Aminiya:
2025-08-09@09:49:55 GMT

Iyalan Kanawa da aka kashe a Uromi sun zargin gwamnati da yin watsi da su

Published: 24th, June 2025 GMT

Iyalan mafarauta 16 ’yan Jihar Kano da aka yi wa kisan gilla a garin Uromi da ke Jihar Edo sun yi zargin cewa gwamnati ta yi watsi da su.

Wasu daga cikin waɗanda suka tsallake rijiya da baya a harin da kuma iyalan waɗanda aka kashe, sun bayyana cewa alƙawarin kuɗin magani da tallafi da kuma diyya fa gwamnatocin jihohin Edo da Kano suka yi musu bai wuce fatar baki ba.

Ayarin farautan sun baro garin Fatakwal na Nijar Ribas ne, a hanyarsu ta komawa gida domin bikin Ƙaramar Sallah, amma wasu ’yan banga a Uromi suka tare su, suka yi musu kisan gilla.

Akasarin mafarautan sun fito ne daga yankin Toronkawa da ke Ƙaramar Hukumar Bunkure ta Jihar Kano, tare  da abokansu daga ƙananan hukumomin Garko da Kibiya da Rano.

Iran da Isra’ila sun amince da tsagaita wuta —Trump NAJERIYA A YAU: Dabarun Samun Kuɗaɗe Ta Hanyar Amfani Da Wayar Hannu

’Yan kaɗan daga cikinsu ne suka sha da ƙyar a harin na Uromi na ranar 28 ga watan Maris, wanda ya sha tofin Allah-tsine daga ɓangarori daban-daban.

’Yan sanda sun bayyana cewa sun kama mutum 14 bisa zargin hannunsu a harin, a yayin da gwamnatocin jihohin Kano da kuma inda abin ya faru, suka yi alƙawarin ɗaukat matakan da suka dace na tallafi ga waɗanda abin ya shafa da iyalansu da kuma tabbatar da cewa an hukunta masu laifin.

A watan Afrilu Gwamnan Jihar Edo, Monday Okpebholo, ya sanar da kafa kwamitin bincike na haɗin gwiwa da Gwamnatin Tarayya kan lamarin.

Gwamna Okpebholo ya sanar da haka ne bayan mataimakin Gwamnan Kano, Aminu Abdulsalam Gwarzo, ya jagoranci jami’an gwamnatin Kano suka yi takakkiya zuwa Edo bayan kisan da aka yi wa Kanawan.

Daga bisani Okpebholo ya kai ziyarar ta’aziyya Kano, inda ya yi alƙawarin biyan diyya ga iyalan mamatan da kuma majinyatan da harin ya shafa.

A nasa jawabin Gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf, wanda ya jagoranci Okpebholo zuwa garin Toronkawa, ya jaddada cewa gwamnatin jihar za ta yi duk mai yiwuwa domin ganin an biya cikakken diyya ga iyalan. Ya kuma yi musu alƙawarin tallafi na kuɗaɗe da kayan abinci.

Gwamnatocin Kano da Edo sun yi gum

Aminiya ta tuntuɓi Kwamishinan Yaɗa Labarai na Jihar Kano, Ibrahim Garba Waiya, wanda kuma mamba ne a kwamitin binciken, kan dalilin rashin cika alƙawuran da gwamnatin jihar ta yi wa mutanen da abin ya shafa, amma ya ƙi cewa komai.

Haka shi ma Kwamishinan Jihar Edo, Paul Ohonbamu da Sakataren Yaɗa Labaran Gwamnan jihar, Free Itua, ba su amsa kiranmu ba ko rubutattun tambayoyin da aka tura musu.

Wakilinmu ya tuntuɓi shugaban al’ummar Hausawa a Jihar Edo, Alhaji Badamasi Saleh, amma ya bayyana cewa ba shi da masaniya game da ko gwamnatin jihar ta biya diyyar da ta yi wa mutanen alƙawari.

Ba a cika mana alƙawari ba

A garin Toronkawa kuma, iyalai da ragowar mafarautan da harin ya shafa sun ce ba a cika alƙawarin ba.

Ɗaya daga cikin mafarautan da ya tsallake rijiya da baya, Ibrahim Isah, ya tabbatar da hakan, inda ya ƙara da cewa, “Yanzu da ƙyar nake iya kula da iyalina. Yarana ’yan ƙanana ne ballantana su tallafa min.

“An yi mana alƙawarin za a kula da mu a asibiti, amma daga aljihuna na kashe kuɗin jinya N40,000, duk da haka ban samu kulawar da ta dace ba.”

Ya ce duk da alƙawarin tallafin abinci da sauransu da Gwamnatin Kano ta yi musu, amma ba su gani a ƙasa. “Sun ce sun kawo mana kuɗi da abinci, amma dai ba mu komai ba.

