Gwamnati Ta Bayar Da Tabbaci Akwai Tsaro A Abuja Duk da Gargaɗin Da Ofishin Jakadancin Amurka Ya Yi
Published: 24th, June 2025 GMT
Ya ce: “Duk da cewa Gwamnatin Tarayya ta amince da haƙƙin ofisoshin jakadanci na ƙasashen waje, ciki har da na Amurka, na fitar da gargaɗin tafiye-tafiye ga ‘yan ƙasar su, yana da muhimmanci a faɗa a fili cewa Abuja tana da tsaro ga ‘yan ƙasa da mazauna da kuma baƙi baki ɗaya.”
Ya bayyana cewa hukumomin tsaro a Nijeriya suna aiki tuƙuru dare da rana don tabbatar da tsaron rayuka da dukiyoyin jama’a, ya ƙara da cewa tsarin tsaro a Abuja yana aiki yadda ya kamata tare da nasarori masu yawa wajen gano duk wata barazana da kuma daƙile ta kafin ta faru.
Ministan ya ƙara da cewa gargaɗin da Amurka ta fitar ba ya nuni da wata barazana kai-tsaye ga Abuja, illa ya dogara ne da al’amuran tsaro na duniya gaba ɗaya.
Ya ce: “Mun fahimci cewa gargaɗin da Amurka ta fitar ya ta’allaƙa ne da wasu abubuwan da ke faruwa a duniya gaba ɗaya, ba wai yana nuna wata barazana kai-tsaye ko ta gaggawa a cikin Babban Birnin Tarayya ba.
“Sai dai muna sake jaddadawa ga dukkan ofisoshin jakadanci, da masu zuba jari da abokan cigaba, da jama’a gaba ɗaya cewa babu wani dalilin fargaba.”
Ya kuma bayyana ƙudirin gwamnati wajen tabbatar da zaman lafiya da tsaro a birnin tarayya, yana mai cewa: “Gwamnatin Tarayya tana son sake jaddada ƙudirin ta na kare lafiyar duk mazauna ƙasar nan tare da ci gaba da tabbatar da martabar Abuja a matsayin ɗaya daga cikin manyan biranen da suka fi tsaro a duniya.”
Daga ƙarshe, ya buƙaci jama’a da su ci gaba da gudanar da harkokin su cikin kwanciyar hankali ba tare da tsoro ba, tare da yin taka-tsantsan da kuma bayar da rahoto kan duk wani abu da suka ga ya ɗaure masu kai ga jami’an tsaro mafi kusa.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
Haƙar Ma’adinai Ba Bisa Ƙa’ida Ba Barazana Ce Ga Tsaro A Yammacin Afirka – Tinubu
Ya kuma roƙi shugabannin ƙasashen Yammacin Afirka su haɗe kai wajen yaƙi da ƙungiyoyi masu amfani da ma’adinai ba bisa ƙa’ida ba, inda ya bayyana cewa irin waɗannan ayyuka suna ƙara haifar da tashin hankali da talauci.
Ministan Shari’a, Lateef Fagbemi, shi ma ya yi kira ga ƙasashen yankin su amince da yarjejeniyar ECOWAS kan cin hanci, domin hana masu rashawa samun wajen ɓuya.
“Mu tabbatar babu inda ɓarayi za su ɓuya. Duk wanda yake tayar da hankali a ƙasashenmu bai kamata ya samu natsuwa ba,” in ji Fagbemi.
Ƙungiyar NACIWA ƙungiya ce ta hukumomin yaƙi da cin hanci daga ƙasashen ECOWAS, wadda ke aiki tare wajen yaƙi da rashawa.
Shugaban ƙungiyar na yanzu shi ne Ola Olukoyede, wanda kuma shi ne Shugaban Hukumar EFCC ta Nijeriya.
ShareTweetSendShare MASU ALAKA