Gwamnati Ta Bayar Da Tabbaci Akwai Tsaro A Abuja Duk da Gargaɗin Da Ofishin Jakadancin Amurka Ya Yi
Published: 24th, June 2025 GMT
Ya ce: “Duk da cewa Gwamnatin Tarayya ta amince da haƙƙin ofisoshin jakadanci na ƙasashen waje, ciki har da na Amurka, na fitar da gargaɗin tafiye-tafiye ga ‘yan ƙasar su, yana da muhimmanci a faɗa a fili cewa Abuja tana da tsaro ga ‘yan ƙasa da mazauna da kuma baƙi baki ɗaya.”
Ya bayyana cewa hukumomin tsaro a Nijeriya suna aiki tuƙuru dare da rana don tabbatar da tsaron rayuka da dukiyoyin jama’a, ya ƙara da cewa tsarin tsaro a Abuja yana aiki yadda ya kamata tare da nasarori masu yawa wajen gano duk wata barazana da kuma daƙile ta kafin ta faru.
Ministan ya ƙara da cewa gargaɗin da Amurka ta fitar ba ya nuni da wata barazana kai-tsaye ga Abuja, illa ya dogara ne da al’amuran tsaro na duniya gaba ɗaya.
Ya ce: “Mun fahimci cewa gargaɗin da Amurka ta fitar ya ta’allaƙa ne da wasu abubuwan da ke faruwa a duniya gaba ɗaya, ba wai yana nuna wata barazana kai-tsaye ko ta gaggawa a cikin Babban Birnin Tarayya ba.
“Sai dai muna sake jaddadawa ga dukkan ofisoshin jakadanci, da masu zuba jari da abokan cigaba, da jama’a gaba ɗaya cewa babu wani dalilin fargaba.”
Ya kuma bayyana ƙudirin gwamnati wajen tabbatar da zaman lafiya da tsaro a birnin tarayya, yana mai cewa: “Gwamnatin Tarayya tana son sake jaddada ƙudirin ta na kare lafiyar duk mazauna ƙasar nan tare da ci gaba da tabbatar da martabar Abuja a matsayin ɗaya daga cikin manyan biranen da suka fi tsaro a duniya.”
Daga ƙarshe, ya buƙaci jama’a da su ci gaba da gudanar da harkokin su cikin kwanciyar hankali ba tare da tsoro ba, tare da yin taka-tsantsan da kuma bayar da rahoto kan duk wani abu da suka ga ya ɗaure masu kai ga jami’an tsaro mafi kusa.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
Tinubu ya gana da Janar Christopher Musa bayan Ministan Tsaro ya yi murabus
Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya yi wata ganawar sirri da tsohon Babban Hafsan Tsaron Najeriya, Janar Christopher Gwabin Musa a Fadar Shugaban Kasa.
Ganawar Tinubu da Janar CG Musa ya auku ne a ranar Litinin da dare, jim kadan kafin sanarwar murabus din Ministan Tsaro, Alhaji Muhammad Badaru Abubakar.
Majiyoyi na cewa gananawar shugaban kasa da Janar CG Musa na da nasaba da shirin shugaban kasar na cike gurbin da Badaru ya bari da kuma garambawul a shugabancin tsaron Najeriya.
Mai magana da yawun shugaban kasa Bayo Onanuga ya sanar cewa Badaru ya yi murabus ne saboda dalilai na rashin lafiya.
An kama ’yan bindiga 4 a Kano MAAUN: Ƙungiyar iyaye ta musanta zargin ƙara ƙudin yaye ɗalibai a jami’arBadaru ya ajiye aiki ne a daidai lokacin da Najeriya ke fama da karuwar matsalar tsaro musammana a shiyyar Arewa lamarin da ya sa Shugaba Tinubu ya ayyan dokar ta-baci kan sha’anin tsaro.
A cikin ’yan watannin nan ’yan ta’adda a hare-harensu, suka kashe wani Janar din soja, Kwamandan Birget na 25 da ke Jihar Borno, Birgediya-Janar Uba Musa da dakarunsa a Jihar Borno, inda kuma suka yi garkuwa da wasu mata a gona.
A kwanan nan ’yan ta’adda sun tsananta kai hare-hare a Jihar Kano, baya ga sace daruruwan dalibai a jihohin Kebbi da Neja da kuma yin garkuwa da masu ibada a Jihohin Kwara da Kogi da kuma sace wasu mata a Borno.