“Mun je sakatariyar ƙaramar hukuma, aka ce ciyaman ya tafi Saudiyya, amma mataimakinsa ya ce suna aiki a kan lamarin,” a cewar Malaman Ibrahim ɗan shekara 45.

Malama Zahura Haruna, matan ɗaya daga cikin mafarautan da aka kashe, ta ce, “Rayuwa ta yi mana ƙunci, yanzu na zama nauyi ga surukaina, da ma shi ne mai ƙarfin gidan. Yanzu da maƙwabta muka dogara don samun abinci.”

A Ƙaramar Hukumar Kibiya kuma, Malam Bala Dutse, wanda aka kashe ɗansa Ahmadu a harin Ironsi, ya bayyana wa wakilinmu cewa ba su ji komai daga ɓangaren gwamnati ba, amma, “aƙalla ya kamata su fito su yi mana bayanin abin da suka tsara yi game da biyan diyyan.”

Wata mai takaba daga cikin matan mafarautan da aka kashe, Hauwa’u Isah, ta ce, “sun yi mana alƙawarin adalci, amma kullum sai ka ga abin kamar kalaman siyasa ne kawai.”

Amma Mataimakin Shugaban Ƙaramar Hukumar Kibiya, Nasiru Adam Abdulaziz, ya jaddada aniyar ƙaramar hukumar ta mama wa waɗanda abin ya shafa adalci.

Ya ce, “Waɗannan iyalan sun cancanta a yi musu bayani kuma ina da ƙwarin gwiwa cewa gwamnati za ta yi abin da ya dace.”

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: mafarauta Matafiya mafarautan da

এছাড়াও পড়ুন:

Ana zargin ‘yan sanda da karya hannun Sowore

Ana zargin wasu ‘yan sanda daga Sashen Binciken ‘yan sanda na Kasa sun kutsa inda ake tsare dan gwagwarmaya Omoyele Sowore a Abuja, inda suka fita da shi da karfin tuwo zuwa wani wuri da har yanzu ba a sani ba.   Haka kuma kamar yadda Sowore ya sanar a shafinsa na sada zumunta na Facebook, ya yi zargin cewa an karya hannunsa yayin da jam’an suka finciko shi da karfin tsiya daga inda yake tsare wajen qarfe 6:00 na safiyar yau Alhamis a kokarinsu na kai shi kotu ba tare da sanar da lauyansa ba..   A jiya Laraba ne dai Sowore ya amsa gayyatar da ofishin Babban Sufeton ‘Yan sanda na kasa ya yi masa don ya amsa wasu tambayoyi da suke da alaka da zanga-zangar da tsofaffin ‘yan sanda suka yi a makon jiya   Ana kuma son karin bayani kan zargin da Sowore ya yi na cewa, Babban Sufeton na Kasa ya kara wa jami’an ‘yan sandar da ke aiki a gidansa girma ba bisa ka’ida ba.   Sai dai ya yi watsi da zarge-zargen inda ya bayyana su a matsayin borin kunya da hukumar ‘yan sandan take don “dauke hankalin jama’a daga abin kunyar da Babban Sufeton na kasa Kayode Egbetokun da kuma hukumar ‘yan sandan ke aikatawa.   Tuni dai Kungiyar kare Hakkin Bil’Adama ta Amnesty International ta fitar da sanarwar yin Allah wadai da kamun da hukumar ‘yan sandan ta Najeriya ta yi wa Sowore wanda ta ce ya sba wa ‘yancinsa na fadin albakacin baki.   Haka kuma Amnesty International ta bukaci a saki Omoleye Sowore nan take ba tare da gindaya masa wasu sharuda ba.   Shi ma dan gwagwarmaya Bello Galadanci da aka fi sani da Dan Bello, ya yi tir da kamun da aka yi wa Sawore tare da kiran a sake shin an take kamar yadda ya rubuta a shafinsa na Facebook.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • ADA/ADC, APC Da PDP: Jam ’iyyun Siyasa Da Ke Shan Jinin ’Yan Nijeriya
  • ’Yan damfara 2 sun shiga hannun ’yan sanda a Yobe
  • Nijeriya Na Asarar Tiriliyan 3.2 Sanadiyyar Watsi Da Noma A Gandun Daji
  • Abba ya yi alhinin hadiminsa da ’yan daba suka kashe a Kano
  • ’Yan sanda sun ƙwato jariri da aka sace a asibitin Ekiti
  • Ana zargin ‘yan sanda da karya hannun Sowore
  • Matasan Kauru Sun zargin Dan Majalisar Dokoki Barnabas Danmaigona da Rashin tabuka komai
  • Ma’aikatan gwamnati na amfani da kudaden sata wajen gina rukunin gidaje – EFCC
  • Gwamna ya yi wa iyalan ’yan wasan Kano da suka rasu a hatsari goma ta arziki
  • Gwamnan Kano ya gargaɗi muƙarrabansa bayan murabus ɗin Kwamishina