindiga sun sace babban alƙali a Bayelsa 

Shugaba Tinubu, wanda ya yi wa’adin shugabancin ƙungiyar sau biyu tun daga shekarar 2023, ya bayyana cewa shugabancin ECOWAS babban abu ne a rayuwarsa.

Ya ce: “Yayin da nake miƙa ragamar shugabanci ga abokina kuma ɗan uwana, Shugaba Julius Maada Bio, ina mai gamsuwa da fatan alheri ga makomar Yammacin Afirka.”

Ya ƙara da cewa wajibi ne ƙasashen yankin su haɗa kai wajen tabbatar da zaman lafiya, ci gaban dimokuraɗiyya da kuma bunƙasa tattalin arziƙi.

“Mu ƙara inganta haɗin kai, mu mutunta ƙa’idojin diflomasiyya, sannan mu tabbatar da ci gaba wanda zai haɗa kowa da kowa musamman matasa, mata da waɗanda ke cikin mawuyacin hali,” in ji Tinubu.

A jawabinsa na karɓar shugabanci, Shugaba Bio ya gode wa Tinubu bisa jagoranci mai cike da hangen nesa da kyakkyawan fata.

Ya ce: “Shugabancinka a ECOWAS ya nuna jajircewa wajen ƙarfafa tattaunawar yankin, farfaɗo da tattalin arziƙi da wanzar da zaman lafiya.

“Na ji kaina a matsayin mai ɗaukar wannan nauyi domin ci gaba daga inda ka tsaya.”

Shugaba Bio ya bayyana cewa akwai buƙatar ECOWAS ta ƙara dagewa wajen kare dimokuraɗiyya, inganta tsaro da bunƙasa tattalin arziƙi.

“Dole mu sake fasalin ECOWAS ta yadda za ta zama mai gaskiya, inganci da amsa buƙatun al’ummarta,” in ji shi.

Ya kuma bayyana matsalolin da yankin ke fuskanta kamar ta’addanci, taɓarɓarewar siyasa da matsin tattalin arziki.

Ya ce: “Fagen dimokuraɗiyya yana fuskantar ƙalubale a sassa daban-daban na yankin. A wasu ƙasashe, tsarin mulki ya rikiɗe.

“Amma matasa na faɗin Yammacin Afirka na buƙatar ba kawai zaɓe ba, har ma da gaskiya, da ba su damar shiga cikin tafiyar da rayuwar ƙasa.”

Hakazalika, Bio ya ce zai yi jagoranci ECOWAS cikin gaskiya da fifita buƙatun al’umma tare da inganta haɗin kan yankin.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: ECOWAS

এছাড়াও পড়ুন:

Ya Kamata Sin Da Amurka Su Hau Turbar Hadin Gwiwa Da Samun Moriyar Juna A Sabon Lokaci

A daren ranar 19 ga wannan wata, shugaban kasar Sin Xi Jinping da takwaransa na kasar Amurka Donald Trump sun tattauna ta wayar tarho, inda shugaba Xi ya jaddada cewa, alakar Sin da Amurka na da matukar muhimmanci, Sin da Amurka na iya cimma nasarar bai daya da wadata tare, ta yadda za su amfani kawunansu, da ma sauran sassan duniya baki daya. A nasa bangare kuwa, shugaba Trump cewa ya yi, alakar Amurka da Sin ita ce mafi muhimmancin dangantaka a duniya, yana mai cewa, aiki tare tsakanin kasashen biyu ka iya haifar da manyan abubuwa da za su ingiza zaman lafiya da daidaito a duniya. Ya yi fatan wanzar da babbar dangantaka mai armashi ta dogon lokaci tsakanin kasarsa da Sin.

A cikin wannan tattaunawar, shugaba Xi ya bayyana ra’ayi da matsayin Sin kan batutuwan dake shafar dangantakar kasashen biyu, ya yi nuni da cewa, ya kamata Sin da Amurka su yi kokari da hadin gwiwa, kana kasar Amurka ta magance daukar matakan kayyade ciniki daga bangare daya, ta haka za a magance kawo illa ga nasarorin da kasashen biyu suka samu yayin shawarwarinsu a zagaye da dama. Game da batun TikTok, ana son ganin kamfanoni su tattauna bisa tushen ka’idojin kasuwanci, da cimma daidaito bisa dokokin kasar Sin da ka’idojin daidaiton samun moriya, ana fatan Amurka za ta samar da yanayin ciniki mai bude kofa da adalci da rashin nuna bambanci ga kamfanonin Sin da suka zuba jari a Amurka. Shugaba Trump ya bayyana cewa, Amurka tana fatan za a ingiza hadin gwiwar tattalin arziki da cinikayya a tsakanin kasashen biyu, kuma zai nuna goyon baya ga tawagogin kasashen biyu da su yi shawarwari don daidaita batun TikTok yadda ya kamata.

Akwai sharhin da aka yi game da cewa, tattaunawar dake tsakanin shugabannin kasashen biyu ta shaida cewa, Sin da Amurka sun samu muhimmin ci gaba kan cimma yarjejeniyar daidaita batun TikTok. Direktan ofishin nazarin siyasar kasa da kasa na kungiyar masana masu nazarin manufofin duniya na kwalejin ilmin zamantakewar al’ummar kasar Sin Zhao Hai ya yi fatan cewa, idan Sin da Amurka suka iya daidaita batun TikTok, to za a samar da sharadi ga kamfanonin kasashen biyu a kan yadda za su yi harkokin kasuwanci a kasuwar kasashen biyu, inda ta hakan za a sa kaimi ga Sin da Amurka wajen ganin sun daidaita sauran batutuwan tattalin arziki da cinikayya baki daya. (Zainab Zhang)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Xi Ya Bukaci Hada Karfi Da Karfe Wajen Gina Yankin Xinjiang Ya Zama Mafi Kyau
  • Xi Jinping Zai Halarci Bikin Murnar Cika Shekaru 70 Da Kafuwar Yankin Xinjiang Na Uygur Mai Cin Gashin Kansa
  • Kashi 80 Cikin Dari Na MDD Sun Amince Da Falasdinu A  Matsayin Kasa.
  • Tattalin arzikin Najeriya ya ƙara haɓaka — NBS
  • NEF za ta ƙaddamar da taron zuba jari don bunƙasa Arewa
  • Korea Ta Arewa Ta Sanar Da Kera Wani  Sabon Makami Na Sirri
  • Birtaniya Ta Amince Da Kafa Falasɗin A Matsayin Ƙasa
  • Birtaniya Zata Amince Da Falasɗin A Matsayin Ƙasa
  • Ya Kamata Sin Da Amurka Su Hau Turbar Hadin Gwiwa Da Samun Moriyar Juna A Sabon Lokaci
  • Shugaban Kasar Iran Ya Yi Kira Ga Samar Da Tattalin Arziki Da Shugabancin Kwararru